Sashe 15
Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*****
Kamar yadda Abba ya fada basu kwana a karofi ba Inno dai da Baba Ati suna nan zasu kwana Biyu,Sai Dare suka isa gida,Ranar Abba barci ma rabi da rabi yayi washegari da yaje Office idanuwansa yayi ja matuka alamun baya cikin natsuwarsa,Kansa sai ya fara ciwo shiyasa ya Dawo gida ya kwanta Ammi tasan Baban Nana bai iya Fushi ba ballatana abunda ya shafi yaransa,Dakyar ta Lallashesa yaci abinci ya sha mgani ya kwanta sai bayan La'asar ya tashi ya yi wanka ya Sauya kaya Ammi sun yi waya da su Nana Fatima ammh bata fada musu yadda zaman ya kaya ba.
Nana Fatima sai taji Hankalinta ya kwanta da Ammi tace Fa'i na Karofi har alokacin.
Abba ko Dariya ya Daina yi yana Sakawa da warwaran yadda zai karb'an ma Fa'iza Takardan Sakinta ko Hiran Daran da sukan taba da Hafsah da Nana khadija ranar bai samu ba,Daman kuma Ammi tace bai jin Dadi daga gaisuwa da Tambayan ya jiki ya koma ya kwanta ya Lumshe ido shiyasa suka fice suka koma Shashen Ammi suna Tunanin kila ciwon kan ne ya matsa ma Abba.
Yayi nisa cikin tunanin sa har baisan sanda Maman Nana ta shigo ba itama gajiya tayi da kiran sunansa ta matso kusa da shi tana Taba kafarsa Lokaci daya da kiran sunansa"Baban Nana"
Firgigit yayi kamar wanda ya farka Daga barci sai yaci karo da sanyin Idaniyarsa,Azizat.
Ajiyar rai ya sauke cikin wani yanayi ya kasa mgana Maman Nana ta zauna gefensa,Sai ya matsa ya bata wajen zama ya mike dakyau ya gyara zama kafadunsu na dukan juna.
Cikin wani yanayi Ammi ta kallesa tana Fadin"Haba Baban Nana meyasa..?wannan tunanin da kake yi fa ba mafita ba ne"
Numfashi ya sauke kafin yace"Alkwarin da nayi ma Fa'iza ke damuna Maman Nana na rasa ta hanyar da zan karban mata takardan Sakinta Ishaq bazai yi sakin nan cikin Sauki ba"
Ko na kai shi kara kotu ne..?
Da Sauri ta girgiza kai kafin tace"A'a duk bata kai haka ba Baban Nana. akwai ya'ya tsakani sannan ga zumunci a bi dai komai a sannu. Kowa ya shaida zalunci da Kuntatawa a zaman auren Fa'iza da shi mganar ma yaki sakinta bai taso ba".
Abba yayi shuru ya kasa mgana Ammi ta cigaba da bashi mgana cikin kwantar da Hankali har ya samu natsuwa cikin Sauke ajiyar rai yace"Bakomai nasan ta inda zan Bullo masa"
Ammi tace"kabi a sannu Baban Nana nasan ka sarai"
Mirmishi yayi mata kafin yace"In sha Allahu"
Daganan shi da kanshi ya Rufe mganar bayan ya bude mganar kayan Funitures din da yake so a saka a sabon gininsa na karofi Ammi tace"Ga inda muke siyan kaya kano.
Har gida zasu kai komai su kuma gyara wajen"
Kai tsaye yace"Ki yi lissafin kudin zan Tura miki ta asusun ki"
Da kai ta gyada masa kafin su cigaba da Hiran su sama sama na mata da Miji masu kaunar juna da Fahimtar juna.
A cikin Hiran ne Ammi ta kallesa tana Fadin"Wai ina labarin Engr ne Baban Nana..?kwana Biyu ban ji kuna waya ba hala bai shigo kaduna ba ne..?
Abba yayi hamma kafin yace"Gaskiya satin nan kaf bamu yi waya. Mgana ta dashi ta karshe yace zai je London ina kyautata zaton ya tafi ayyuka ne suka masa yawa kinsan Engr da Sabgogi da yawa fa"
Ammi tace"Sosai fa,ya jikin Hajiya Kudirat kwanaki na kira Hajiya Shukran bata Dauka ba,Azima ta fadamin kwanaki ta shigo ta gaida Hajiya Jikin Hajiya tafisu ne ya matsa tazo Dubata"
Abba yace"Haba tuni ta warware kamar ma Engr yace min ta saka rigima sai ta koma Benue ,Lokacin muna Warri tare da shi naji an kirasa ana fadin ya Lallasheta yace rigimmiyar Tsohuwa a barta tatafi mana"
Ammi tayi Dariya kafin tace"Kai a wannan matar akwai rigima wlh,ka tuna da mukaje dubata sai Yarbanci take tana masifa saboda za'a bata mgani sai da D'anta yazo ya lallasheta ta yarda fa"
Abba na mirmishi yace"Engr na yawan Fadin rigimarta tana matukar son mahaifinsa da su kansu tunda shi kadai take da shi ance Haihuwanta Goma tara duk sun yi wabi ne shi kadai ya tsaya"
Ammi tace"Allah sarki.."
Nan ya cigaba da bata wasu labaran itama tana bashi wanda ta sani Dalilin Hajiya Tafisu,Suna ta yabon kirkin Engr da iyayensa.
Abba yace"Muna da Seminar a Abuja sai dai ban sani ba ko zai samu zuwa"
Ammi tace"To kila in yana gari"
Abba yace"Ba lalle ba gaskiya"
Da haka suka rufe wannan Hiran suka Fara shirin kwanciyaa
*******
Tunda ga ranar da Abba ya bar Karofi, Rana bazata tab'a fitowa ta fad'i Abba bai kirani mun gaisa yaji Lafiyata ba.
sannan ya turamin 100k na bunkasa kasuwancina mganar makaranta kuma Mallam yace a jira sakin ya tabbata nayi iddata in nagama ina da Damar fita duk inda naga Dama,Da haka sai na Dakata ammh na samu natsuwa da kwanciyar Hankali,sannan na fara maida jikina,Goggo na da almajirai masu Dibo ruwa da sharan Tsakar gida gyaran Daki kawai nake yi sai Girki,Yarana kuma muna mgana da su ta wayar Zainab ammh ba ko da yaushe ba,Goggo da kanta ta shiga kasuwa ta min siyayyan kayan zobo da Kunin Aya,aka sauke a dayan Dakin inda na saka Freezer dina sana'ata zata dawo gadan gadan tunda zaman bazai min Dadi ba.
Goggo ta aikamin makota yaya mariya ma haka tunda nan kusa da su suna siya Lokacin da ta kan sara a wajena shiyasa da na fara Zobo ba laifi ana samun ciniki matsala D'aya na samu Rashin wuta in nayi kunin aya sai ya fara Lalacewa kafin ya kare Tunda ba ciniki ba kamar Lokacin ina katsina ba.
Da na fad'ama Abba ana matsalan wuta batare da sanina ba Sai ga Yaya Isa da katon Generator in ji Abba sai dai na kira nayi Godiya Baba Ati na nan bata koma ba,Inno dai Abba ya Turo Direba ya Dauketa zataje ganin Likitan ido.
Gida kuma Tuni ma'aikata sun zo sun kawata gidan da kayan Furnitures masu kyau muma mun je mun gani mun kara gyara gidan nan Su Abba zasu rika sauka Tunda Baba Ati tace bazata iya zama ita kadai ba.
Muna waya da Anty Fadila kuma tana zuwa duk weekend tana Duba su Amir suma Baban nasu na kawo su Tunda yaga sun shaku da yaranta.
Mama bata koma Lagos ba tana katsina wajen Anty Binta sai dai Badariya da Jamal suna chan Zainab ga Tsohon ciki ammh haka ta fara zuwa aikin da Mahaifinta ya samar mata sannan kuma ya siya mata Motar da zata rika zirga zirga aciki ta Riga ta sadakar maman Amir bazata Dawo ba.
Shi kan shi Uban gayyar tun bayan Tafiyarsa sai kirana yake yi ban taba Dauka ba,in dai naga shine ammh ina Daukan kiran Zainab Saboda nasan ko ita ko yara ko kuma Badariya,Har Jamal ma yana kirana duk korafin su Daya na dawo sai dai na bisu da toh ammh su kan su sun tabbatar da bazan Dawo ba.
Dad'ina Daya da su Amir suka fadamin sai la'asar suke tashi daga makarantar Boko,gidan Anty Fadila suke zama saboda yaranta suna da Malamin islamiya in suka yi karatun Tare babansu in ya tashi aiki sai ya Biya ya Dauke su,Zaman su sai asabar da Lahadi shima gidan Anty Fadila suke yin shi Zainab fama take da kanta Ko nata ya'yan su Amir ke kula da su sai mai renon da ta zo da'ita.
Ashe bani kadai Ishaq ke kira ba Harda Abba shima bai kara Saurarensa ba domin yace in yana son mgana da shi ya rubutamin Takardan Sakina,Tun bayan Lokacin Abba bai zo Karofi ba sai dai Hafsah da Nana Khadija sun zo sun yi Sati Daya suka koma Hafsah ta zama katuwa tayi jajir da ita ta samu Waddatccen hutu da jin Dadi.
Ba Laifi sana'ata ta Dawo kuma Tunda aka ganeni ana ciniki sannan Goggo tasan almajiranta na Dauka su tafin da shi wata makarantar maza ta secondary sai kudina suma da suka gane har gida suke zuwa siya in ba Wuta sai na Tada in ji na,Ganin aikin namin yawa yasa Goggo ta ce na Dauki wacce zata rika taimakamin nan makotan su Goggo na samu wata Jummala Mijinta ya rasu tana da marayin ya'ya ita mukayi ciniki da ita zan rika bata 5k duk wata ta amince da Murnan ita ke Dafamin zobo ta kuma wanke aya ta kai nika nawa kawai Dubawa da zaman Had'awa sai aikin ya Ragemin Kuma Alhamudulillah sai Hankalina ya Dauke Damuwa ta rage samun Muhalli a zuciyata,Saboda ayyukan dake gabana.
Yaya Asiya duk abunda ya Faru Labari taji mun yi mgana ta waya abu daya tace min"Fa'iza ki zauna ki yi Tunanin makomar rayuwarki in rabuwa da Ishaq mafita ce gareki zamu baki Goyon baya,in kuma komawarki itace Mafita Fa'iza ki koma Dakin ki ki Rumgumi ya'yan ki''
Da toh kawai na amsa mata Saboda bani da abun ce mata komai zan Fad'a bazata gane ba Makotana ma muna waya da su barin ma Sa'adatu sai dai ban taba Fada musu ina Karofi ba na barsu a ina Lagos ne Haka ma Hajiya sai dai ita nasan Kila Raliya zata Fadamata ammh har Lokacin batamin mgana ba,Sai nima na share ban mata ba,na maida jikina duk da ramar kasusuwan wuyana basu shige ba,Sai dai sun fara shigewa din
Koda yaushe Nasiha ne tsakanina da yan'uwa suna Lallab'ani Saboda na samu kwanciyar Hankali kuma na samu matuka.
Anty Binta ta kirani sau biyu tana min Daidaiciyar mgana na bita da Toh,ta kuma saka har Anty Mahma da Halisa suka kirani duka mganan su kan ya'ya ne na koma Saboda su,ni ko bana cewa komai sai dai toh, sai yanzu suka san da yaran..? Bazan kara bari Saboda ya'yana a cutar dani ba.
Suna ta so na koma ne na cigaba da Bautar da na saba ina bakin Alkalami ya Riga ya bushe ba Ishaq ba gabad'aya maza ne da aure ya fita kaina kwata kwata.
*******
Kamar yadda Abba ya fada basu kwana a karofi ba Inno dai da Baba Ati suna nan zasu kwana Biyu,Sai Dare suka isa gida,Ranar Abba barci ma rabi da rabi yayi washegari da yaje Office idanuwansa yayi ja matuka alamun baya cikin natsuwarsa,Kansa sai ya fara ciwo shiyasa ya Dawo gida ya kwanta Ammi tasan Baban Nana bai iya Fushi ba ballatana abunda ya shafi yaransa,Dakyar ta Lallashesa yaci abinci ya sha mgani ya kwanta sai bayan La'asar ya tashi ya yi wanka ya Sauya kaya Ammi sun yi waya da su Nana Fatima ammh bata fada musu yadda zaman ya kaya ba.
Nana Fatima sai taji Hankalinta ya kwanta da Ammi tace Fa'i na Karofi har alokacin.
Abba ko Dariya ya Daina yi yana Sakawa da warwaran yadda zai karb'an ma Fa'iza Takardan Sakinta ko Hiran Daran da sukan taba da Hafsah da Nana khadija ranar bai samu ba,Daman kuma Ammi tace bai jin Dadi daga gaisuwa da Tambayan ya jiki ya koma ya kwanta ya Lumshe ido shiyasa suka fice suka koma Shashen Ammi suna Tunanin kila ciwon kan ne ya matsa ma Abba.
Yayi nisa cikin tunanin sa har baisan sanda Maman Nana ta shigo ba itama gajiya tayi da kiran sunansa ta matso kusa da shi tana Taba kafarsa Lokaci daya da kiran sunansa"Baban Nana"
Firgigit yayi kamar wanda ya farka Daga barci sai yaci karo da sanyin Idaniyarsa,Azizat.
Ajiyar rai ya sauke cikin wani yanayi ya kasa mgana Maman Nana ta zauna gefensa,Sai ya matsa ya bata wajen zama ya mike dakyau ya gyara zama kafadunsu na dukan juna.
Cikin wani yanayi Ammi ta kallesa tana Fadin"Haba Baban Nana meyasa..?wannan tunanin da kake yi fa ba mafita ba ne"
Numfashi ya sauke kafin yace"Alkwarin da nayi ma Fa'iza ke damuna Maman Nana na rasa ta hanyar da zan karban mata takardan Sakinta Ishaq bazai yi sakin nan cikin Sauki ba"
Ko na kai shi kara kotu ne..?
Da Sauri ta girgiza kai kafin tace"A'a duk bata kai haka ba Baban Nana. akwai ya'ya tsakani sannan ga zumunci a bi dai komai a sannu. Kowa ya shaida zalunci da Kuntatawa a zaman auren Fa'iza da shi mganar ma yaki sakinta bai taso ba".
Abba yayi shuru ya kasa mgana Ammi ta cigaba da bashi mgana cikin kwantar da Hankali har ya samu natsuwa cikin Sauke ajiyar rai yace"Bakomai nasan ta inda zan Bullo masa"
Ammi tace"kabi a sannu Baban Nana nasan ka sarai"
Mirmishi yayi mata kafin yace"In sha Allahu"
Daganan shi da kanshi ya Rufe mganar bayan ya bude mganar kayan Funitures din da yake so a saka a sabon gininsa na karofi Ammi tace"Ga inda muke siyan kaya kano.
Har gida zasu kai komai su kuma gyara wajen"
Kai tsaye yace"Ki yi lissafin kudin zan Tura miki ta asusun ki"
Da kai ta gyada masa kafin su cigaba da Hiran su sama sama na mata da Miji masu kaunar juna da Fahimtar juna.
A cikin Hiran ne Ammi ta kallesa tana Fadin"Wai ina labarin Engr ne Baban Nana..?kwana Biyu ban ji kuna waya ba hala bai shigo kaduna ba ne..?
Abba yayi hamma kafin yace"Gaskiya satin nan kaf bamu yi waya. Mgana ta dashi ta karshe yace zai je London ina kyautata zaton ya tafi ayyuka ne suka masa yawa kinsan Engr da Sabgogi da yawa fa"
Ammi tace"Sosai fa,ya jikin Hajiya Kudirat kwanaki na kira Hajiya Shukran bata Dauka ba,Azima ta fadamin kwanaki ta shigo ta gaida Hajiya Jikin Hajiya tafisu ne ya matsa tazo Dubata"
Abba yace"Haba tuni ta warware kamar ma Engr yace min ta saka rigima sai ta koma Benue ,Lokacin muna Warri tare da shi naji an kirasa ana fadin ya Lallasheta yace rigimmiyar Tsohuwa a barta tatafi mana"
Ammi tayi Dariya kafin tace"Kai a wannan matar akwai rigima wlh,ka tuna da mukaje dubata sai Yarbanci take tana masifa saboda za'a bata mgani sai da D'anta yazo ya lallasheta ta yarda fa"
Abba na mirmishi yace"Engr na yawan Fadin rigimarta tana matukar son mahaifinsa da su kansu tunda shi kadai take da shi ance Haihuwanta Goma tara duk sun yi wabi ne shi kadai ya tsaya"
Ammi tace"Allah sarki.."
Nan ya cigaba da bata wasu labaran itama tana bashi wanda ta sani Dalilin Hajiya Tafisu,Suna ta yabon kirkin Engr da iyayensa.
Abba yace"Muna da Seminar a Abuja sai dai ban sani ba ko zai samu zuwa"
Ammi tace"To kila in yana gari"
Abba yace"Ba lalle ba gaskiya"
Da haka suka rufe wannan Hiran suka Fara shirin kwanciyaa
*******
Tunda ga ranar da Abba ya bar Karofi, Rana bazata tab'a fitowa ta fad'i Abba bai kirani mun gaisa yaji Lafiyata ba.
sannan ya turamin 100k na bunkasa kasuwancina mganar makaranta kuma Mallam yace a jira sakin ya tabbata nayi iddata in nagama ina da Damar fita duk inda naga Dama,Da haka sai na Dakata ammh na samu natsuwa da kwanciyar Hankali,sannan na fara maida jikina,Goggo na da almajirai masu Dibo ruwa da sharan Tsakar gida gyaran Daki kawai nake yi sai Girki,Yarana kuma muna mgana da su ta wayar Zainab ammh ba ko da yaushe ba,Goggo da kanta ta shiga kasuwa ta min siyayyan kayan zobo da Kunin Aya,aka sauke a dayan Dakin inda na saka Freezer dina sana'ata zata dawo gadan gadan tunda zaman bazai min Dadi ba.
Goggo ta aikamin makota yaya mariya ma haka tunda nan kusa da su suna siya Lokacin da ta kan sara a wajena shiyasa da na fara Zobo ba laifi ana samun ciniki matsala D'aya na samu Rashin wuta in nayi kunin aya sai ya fara Lalacewa kafin ya kare Tunda ba ciniki ba kamar Lokacin ina katsina ba.
Da na fad'ama Abba ana matsalan wuta batare da sanina ba Sai ga Yaya Isa da katon Generator in ji Abba sai dai na kira nayi Godiya Baba Ati na nan bata koma ba,Inno dai Abba ya Turo Direba ya Dauketa zataje ganin Likitan ido.
Gida kuma Tuni ma'aikata sun zo sun kawata gidan da kayan Furnitures masu kyau muma mun je mun gani mun kara gyara gidan nan Su Abba zasu rika sauka Tunda Baba Ati tace bazata iya zama ita kadai ba.
Muna waya da Anty Fadila kuma tana zuwa duk weekend tana Duba su Amir suma Baban nasu na kawo su Tunda yaga sun shaku da yaranta.
Mama bata koma Lagos ba tana katsina wajen Anty Binta sai dai Badariya da Jamal suna chan Zainab ga Tsohon ciki ammh haka ta fara zuwa aikin da Mahaifinta ya samar mata sannan kuma ya siya mata Motar da zata rika zirga zirga aciki ta Riga ta sadakar maman Amir bazata Dawo ba.
Shi kan shi Uban gayyar tun bayan Tafiyarsa sai kirana yake yi ban taba Dauka ba,in dai naga shine ammh ina Daukan kiran Zainab Saboda nasan ko ita ko yara ko kuma Badariya,Har Jamal ma yana kirana duk korafin su Daya na dawo sai dai na bisu da toh ammh su kan su sun tabbatar da bazan Dawo ba.
Dad'ina Daya da su Amir suka fadamin sai la'asar suke tashi daga makarantar Boko,gidan Anty Fadila suke zama saboda yaranta suna da Malamin islamiya in suka yi karatun Tare babansu in ya tashi aiki sai ya Biya ya Dauke su,Zaman su sai asabar da Lahadi shima gidan Anty Fadila suke yin shi Zainab fama take da kanta Ko nata ya'yan su Amir ke kula da su sai mai renon da ta zo da'ita.
Ashe bani kadai Ishaq ke kira ba Harda Abba shima bai kara Saurarensa ba domin yace in yana son mgana da shi ya rubutamin Takardan Sakina,Tun bayan Lokacin Abba bai zo Karofi ba sai dai Hafsah da Nana Khadija sun zo sun yi Sati Daya suka koma Hafsah ta zama katuwa tayi jajir da ita ta samu Waddatccen hutu da jin Dadi.
Ba Laifi sana'ata ta Dawo kuma Tunda aka ganeni ana ciniki sannan Goggo tasan almajiranta na Dauka su tafin da shi wata makarantar maza ta secondary sai kudina suma da suka gane har gida suke zuwa siya in ba Wuta sai na Tada in ji na,Ganin aikin namin yawa yasa Goggo ta ce na Dauki wacce zata rika taimakamin nan makotan su Goggo na samu wata Jummala Mijinta ya rasu tana da marayin ya'ya ita mukayi ciniki da ita zan rika bata 5k duk wata ta amince da Murnan ita ke Dafamin zobo ta kuma wanke aya ta kai nika nawa kawai Dubawa da zaman Had'awa sai aikin ya Ragemin Kuma Alhamudulillah sai Hankalina ya Dauke Damuwa ta rage samun Muhalli a zuciyata,Saboda ayyukan dake gabana.
Yaya Asiya duk abunda ya Faru Labari taji mun yi mgana ta waya abu daya tace min"Fa'iza ki zauna ki yi Tunanin makomar rayuwarki in rabuwa da Ishaq mafita ce gareki zamu baki Goyon baya,in kuma komawarki itace Mafita Fa'iza ki koma Dakin ki ki Rumgumi ya'yan ki''
Da toh kawai na amsa mata Saboda bani da abun ce mata komai zan Fad'a bazata gane ba Makotana ma muna waya da su barin ma Sa'adatu sai dai ban taba Fada musu ina Karofi ba na barsu a ina Lagos ne Haka ma Hajiya sai dai ita nasan Kila Raliya zata Fadamata ammh har Lokacin batamin mgana ba,Sai nima na share ban mata ba,na maida jikina duk da ramar kasusuwan wuyana basu shige ba,Sai dai sun fara shigewa din
Koda yaushe Nasiha ne tsakanina da yan'uwa suna Lallab'ani Saboda na samu kwanciyar Hankali kuma na samu matuka.
Anty Binta ta kirani sau biyu tana min Daidaiciyar mgana na bita da Toh,ta kuma saka har Anty Mahma da Halisa suka kirani duka mganan su kan ya'ya ne na koma Saboda su,ni ko bana cewa komai sai dai toh, sai yanzu suka san da yaran..? Bazan kara bari Saboda ya'yana a cutar dani ba.
Suna ta so na koma ne na cigaba da Bautar da na saba ina bakin Alkalami ya Riga ya bushe ba Ishaq ba gabad'aya maza ne da aure ya fita kaina kwata kwata.
*******