Sashe 26
Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A satin suka fara workshop din,
A nan babban ma'aikantansu na NNPC da ke kaduna. in Abba ya fita tun safe sai dare Direba ke dawo da shi gida a gajiye. wanka kawai yake yi yaci abinci ya kwanta,kwana uku da Farawarsu ranar da daddare bayan ya dawo yana cin abincin da na Dafa na shigo ni kuma mu gaisa.
Ina zaune gefensa na Hagu Ammi na barayin Dama ganin ya share Mulmulen tuwon shinkafa guda uku da Ammi ta sakamai ammh kuma yana mganar ta karamai,jin haka yasa muka kallesa a tare ni da ita cikin mamaki tace"Na hudu fa kenan Baban Nana.."
Cikin ka'da kai yace"yunwa nake ji ne Maman Nana. rabo na da abinci tun karin da nayi na Safe fa."
Cikin mamaki tace"Tun Safe fa Baban Nana?baka ce min akwai restaurant guda da aka dauko suna baku abinci a wajen ba..?
Kai tsaye Abba ya kalleni kafin yace"D'iyata k'aramin tuwon nan kin ji,in na biye ta tambayoyin wannan uwar taku yunwar sai ta kara jigatani"
Ina Dariya kafin nayi mgana,Ammi ta zubamai ta karamai hade da miyar Ogun din da nayi wacce taji Bushasshen kifi da Kashin Rago.
Sai da ya fara ci sannan ya Dago yana Fadin"Wato maman Nana Allah ya yi ma Diyar nan taki albarka ta shagwabani da girke girkenta duk inda naje naci abinci in ba Dandanon Abincin ki ko nata ba,wlh baya kosar dani sam ga masu abincin sai ma abunda ka zaba ni dai wlh kada'n nake ci sai naji duk ba Dadi na gwammace in na dawo sai naci gabad'aya"
Ammi tace"Gaskiya to bari ka Hakuri kana ci zama da yunwa ina yaga amfani in wani cutar ta kama ka fa..?
Abun wanke hannu yace ta tara masa sai da ya wanke hannu da bakinsa sannan ya koma ya kishingida yana Hamdala ni na kwashe kayan zuwa Kitchen ban koma Falon Abba ba,sai na wuce dakin da na sauka nayi shirin kwanciya ban san kuma ya Abba suka karkare mganar ba da Ammi sai washegari Ammi ke kara min mganar cikin wasa tace"Jiya kin ji Baban ku da rigima. Kamar wani yaro yana zama da yunwa sai kaci abunda ke hannunka in ya dawo sai yaci na gida ba shikenan ba"
Nima cikin Dariyan nace"Ba matsala fa Ammi za'a iya yi masa abincin sai Direba ya rika zuwa yana karban masa'"
Ammi ta kalleni kafin tace"Ko..?duk wahala ce Fa'i bar rigiman Baban ku kin ji"
Ni kuma na Dage sai a rika yin haka Ammi ta tabe baki tana fadin"Ke mai Uba ko..?Allah ya ba da sa"a
Abba na dawowa ta fad'amai sai ya Daga waya ya kirani Lokacin ina waya da Badariya sai da muka gama naga kiransa sai na saka Hijabi zuwa Falonsa,a chan na iske Hafsah da Nana khadija suna ganina suka fara Rige rigen tashi Ammi ta kallesu tana Fadin"Daga gani baku da gaskiya ko..?
Ina Dariya nace"Ammi Wainar Fulawa na soya nafa saka musu nasu. daga shigata wanka suka zagayo suka Kwashe wanda na bari zan ci"
Ammi tace"mugaye shiyasa zasu gudu"
Dariya suka saka Nana Khadija tace"Bani bace fa Hafsi ce"
Hafsatu tayi saurin cewa"Wlh bani ba ce ni da bana cin wainar fulawa ma"
Hararanta nayi kafin nayi mgana ta kama kanta Abba waya yake yi shiyasa bai sakamana baki ba sai da ya gama su kuma Lokacin sun fice suna Dariya su san abunda suka aikata.
Zama nayi gefen Abba muka gaisa ya amsa cikin Sakewa kafin yace"Mamarku ta fad'amin kin ce bazaki bar babanki da yunwa ba ko.?
Ina mirmishi na Daga kaina kafin nace"To Abba kana damu meyasa zaka zauna da yunwa?
Abunda kake so shi za'ayi maka."
Jinjina kai ya yi Lokaci daya yana fadin"Nagode sosai Allah ya yi miki albarka yasa ya'yanki su rama miki.
Ammi ta amsa da Ameen kafin tace"Ba ka ce Allah ya bata miji nagari ba..?
Ina jin Haka na mike ina fadin"Abba mu kwana lafiya"
Ammi ta bini da Dariya tana Fadin"Diyar taka Baban Nana sai kayi da gaske ko wani gwaskan muka samu sai ta bamu kunya na lura da take takenta"
Abba ya murmusa kafin yace"kyaleta ba mai yi mata Dole. in ma bazata kara yin auren ba ina bayanta"
Ammi ta karkace baki kafin tace"Haba da kuruciyarta Baban Nana..?Allah zai kawo mata wani wanda zai kaunace ta saboda Allah ya rud'ata ta zo da kanta tana fadin Abba na amince masa"
Ta karishe fad'a tana Dariya Abba ya jinjina kai yana Fadin"Allah yasa ni dai a nawa shawaran ta daidaita da Baban yaran nan ishaq ya yi nadama sosai wlh in da zata koma da ni kaina naso hakan'"
Yana mgana Ammi na tabe baki sai da ya gama sannan tace"Nafi yi ma Fa'iza sha'awar sabuwar rayuwa akan ta koma Rayuwarta ta baya kwata kwata ishaq bai chanchanci a basa wani Dama ba, gwara haka dai kowa da nashi Kaddaran"
Kai kawai Abba ya kada kafin yace"Tunda baki son sa ai komai zaki ce, ammh duk in da zata je bai kai inda ta fara gina Zuru'arta ba azizat. da sabon yabe duk lalacewar tsoho wlh gwara tsohon yaben nan ni a ganina"
Ammi ta kada kai kafin tace"Wlh wani Sabon Yaben yafi tsohon sau Duhu"
Kyaleta yayi sanin Halinta ita ko taki Hakura tacigaba da fadin"kuma in kana mganar ya'ya ne ai sun saba da Rashinta,suna zaune gidan uban su in da ya dace da su ita kuma Allah ya bata wani mijin taje tayi auranta ta Huta taji dadinta"
Abba ya gyara zama yana fadin"Allah ya bata Azizat"
Dariya tayi kafin tace"Ameen Baban Nanas d'ina"
Girgiza kai yayi yana mirmishi kafin yace"'Allah ya shirya Maman Abdul'ahad'
Da Ameen ta amsa mai tana Dariya mganar Fa'iza suka rufe su ka kama na Raliya da mganar sai Walid ya yi kwari za'a shiryamata tafiya wajen mijinta.
******
Kamar yadda nayi alkwari ban sauya ba tunda ina nan ba ranar Tafiya. Goggo ma bata damu ba tasan daman Ammi nata korafin rashin zuwana,aranta daman tasan sai an ganni kawai,daman ni nake yin girkin Rana sai nake dib'arma Abba Ammi ta kirasa ya turo Direba ya Daukan masa ya kai masa watarana ma in ya makara sai dai a basket yake tafiya da abun karin nasa ya yi achan ba'a Rufe Sati ba Ranar Abba ya dawo yace yunwa yake ji sosai.
Ammi ta kallesa yana ragema Tie din wuyansa tsukewa tace"a'ah ina abincin da direba yakai maka..?
Kai ya girgiza kafin yace"Wani abinci..?ai ina gaya miki tun rana na biyu da Ashuru ya fara karbo'min abincin su Engr Bashir suka sakamin ido. wlh tun suna su biyu har sukamin gayya suna min tsiyan ina musu wayau ina barin su da abincin kedaran maza ga mai dadi da Dadin dand'ano,da nakan samu naci ko ba da yawa ba,ai yau ko a bakina ina gaya miki Engr ya ga Shigar Ashiru Office d'i na da kwandon abincin bai yi mgana ba sai da aka tashi sallah da cin abinci yaga mun zame jiki mun shige Office dina ya Rutsamu Maman nana"
Ammi ta zaro ido tana Fadin"Allah yasa ba laifi kuka yi ba?
Abba yace"Wani laifi..?ai shima cewa yayi an munafuncensa barin ma ni ban taba gayyatansa shima yazo aci abincin da shi ba,karshen ta dai wanda zan ci na bar mai ni da yunwa na yini wlh sai santi suke suna fadin muna jiran na gobe Engr Usman"
Ammi na Dariya tace"To sai kace musu me..?
Abba yace"Nace ba mai gajiyarmin da D'iya kunyar Engr naji domin da kansa yace a fada miki a sawo da nashi Gobe ba Baban Nana kadai ke kaduna ba"
Ya karishe fada yana Dariya Ammi ma Mirmishinta take yi kafin tace"Allah Sarki kada ya damu zan fad'ama Fa'i ta kara sanwa Hannunta ya yi albarka"
Abba yace"Ban so a rika wahalar da ita ba domin Engr ya yi mgana ba, har ni hakura zan yi mu rika cin wanda ma'aikata ta bamu"
Ammi tace"A'a bazai ayi haka ba. bazai gagara ba in sha Allahu"
Da farko Abba bai amimce ba Darajan Engr da ba abunda bazai iya masa ba yasa ya amince,ammh sai da ya kirani yamin mgana har da bani Hakuri ina Son Halin Abba mutum nagari mai sanin Darajan dan Adam
Ni ko nace masa bakomai na saba ba aikin da zai gagareni nan duniya.
Abba nata min godiya kamar bai isa dani ba.
Tunda ga ranar na kara sanwa a babban Tukunya nake yin girkin,a cika manyan kololi direba ya kai musu bayan abinci kullum da kalan lenukan da nake hada musu kala kala wadanda muka koya a katsina da kuma daman wadanda na iya tun a baya abinci ko kala kala nau'ika Dabam Dabam,ko wata rana da kalan Godiyan da Abba zai ce sun ce ayi min in ya dawo da farko sun zata Ammi ce ke yin girki daga baya ya fada musu Diyarsa ce to sun zata ko cikin ma yaran da ya Haifa ne.
Abba da kansa ya fad'amin wani cikin abokan aikinsa yace a jinjina min tabbas a gaisheni bai taba cin girki mai Dadin girki ma ba har ko na matarsa Ranar ma Dubu Ashirin Abba ya kawo min Sabbin yan Dubu Dubu yace gashi in ji Engr yace a kai ma yar Baiwa.
Ammi nata Dariya da naki karban Abba ya min tsawa yace maza na karba ai kyauta suka bani na wahalan da nake yi sai na karba,Itama Ammi da nace ta ciri wani abu ki tayi haka takemin ko Aikin Hada Turare na samu in na bata wani abu bata karba,Sai dai na bama su Hafsah kowacce dubu uku suna ta Murna.
Inno ma na bata Dubu ukun ta karba tana ta saka albarka tana nan idonta ya tashi tana ta fama da shi Baba Ati na Korafi bata dawo ba.
Yau da gobe bata bar komai ba,Har ga shi su Abba sun kamallah warkshop din su cikin nasara,Ranar da suka gama washegari bayan Abba ya fita ya kira Ammi a waya yace ayi girki na Mutum goma haka su Engr sun ce zasu zo godiya anjuma da Daddare.
A nan babban ma'aikantansu na NNPC da ke kaduna. in Abba ya fita tun safe sai dare Direba ke dawo da shi gida a gajiye. wanka kawai yake yi yaci abinci ya kwanta,kwana uku da Farawarsu ranar da daddare bayan ya dawo yana cin abincin da na Dafa na shigo ni kuma mu gaisa.
Ina zaune gefensa na Hagu Ammi na barayin Dama ganin ya share Mulmulen tuwon shinkafa guda uku da Ammi ta sakamai ammh kuma yana mganar ta karamai,jin haka yasa muka kallesa a tare ni da ita cikin mamaki tace"Na hudu fa kenan Baban Nana.."
Cikin ka'da kai yace"yunwa nake ji ne Maman Nana. rabo na da abinci tun karin da nayi na Safe fa."
Cikin mamaki tace"Tun Safe fa Baban Nana?baka ce min akwai restaurant guda da aka dauko suna baku abinci a wajen ba..?
Kai tsaye Abba ya kalleni kafin yace"D'iyata k'aramin tuwon nan kin ji,in na biye ta tambayoyin wannan uwar taku yunwar sai ta kara jigatani"
Ina Dariya kafin nayi mgana,Ammi ta zubamai ta karamai hade da miyar Ogun din da nayi wacce taji Bushasshen kifi da Kashin Rago.
Sai da ya fara ci sannan ya Dago yana Fadin"Wato maman Nana Allah ya yi ma Diyar nan taki albarka ta shagwabani da girke girkenta duk inda naje naci abinci in ba Dandanon Abincin ki ko nata ba,wlh baya kosar dani sam ga masu abincin sai ma abunda ka zaba ni dai wlh kada'n nake ci sai naji duk ba Dadi na gwammace in na dawo sai naci gabad'aya"
Ammi tace"Gaskiya to bari ka Hakuri kana ci zama da yunwa ina yaga amfani in wani cutar ta kama ka fa..?
Abun wanke hannu yace ta tara masa sai da ya wanke hannu da bakinsa sannan ya koma ya kishingida yana Hamdala ni na kwashe kayan zuwa Kitchen ban koma Falon Abba ba,sai na wuce dakin da na sauka nayi shirin kwanciya ban san kuma ya Abba suka karkare mganar ba da Ammi sai washegari Ammi ke kara min mganar cikin wasa tace"Jiya kin ji Baban ku da rigima. Kamar wani yaro yana zama da yunwa sai kaci abunda ke hannunka in ya dawo sai yaci na gida ba shikenan ba"
Nima cikin Dariyan nace"Ba matsala fa Ammi za'a iya yi masa abincin sai Direba ya rika zuwa yana karban masa'"
Ammi ta kalleni kafin tace"Ko..?duk wahala ce Fa'i bar rigiman Baban ku kin ji"
Ni kuma na Dage sai a rika yin haka Ammi ta tabe baki tana fadin"Ke mai Uba ko..?Allah ya ba da sa"a
Abba na dawowa ta fad'amai sai ya Daga waya ya kirani Lokacin ina waya da Badariya sai da muka gama naga kiransa sai na saka Hijabi zuwa Falonsa,a chan na iske Hafsah da Nana khadija suna ganina suka fara Rige rigen tashi Ammi ta kallesu tana Fadin"Daga gani baku da gaskiya ko..?
Ina Dariya nace"Ammi Wainar Fulawa na soya nafa saka musu nasu. daga shigata wanka suka zagayo suka Kwashe wanda na bari zan ci"
Ammi tace"mugaye shiyasa zasu gudu"
Dariya suka saka Nana Khadija tace"Bani bace fa Hafsi ce"
Hafsatu tayi saurin cewa"Wlh bani ba ce ni da bana cin wainar fulawa ma"
Hararanta nayi kafin nayi mgana ta kama kanta Abba waya yake yi shiyasa bai sakamana baki ba sai da ya gama su kuma Lokacin sun fice suna Dariya su san abunda suka aikata.
Zama nayi gefen Abba muka gaisa ya amsa cikin Sakewa kafin yace"Mamarku ta fad'amin kin ce bazaki bar babanki da yunwa ba ko.?
Ina mirmishi na Daga kaina kafin nace"To Abba kana damu meyasa zaka zauna da yunwa?
Abunda kake so shi za'ayi maka."
Jinjina kai ya yi Lokaci daya yana fadin"Nagode sosai Allah ya yi miki albarka yasa ya'yanki su rama miki.
Ammi ta amsa da Ameen kafin tace"Ba ka ce Allah ya bata miji nagari ba..?
Ina jin Haka na mike ina fadin"Abba mu kwana lafiya"
Ammi ta bini da Dariya tana Fadin"Diyar taka Baban Nana sai kayi da gaske ko wani gwaskan muka samu sai ta bamu kunya na lura da take takenta"
Abba ya murmusa kafin yace"kyaleta ba mai yi mata Dole. in ma bazata kara yin auren ba ina bayanta"
Ammi ta karkace baki kafin tace"Haba da kuruciyarta Baban Nana..?Allah zai kawo mata wani wanda zai kaunace ta saboda Allah ya rud'ata ta zo da kanta tana fadin Abba na amince masa"
Ta karishe fad'a tana Dariya Abba ya jinjina kai yana Fadin"Allah yasa ni dai a nawa shawaran ta daidaita da Baban yaran nan ishaq ya yi nadama sosai wlh in da zata koma da ni kaina naso hakan'"
Yana mgana Ammi na tabe baki sai da ya gama sannan tace"Nafi yi ma Fa'iza sha'awar sabuwar rayuwa akan ta koma Rayuwarta ta baya kwata kwata ishaq bai chanchanci a basa wani Dama ba, gwara haka dai kowa da nashi Kaddaran"
Kai kawai Abba ya kada kafin yace"Tunda baki son sa ai komai zaki ce, ammh duk in da zata je bai kai inda ta fara gina Zuru'arta ba azizat. da sabon yabe duk lalacewar tsoho wlh gwara tsohon yaben nan ni a ganina"
Ammi ta kada kai kafin tace"Wlh wani Sabon Yaben yafi tsohon sau Duhu"
Kyaleta yayi sanin Halinta ita ko taki Hakura tacigaba da fadin"kuma in kana mganar ya'ya ne ai sun saba da Rashinta,suna zaune gidan uban su in da ya dace da su ita kuma Allah ya bata wani mijin taje tayi auranta ta Huta taji dadinta"
Abba ya gyara zama yana fadin"Allah ya bata Azizat"
Dariya tayi kafin tace"Ameen Baban Nanas d'ina"
Girgiza kai yayi yana mirmishi kafin yace"'Allah ya shirya Maman Abdul'ahad'
Da Ameen ta amsa mai tana Dariya mganar Fa'iza suka rufe su ka kama na Raliya da mganar sai Walid ya yi kwari za'a shiryamata tafiya wajen mijinta.
******
Kamar yadda nayi alkwari ban sauya ba tunda ina nan ba ranar Tafiya. Goggo ma bata damu ba tasan daman Ammi nata korafin rashin zuwana,aranta daman tasan sai an ganni kawai,daman ni nake yin girkin Rana sai nake dib'arma Abba Ammi ta kirasa ya turo Direba ya Daukan masa ya kai masa watarana ma in ya makara sai dai a basket yake tafiya da abun karin nasa ya yi achan ba'a Rufe Sati ba Ranar Abba ya dawo yace yunwa yake ji sosai.
Ammi ta kallesa yana ragema Tie din wuyansa tsukewa tace"a'ah ina abincin da direba yakai maka..?
Kai ya girgiza kafin yace"Wani abinci..?ai ina gaya miki tun rana na biyu da Ashuru ya fara karbo'min abincin su Engr Bashir suka sakamin ido. wlh tun suna su biyu har sukamin gayya suna min tsiyan ina musu wayau ina barin su da abincin kedaran maza ga mai dadi da Dadin dand'ano,da nakan samu naci ko ba da yawa ba,ai yau ko a bakina ina gaya miki Engr ya ga Shigar Ashiru Office d'i na da kwandon abincin bai yi mgana ba sai da aka tashi sallah da cin abinci yaga mun zame jiki mun shige Office dina ya Rutsamu Maman nana"
Ammi ta zaro ido tana Fadin"Allah yasa ba laifi kuka yi ba?
Abba yace"Wani laifi..?ai shima cewa yayi an munafuncensa barin ma ni ban taba gayyatansa shima yazo aci abincin da shi ba,karshen ta dai wanda zan ci na bar mai ni da yunwa na yini wlh sai santi suke suna fadin muna jiran na gobe Engr Usman"
Ammi na Dariya tace"To sai kace musu me..?
Abba yace"Nace ba mai gajiyarmin da D'iya kunyar Engr naji domin da kansa yace a fada miki a sawo da nashi Gobe ba Baban Nana kadai ke kaduna ba"
Ya karishe fada yana Dariya Ammi ma Mirmishinta take yi kafin tace"Allah Sarki kada ya damu zan fad'ama Fa'i ta kara sanwa Hannunta ya yi albarka"
Abba yace"Ban so a rika wahalar da ita ba domin Engr ya yi mgana ba, har ni hakura zan yi mu rika cin wanda ma'aikata ta bamu"
Ammi tace"A'a bazai ayi haka ba. bazai gagara ba in sha Allahu"
Da farko Abba bai amimce ba Darajan Engr da ba abunda bazai iya masa ba yasa ya amince,ammh sai da ya kirani yamin mgana har da bani Hakuri ina Son Halin Abba mutum nagari mai sanin Darajan dan Adam
Ni ko nace masa bakomai na saba ba aikin da zai gagareni nan duniya.
Abba nata min godiya kamar bai isa dani ba.
Tunda ga ranar na kara sanwa a babban Tukunya nake yin girkin,a cika manyan kololi direba ya kai musu bayan abinci kullum da kalan lenukan da nake hada musu kala kala wadanda muka koya a katsina da kuma daman wadanda na iya tun a baya abinci ko kala kala nau'ika Dabam Dabam,ko wata rana da kalan Godiyan da Abba zai ce sun ce ayi min in ya dawo da farko sun zata Ammi ce ke yin girki daga baya ya fada musu Diyarsa ce to sun zata ko cikin ma yaran da ya Haifa ne.
Abba da kansa ya fad'amin wani cikin abokan aikinsa yace a jinjina min tabbas a gaisheni bai taba cin girki mai Dadin girki ma ba har ko na matarsa Ranar ma Dubu Ashirin Abba ya kawo min Sabbin yan Dubu Dubu yace gashi in ji Engr yace a kai ma yar Baiwa.
Ammi nata Dariya da naki karban Abba ya min tsawa yace maza na karba ai kyauta suka bani na wahalan da nake yi sai na karba,Itama Ammi da nace ta ciri wani abu ki tayi haka takemin ko Aikin Hada Turare na samu in na bata wani abu bata karba,Sai dai na bama su Hafsah kowacce dubu uku suna ta Murna.
Inno ma na bata Dubu ukun ta karba tana ta saka albarka tana nan idonta ya tashi tana ta fama da shi Baba Ati na Korafi bata dawo ba.
Yau da gobe bata bar komai ba,Har ga shi su Abba sun kamallah warkshop din su cikin nasara,Ranar da suka gama washegari bayan Abba ya fita ya kira Ammi a waya yace ayi girki na Mutum goma haka su Engr sun ce zasu zo godiya anjuma da Daddare.