Sashe 44
Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
******
Karfe Daya na ranar asabar din karshen mako,Dubban mutane suka Shaida Daurin auran *ENGR ABDULBASIT ABDULGHAFFAR ALUWATOSIN*
Tare da Amaryan sa *FA'IZA SIDI KAROFI* sauyin da aka same shi batare da kowa ya sani ba.
Abba shi ya yi ma Engr walicci Ya yin da Mallam ya zama waliyyina,Akan Sadaki Dubu Dari,kuma Engr ya biya da Cheque din banki tunda ba shi da Cash a hannunsa.
sannan Direban Engr ne kadai ya shaida Daurin auran sai shi Engr d'in cikin mutanensa, sai dai ya saka an Dauki komai Live ta Vedio call ga su Papa da Sweetheart da Sisters dinsa.
Daurin auran da ya faranta Zuciyar Engr sannan ya Kusa tafiya da Bugawar zuciyar Ishaq kabir karofi.
Engr gaban mutane acikin masallaci ya yi sujudul shukru kafin ya Daga ya hannayensa sama yana Fadin"Allah na gode maka. ba wayau na ba ne kuma Dubarata ba ne da ka bani Faa'iza amatsayin mata ba,Allah karka barni ni kad'ai ka yi min jagora wajen tafiyar da rikon Amanarta a tare dani"
Ba su Abba ba kowa dake masallacin nan Engr ya Burgesu ciki har da Jamal da yazo Daurin auran yayansa da ma wasu daga cikin abokansa sai sukaji Labari ya sha bambam.
Kallonsa kawai ake yi duk yayi zufa sai uban zare ido yake jamal ya taso yazo wajensa yana fadin"Yaya Ishaq ya haka..?
Sai a lokacin ya fara Nadaman abunda ya aikata duk da yayi nadaman tun ad'azu din ammh bai Taba Tunanin zai iya rasa Faa'iza a wannan gabar ba.
Ya dauka bata da wani zabi sai zabin shi da ya'yan su.
Idanuwansa sun tara kwallah dishi dishi yake hango Amir tare da Abba tun bayan da ya barsa nan bakin kofa bai kara ganinsa ba sai yanzu.
Kamar in ya gane manufar abun Amir ya fara Gudunsa kenan..?
Kenan yaji abunda ya faru tsakaninsa da Fa'iza..?
Innalillahi wani"inna ilaihirraju'un
Ya fadi a zucci da Sarari kamar yadda ya saki wannan salatin haka suma acikin gidan Goggo,Mama da su Anty Binta ke salatin lamarin.
Har Labari yazo cewa ba da Ishaq aka Daura aure ba da Engr ne.
*Janafty*
*KNKB3015*
*Na gaida ke,My Anty. Anty Sis♥️Kyakyawan sharhin ki yasa kin gama fad'in komai game da wannan labarin,Madallah da ke,Allah ya raya Zuru'a*
*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*
*AWANNI BIYU KAFIN DAURIN AURAN*.
A lokacin da na shige dakin Matar Yaya Salisu Zulaihat,bana cikin hayyacina zuciyata gabadaya tayi Duhu tare da wani irin kuncin da na jima ban jini cikin yanayin ba.
Kuka nake yi da hawaye da sautin muryata ina tuna kalaman Ishaq gareni da ya kirani Datti gaban Mutum mai karamci irin Engr.
Tunani nayi cewa har abada bazan yi kima a idon Ishaq ba,baya sona kuma bazai taba sona ba,ba abunda zai iya sauya wannan abun kawai dai akwai wani gibi ko bangaran da ni zan cike masa ne shiyasa yaso komawata garesa.
Ammh daga yanzu na fahimci komai kuma bazan kara bari rayuwata ta kara shiga wani hali ba,ya'yana na wa ne har kuma gaban Abada ba su da uwar da ta fini a wajen su,ko da sun Raunana na dan Lokaci ne zasu dawo daidai da yardan Allah.
Da wayar Yaya Salisu nayi amfani na kira Abba ina kuka daman na Haddace lambarsa sai da na saka naga shima ashe yana da lambarsa.
Jina cikin kuka da Damuwa yasa Abba yace na zauna a inda nake ga su nan zuwa shi da mallam bayan na fad'a musu ina gidan su Yaya isa.
Sai da naji muryan Abba na bude kofa ina kuka gabansu na zube na had'a Hannayena Biyu ina fadin"Abba in nace na fasa komawa gidan Ishaq ran ka zai baci..?ba zaka kalleni a wacce ta maida kai karamin mutum ba..?
Sai Abba ya saka Hannu ya Dago ni Cikin wani yanayi muka isa har falo kan Daya daga cikin kujerun falon ya zaunar dani su ma duka suka samu gefena suka zauna cikin Tausasawa Abba yace"Bazan taba cewa ba Fa'iza daman ai zabin naki ne ba namu ba ko ba haka ba Mallam..?
Sai ya jinjina kai yana fadin"kwarai da gaske"
Cikin kuka na zayyane ma Abba komai da ya faru tsakanina da Ishaq na karishe da fadin"Abba ko waye ka auramin shi ni dai ka taimaka kada ka auramin Ishaq Saboda yace ni Datti ce bazan je ce na gurbata masa Tarbiyan ya'ya ba'
Na karishe fad'a cikin gunjin kuka Abba ya yi shuru ransa ya baci ya kasa mgana Mallam ne yace"Subhanallah shi kuma ya zai yi haka..?Ana mganar aure kuma zargi na shigowa ciki"
Abba ya yi huci kafin yace"Ai shikenan bakomai daman zabin na baki da kaina ban miki katsalandan ba ne, saboda watarana ko bani ki iya sanin abunda ya dace dake. tunda yace haka ya gama mgana ba kwantai kika yi ba Fa'iza ke yar baiwa ce in yace ke Datti ce wani a Dattin zan bashi auranki kuma ya karba tashi ki je ki wanke Fuskarki ki kwantar da Hankalin ki insha Allahu bazaki ji kunya ba Allah zai nuna miki Ribar Hakurin ki tun a duniya."
Kalaman Abba suka sanyayamin rai duk da ban kawo ma Engr a lokacin ba, na riga na yanke hukunci gwara na auri koma waye da na koma ma Waye da auran Ishaq,bayan tafiyar su Abba ba jimawa sai ga Ammi ashe Abba ya yi mata waya yace tazo ta zauna dani.
Alokacin su kan su su Goggo ba su san abunda ya faru ba, ita kanta Abba bai yi mata bayani ba yace dai ina gidan su Isa taje ta zauna dani bayan tazo ne na zayyane mata komai..
Kyafci ta fara kafin tace"Uhm komai akayi da jaki daman sai ya ci kara mutum mai kima irin Engr ya yi ma wannan cin zarafin..?
Ina hawaye na kasa mgana saboda ni kaina kunyar kaina da abunda Ishaq ya yi ma Engr duk ya kamani,Ammi ta rika fada kamar zata ari baki tana fadin"Daman wata Daraja naki ya sani..?dan renin wayau ne fa Jaka ya maidake wacce bata da yanci ki koma ki cigaba da gadin gida da kula da mahaifiyarsa da ya'yansa da matarsa. to ai kuma yaci taliyar karshe ya'ya in bazai rike ba ya baki zaki hada ki rike abinku kuma na tabbatar da Engr wlh ko duka duniya kika haifa bazai gaza ba wajen rike miki su ba'
Ina tsiyayan hawaye nace"Ammi ni fa ban ce Abba ya auramin Engr ba. Cewa nayi ya bani duk wanda yaga Dama"
Ammi ta min dakuwa kafin tace"Kaji min sakarci in ya je ya aura miki wanda baki sani ba fa..?an rabu da bukar kuma sai a haifi Habu"
Ina kuka ne ammh sai da nayi dariya a raina nasan Abba uba ne na gari bazai taba min zabin da zai zama Cutarwa gareni ba, shiyasa ma ban damu ba ni dai tunda na sahale ma kaina Ishaq sai naji kamar an saukemin wani katon dutse mai nauyi daya tokaremin zuciya.
Cigiyata suka fara yi dagachan Gidan Goggo,tunda an ce ina ko tare da Abba ne sai aka kira Ammi tace tana tare dani,Yaya Salisu kuma na tare da Amir yana lallashinsa Domin yaga yaron ya shiga damuwa shi ko Amir kalaman Daada ne ke masa yawo a kwakwalwa tare da Kukan Umma sai yaji ya tsani Daada ta ya zai kira Umma da wannan sunan mara kyau..?
Kuma ya sakata kuka.?
Kawai don yana Da dauriya ne yasa bai yi kuka ba ammh duk yayi zuru zuru.
Abba da Mallam suka tattauna mafita batare da sun yi zencen da kowa ba. Engr na gidan inda Ishaq ya Fice ya barsa cikin kogin nadama,Hankalinsa ya tashi Tunanin abunda ya aikata kuskure ne bai zo mai ba sai da ya aikata wani kishin Fa'iza ne ya taso masa da yasa ya kasa iya Sarrafa kansa. kishin ta samu wanda ya fisa komai yace yana sonta shi ya Dauka bayan shi ba kuma wani namijin da Fa'iza zata Burgesa,yana da yakinin in ba shi ba,Fa'iza ba ta da kowa kuma yana takamar cewa shi da ta gujen ma wa bata da kamarsa sai ga shi Allah ya nuna masa Isharan sa da cewa ita Daukakan Allah ba ta zaba ba ne, Daukakarsa ta kowa da kowa ne koda kai ba kowan kowa ba ne in ya tashi zai Daukaka domin nuna izina ga maza ire iren su ishaq masu Tunani irin nasa.
Har ga Allah shi kan shi Engr bai san da Sauyin mganar ba sai da suka shiga masallaci Abba ya karkata ya ce masa ya kawo sadakin Fa'iza ya bashi auranta Engr sai yaji kamar bai ji da kyau ba, sai da Abba ya maimaita masa bashi da Cash sai cheque ya rubuta ya bada sannan ya kira Sister dinsa kafayatu Vedio call Papa na gida tunda Weekend ne ya bama Direbansa ya Daukan musu Daurin auran Live suka kallah duka duka Lamarin ya faru gaza da mintina talatin ne. sai akalan Fatan alherin ya koma ga Engr a madadin Ishaq da aka barsa baki Bude.
Engr bakinsa kamar zai Tsage daman ga shi ma'aboci mirmishi da Fara'a haka jama'a ke ta ba shi Hannu cikin masu hannu da shi har da Dr.Lawal bako. yazo Daurin auran Abba ya fad'amai Ishaq ma haka shi kan shi da yaga Engr sai da ya rankwafa Aiko a gidan giya akwai babba shi kan shi yasan yanzu ko yarsa zainab bata isa ta Dagama Fa'za kai ba,Tafita komai na Duniya Tunda ta samu miji a gefenta kamar Engr da ya taka matakan Rayuwa masu girma.
*******
Karfe Daya na ranar asabar din karshen mako,Dubban mutane suka Shaida Daurin auran *ENGR ABDULBASIT ABDULGHAFFAR ALUWATOSIN*
Tare da Amaryan sa *FA'IZA SIDI KAROFI* sauyin da aka same shi batare da kowa ya sani ba.
Abba shi ya yi ma Engr walicci Ya yin da Mallam ya zama waliyyina,Akan Sadaki Dubu Dari,kuma Engr ya biya da Cheque din banki tunda ba shi da Cash a hannunsa.
sannan Direban Engr ne kadai ya shaida Daurin auran sai shi Engr d'in cikin mutanensa, sai dai ya saka an Dauki komai Live ta Vedio call ga su Papa da Sweetheart da Sisters dinsa.
Daurin auran da ya faranta Zuciyar Engr sannan ya Kusa tafiya da Bugawar zuciyar Ishaq kabir karofi.
Engr gaban mutane acikin masallaci ya yi sujudul shukru kafin ya Daga ya hannayensa sama yana Fadin"Allah na gode maka. ba wayau na ba ne kuma Dubarata ba ne da ka bani Faa'iza amatsayin mata ba,Allah karka barni ni kad'ai ka yi min jagora wajen tafiyar da rikon Amanarta a tare dani"
Ba su Abba ba kowa dake masallacin nan Engr ya Burgesu ciki har da Jamal da yazo Daurin auran yayansa da ma wasu daga cikin abokansa sai sukaji Labari ya sha bambam.
Kallonsa kawai ake yi duk yayi zufa sai uban zare ido yake jamal ya taso yazo wajensa yana fadin"Yaya Ishaq ya haka..?
Sai a lokacin ya fara Nadaman abunda ya aikata duk da yayi nadaman tun ad'azu din ammh bai Taba Tunanin zai iya rasa Faa'iza a wannan gabar ba.
Ya dauka bata da wani zabi sai zabin shi da ya'yan su.
Idanuwansa sun tara kwallah dishi dishi yake hango Amir tare da Abba tun bayan da ya barsa nan bakin kofa bai kara ganinsa ba sai yanzu.
Kamar in ya gane manufar abun Amir ya fara Gudunsa kenan..?
Kenan yaji abunda ya faru tsakaninsa da Fa'iza..?
Innalillahi wani"inna ilaihirraju'un
Ya fadi a zucci da Sarari kamar yadda ya saki wannan salatin haka suma acikin gidan Goggo,Mama da su Anty Binta ke salatin lamarin.
Har Labari yazo cewa ba da Ishaq aka Daura aure ba da Engr ne.
*Janafty*
*KNKB3015*
*Na gaida ke,My Anty. Anty Sis♥️Kyakyawan sharhin ki yasa kin gama fad'in komai game da wannan labarin,Madallah da ke,Allah ya raya Zuru'a*
*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*
*AWANNI BIYU KAFIN DAURIN AURAN*.
A lokacin da na shige dakin Matar Yaya Salisu Zulaihat,bana cikin hayyacina zuciyata gabadaya tayi Duhu tare da wani irin kuncin da na jima ban jini cikin yanayin ba.
Kuka nake yi da hawaye da sautin muryata ina tuna kalaman Ishaq gareni da ya kirani Datti gaban Mutum mai karamci irin Engr.
Tunani nayi cewa har abada bazan yi kima a idon Ishaq ba,baya sona kuma bazai taba sona ba,ba abunda zai iya sauya wannan abun kawai dai akwai wani gibi ko bangaran da ni zan cike masa ne shiyasa yaso komawata garesa.
Ammh daga yanzu na fahimci komai kuma bazan kara bari rayuwata ta kara shiga wani hali ba,ya'yana na wa ne har kuma gaban Abada ba su da uwar da ta fini a wajen su,ko da sun Raunana na dan Lokaci ne zasu dawo daidai da yardan Allah.
Da wayar Yaya Salisu nayi amfani na kira Abba ina kuka daman na Haddace lambarsa sai da na saka naga shima ashe yana da lambarsa.
Jina cikin kuka da Damuwa yasa Abba yace na zauna a inda nake ga su nan zuwa shi da mallam bayan na fad'a musu ina gidan su Yaya isa.
Sai da naji muryan Abba na bude kofa ina kuka gabansu na zube na had'a Hannayena Biyu ina fadin"Abba in nace na fasa komawa gidan Ishaq ran ka zai baci..?ba zaka kalleni a wacce ta maida kai karamin mutum ba..?
Sai Abba ya saka Hannu ya Dago ni Cikin wani yanayi muka isa har falo kan Daya daga cikin kujerun falon ya zaunar dani su ma duka suka samu gefena suka zauna cikin Tausasawa Abba yace"Bazan taba cewa ba Fa'iza daman ai zabin naki ne ba namu ba ko ba haka ba Mallam..?
Sai ya jinjina kai yana fadin"kwarai da gaske"
Cikin kuka na zayyane ma Abba komai da ya faru tsakanina da Ishaq na karishe da fadin"Abba ko waye ka auramin shi ni dai ka taimaka kada ka auramin Ishaq Saboda yace ni Datti ce bazan je ce na gurbata masa Tarbiyan ya'ya ba'
Na karishe fad'a cikin gunjin kuka Abba ya yi shuru ransa ya baci ya kasa mgana Mallam ne yace"Subhanallah shi kuma ya zai yi haka..?Ana mganar aure kuma zargi na shigowa ciki"
Abba ya yi huci kafin yace"Ai shikenan bakomai daman zabin na baki da kaina ban miki katsalandan ba ne, saboda watarana ko bani ki iya sanin abunda ya dace dake. tunda yace haka ya gama mgana ba kwantai kika yi ba Fa'iza ke yar baiwa ce in yace ke Datti ce wani a Dattin zan bashi auranki kuma ya karba tashi ki je ki wanke Fuskarki ki kwantar da Hankalin ki insha Allahu bazaki ji kunya ba Allah zai nuna miki Ribar Hakurin ki tun a duniya."
Kalaman Abba suka sanyayamin rai duk da ban kawo ma Engr a lokacin ba, na riga na yanke hukunci gwara na auri koma waye da na koma ma Waye da auran Ishaq,bayan tafiyar su Abba ba jimawa sai ga Ammi ashe Abba ya yi mata waya yace tazo ta zauna dani.
Alokacin su kan su su Goggo ba su san abunda ya faru ba, ita kanta Abba bai yi mata bayani ba yace dai ina gidan su Isa taje ta zauna dani bayan tazo ne na zayyane mata komai..
Kyafci ta fara kafin tace"Uhm komai akayi da jaki daman sai ya ci kara mutum mai kima irin Engr ya yi ma wannan cin zarafin..?
Ina hawaye na kasa mgana saboda ni kaina kunyar kaina da abunda Ishaq ya yi ma Engr duk ya kamani,Ammi ta rika fada kamar zata ari baki tana fadin"Daman wata Daraja naki ya sani..?dan renin wayau ne fa Jaka ya maidake wacce bata da yanci ki koma ki cigaba da gadin gida da kula da mahaifiyarsa da ya'yansa da matarsa. to ai kuma yaci taliyar karshe ya'ya in bazai rike ba ya baki zaki hada ki rike abinku kuma na tabbatar da Engr wlh ko duka duniya kika haifa bazai gaza ba wajen rike miki su ba'
Ina tsiyayan hawaye nace"Ammi ni fa ban ce Abba ya auramin Engr ba. Cewa nayi ya bani duk wanda yaga Dama"
Ammi ta min dakuwa kafin tace"Kaji min sakarci in ya je ya aura miki wanda baki sani ba fa..?an rabu da bukar kuma sai a haifi Habu"
Ina kuka ne ammh sai da nayi dariya a raina nasan Abba uba ne na gari bazai taba min zabin da zai zama Cutarwa gareni ba, shiyasa ma ban damu ba ni dai tunda na sahale ma kaina Ishaq sai naji kamar an saukemin wani katon dutse mai nauyi daya tokaremin zuciya.
Cigiyata suka fara yi dagachan Gidan Goggo,tunda an ce ina ko tare da Abba ne sai aka kira Ammi tace tana tare dani,Yaya Salisu kuma na tare da Amir yana lallashinsa Domin yaga yaron ya shiga damuwa shi ko Amir kalaman Daada ne ke masa yawo a kwakwalwa tare da Kukan Umma sai yaji ya tsani Daada ta ya zai kira Umma da wannan sunan mara kyau..?
Kuma ya sakata kuka.?
Kawai don yana Da dauriya ne yasa bai yi kuka ba ammh duk yayi zuru zuru.
Abba da Mallam suka tattauna mafita batare da sun yi zencen da kowa ba. Engr na gidan inda Ishaq ya Fice ya barsa cikin kogin nadama,Hankalinsa ya tashi Tunanin abunda ya aikata kuskure ne bai zo mai ba sai da ya aikata wani kishin Fa'iza ne ya taso masa da yasa ya kasa iya Sarrafa kansa. kishin ta samu wanda ya fisa komai yace yana sonta shi ya Dauka bayan shi ba kuma wani namijin da Fa'iza zata Burgesa,yana da yakinin in ba shi ba,Fa'iza ba ta da kowa kuma yana takamar cewa shi da ta gujen ma wa bata da kamarsa sai ga shi Allah ya nuna masa Isharan sa da cewa ita Daukakan Allah ba ta zaba ba ne, Daukakarsa ta kowa da kowa ne koda kai ba kowan kowa ba ne in ya tashi zai Daukaka domin nuna izina ga maza ire iren su ishaq masu Tunani irin nasa.
Har ga Allah shi kan shi Engr bai san da Sauyin mganar ba sai da suka shiga masallaci Abba ya karkata ya ce masa ya kawo sadakin Fa'iza ya bashi auranta Engr sai yaji kamar bai ji da kyau ba, sai da Abba ya maimaita masa bashi da Cash sai cheque ya rubuta ya bada sannan ya kira Sister dinsa kafayatu Vedio call Papa na gida tunda Weekend ne ya bama Direbansa ya Daukan musu Daurin auran Live suka kallah duka duka Lamarin ya faru gaza da mintina talatin ne. sai akalan Fatan alherin ya koma ga Engr a madadin Ishaq da aka barsa baki Bude.
Engr bakinsa kamar zai Tsage daman ga shi ma'aboci mirmishi da Fara'a haka jama'a ke ta ba shi Hannu cikin masu hannu da shi har da Dr.Lawal bako. yazo Daurin auran Abba ya fad'amai Ishaq ma haka shi kan shi da yaga Engr sai da ya rankwafa Aiko a gidan giya akwai babba shi kan shi yasan yanzu ko yarsa zainab bata isa ta Dagama Fa'za kai ba,Tafita komai na Duniya Tunda ta samu miji a gefenta kamar Engr da ya taka matakan Rayuwa masu girma.
*******