← Book details Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 71

Sashe 35

Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

*Tosin..#*
*Ishaq..#*
*FAA'IZAA...#*

*Janafty*

*KNKB3012*

*Goron Tula*

*Ingantaccen maganine dake saukarda niimar mace sannan dadin dadawa fruit ne ga dadi abaki zakine dashi chakwai sannan bashi da wata illa yadda kikasan fruit haka yake*
*yana da matukar kyau da tasiri ga ma aurata daga mace harna mijin Kuma munada Syrup nasa da akataceshi sannan aka hada da ingantattun magunguna dasuke temakawa ma aurata kwarai don inganta lafiyarsu dakuma maganin matsalarsu ta auratayya yana saukar da niima sosai yana karawa mace dadi fiye dazatanku sai kingwada zak ibada labari insha Allah*

*Sannan akwai zumar kiba*
*Duk macen dake son ta murmure tayi kyau taciko tatada komad'a sosai shaf dinta yafito sosai da sosai to tasha wannan zumar insha Allah zaki gode min*

*Zumar gyara nono*
*Zasu yi kyau suciko ammanfa bawai su tsaya ba😄 zadai suciko suyi kyau sosai insha Allah*

*Zumar hips*
*Indai kinsha zumar nan to hips dinki zai bude zasu yi kyau suciko sosai zaki godemin nina fadamiki insha Allah*

*Note magungunan mu ingantattune basu da side effects kokad'an anyisu da ingantattun*
*magunguna sosai*
*Location Gombe munaturawa ko ina 08030861857*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*

Gabadaya sai naji yar natsuwar da na fara samu kamar an kwace min ita,jikina ya yi sanyi.
Gabbaina sun rusuna,ina kaunar yarana sannan zan iya yin komai saboda naga sun dauwama cikin farinciki sai dai ya zan yi da Engr..?wata zuciyar tace min Sannu Fa'iza riga mallam masallaci Daga had'uwa yau har kin fara tunanin ya zaki yi da shi..?
Sai kaina ya fara wani Dum! eh yau kawai muka na hadu da shi ammh ya yi nasara dawo min da natsuwan da tayi shekaru da kwacemin,sai dai kuma kamar natsuwar ta wucin gadi ce tunda yanzu tana neman ta kwace daga gangan jikina.
Kasa ma fita nayi gabadaya kunya da nauyi tare da sanyin jiki sun haifarmin da kasala ban karya ba ina jin cikina na kukan yunwa ammh Bakina bazai iya karban wani abinci ba.
  Ammi ce ta gaji da jiran fitowata ta Biyoni har dakina ta sameni kunsan dai Ammi ba ruwanta Turkeni take yi sai da na fad'amata yadda muka yi da Engr ai sai ta kama Hanci ta saki Guda kafin tace"Wlh kin yi miji Fa'iza ba domin Engr me kudi ba ne, nake fada miki haka ba,sai domin kyakyawan Hallayansa mutun ne nagari mai kima da sanin Darajan d'an adam ina miki albishir da cewa kin yi miji. mijin da acikin maza Dubu babu kamarsa kada ki tsaya wasa haske ne Allah ya kawo miki ki karbesa hannu Bibbiyu ki yi kuma addu'a muna zamu tayaki. muna nan dake watarana da bakin ki sai kin ce Engr mijin Nuna ma duniya da Tsara ne Fa'i"
Haka ta zauna tana karantomin Hallayar Engr tana kara fito da shi a idanuwana ni ko na kasa ce mata komai har ta fice daga Dakin na shiga wani yanayin da mata ire ire na suke shiga to ni me nake da shi da ya ganni yaji yana sona..?
Amsar da na kasa bama kaina kenan. Ranar ko inno ban je na gaisar ba sai da yammah abinci ma Ammi tayi bata nemeni ba ta barni nayi tunani Abba kuma ban yarda ma mun had'u ba kunyarsa nake ji.
Ammh fa Tunanin Engr bai bar zuciyata ba motsi kadan sai ya fadomin arai sai naji Farinciki ya kamani,ya kirani da rana lambarsa na gani na gane kunya da nauyi suka hanani Dauka sai ga Sakon shi.

"Bamu yi haka da ke ba Fa'iza,a sharadin ki ba bu rowar jin muryan ki mai dadi. Ki taimaka ma Bawan Allah Tosin yaji muryan Matarsa"

Sakon sa ya bani Dariya wai matarsa mutumin nan fa yana da karfin Hali,sai Dare ya kara kirana na Dauka ina Dauka ya sauke ajiyar rai yana Fadin"Har kin sa naji d'adi, zuciya ta tayi Sanyi"
Cikin alamun waka ya fad'a da bansan Lokacin da na kwashe da Dariya ba  Shima sai ya yi Dariyan kafin yace"Tosin din Fa'izaa ne ke mgana ina Fatan kin gane..?
Ina mirmishi nace"Na gane mana ammh ni ba Tosin dina ba ne"
Da Sauri yace"Naki ne mana. Wlh Tosin din nan naki ne Engr Abdulbasit ne na mutane"
Sai naji na kasa musa mai bakinsa ne ya Bude ya cigaba da min Hira yana Fad'amin yana kano gidan Granny din sa tun dazu ta hana shi tafiya zai kwana sai gobe zai wuce Edo yana da Meeting da rana.
Ayyah kawai na iya ce masa kawai sai ya karya wuya yana Fadin"Gaskiya Faa'izaa ba haka ake yi ba. Sai nayi ta kiran waya baki dauka ba. Sannan Dazu kin yi min laifi kika gudu bamu yi sallama ba"
Sai nima naji ban kyauta ba cikin yanayin mganata nace"Kayi hakuri"
Da sauri yace"An yafe miki. ai amarya bata laifi ko ta kashe dan masu gida"
Ni ko nace bata dai kashen ba ne shi kuma sai ya gyara murya yana Fadin"To ki bari ki zo zan jawo miki Taye da kahinde ki kashe su ki gani ai Godiya zan miki ma duk cikin so ne"
Ina mamakin sunayen da ya kira cikin sigar tambaya nace"Taye da kahinde..?
Sai ya yi mirmishi kafin yace"na manta ke baki iya yarenmu ba ko..?kamar kin koya kin gama in dai muna tare.
Taye and Kahinde Twins name ne da Yaroba,Sister na Twins ne ammh asalin sunayen su Kafayatu Abdulghaffar BIMFE,and Sharifatu Abdulghaffar ERIMIPE."
Cikin jinjina kai nace'Tab kowa sai an sakamai sunan yaren naku ne.?
Yana dariya yace"Sosai ke ma ai zan saka miki naki"
Ina rike bakina nace"Fada mu ji"
Sai yayi shuru kamar yana tunani kafin kuma yace"Naki wayan sai nazo,Gani ga ki sai na fad'a miki naki sunan"
Dariya nayi ina hasaso ni da sunan yarbawa wayaga diskindarid'i,hira muka cigaba da yi yawan hiran daman nasane na barkwanci da ban Dariya sai 11pm yace naje na kwanta zamu yi mgana da Safe,ni ina ma na san Dare ya yi haka kai Fa'iza kam na zake da yawa haka na kwana mafarkin Engr da Safe da naje gaida Inno,bayan mun gaisa ta kalleni tana Fadin"Naji abun alheri wajen Aziza..Bawan Allah ne mai halin kirki ne matuka Baban ku yasan karamcin sa in kika amince masa bazaki yi nadama ba Fa'iza, sai dai bamai yi miki Dole kamar yadda Baban ki ya fada duk abunda kika zabama kanki daidai ne Allah ya sanya Alheri"
Na kasa amsawa a fili sai acikin zuciyata haka na koma daki jikina a sanyaye,ina ko daukan wayata nagama ya kirani har sau uku ina shirin kiransa sai ga shi ya sake kirana ina Dauka yace"Gaskiya ni dai ba'a kyautamin ba gaskiya"
Ina mirmishi nace"Da aka yi me ne..?
Sai ya basar yana fadin"Kin ta shi lafiya?nace lafiya lau muka gaisa nan yake fadamin zai bar kano Jirgi zai bi zuwa chan Edo din ba zato fa tsammani naji yana mgana sama sama sai naji wata yar tsohuwa na kwalamin sallama na amsa na gaisheta cikin girmamawa da ta fara kwarara mana addu'o"i sai da naji kwallah ta zuromin tsohuwar nan akwai addu'a a bakinta.
Sai da ya karbi wayar ne kafin nayi mgana ya rigani da cewa"Hajiya ce kakata ta bangaran uwa. na bata labarin ki ne sai kuma taji muna waya sai tace na bata ku gaisa,sai na bata ai kin ga yawan gaisuwa yafi yawan Fada ko Faa'izaa..?
Sai nayi Dariya kafin nace"Hakane Engr"
Yana kada Harshe yace''Laalaa aiko zamu bata ke ma Engr ne a bakin ki..?
Sai da na rufe bakina kafin nace"To Ko Tosin zan ce...?
Yanayin mganata yasa yadda na fadin Tosin sai da naji kyatatan Dariyan sa kai kawai yake girgizawa yana Fadin"Zan rama ne zan rama Faa'iza"
Da wannan hiran muka yi sallama yace zamu yi mgana bayan ya sauka,ammh yana Filin jirgi sai da ya Kirani daman ina Daki waya a kirjina kamar yasan Tunaninsa nake ina Mirmushi ni kadai.
Da rawan jiki na dauka ko sallama ban gama yace"Sharadin mu gobe ne ko Faa'izaa..?
Cikin mamaki nace'Sharad'in me..?
Sai kawai ya yi mirmishi kafin yace"Ashe zan dawo kaduna yau kuwa..?har kin manta..?
Ina jin haka na fara dariya sai shi kuma ya kanne yana Fadin"Kwana uku zan yi a Edo zan shiga gida Benue dagachan zan je Abuja, wlh bakin nan nawa bai Haila sai na gama yadaki a Dangi gabadaya"
Da Sauri nace"Kai don Allah kamar wata yarinya..'"
Shima kai tsayen yace"Yarinya ce mana shekaran ki nawa..?
Kai tsaye nace"35..ban karisa ba ma sai watan jibi"
Irin Dariyan da ya yi ta nishadi kafin yace"Ashe ma da yarinya nake mgana.  Ni ai ban ga  baban mace ba yarinya danya Sharaf zan dauka nima ta jikani da yarintarta na dawo Dan Saurayi shar dani"
Dariya ta kamani kafin nace"da Furfuran zaka dawo yaro.?ni kuma da ya'yan hudun zan zama yarinya sharaf.?
Yana shafa kansa kamar ina kallonsa yace"Ke bar wannan mganar muma fa Tsiffon nan mun iya romancewan nan ko wasu matasan albarka,bar ganina haka Tsab zan dawo dake yarinya Dayan sharaf dake abun da duk mun san komai"
Ya karishe fad'a yana Dariya kunya ta saka na kashe wayar yana ta kira ban Dauka ba kawai sai ga sakon shi.

"Karya nayi Tosin da Faa'izaa basu san komai ba..?
Chapter 35 · 0% Book details