← Book details Hadin Kai Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 50

Sashe 48

Hadin Kai Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shike Nan tunda kina so iya gobe Dole mu koma gida yaushe rabona dake sai ja min Rai kikeyi sabo da kin San Ina sonki da yawa,Murmushi nayi tare da Furta nimafa Ina sonka ka sani ma cikin Sigar rada rada Wanda hakan da nayi har cikin jininsa Wanda yasa ya fisgoni na Fado jikinsa ya rungumeni a jikinsa Yana cewa I love you tare da kissing dina Ni kaina Me too na iya furtawa Ina kissing nasa kamar zamu cinye bakunan junanmu har wani sauti kisses din suke fitarwa Wanda na kusa ma sai yasan Ana tsotse tsotse kamar mayunwacin jariri na tsotsar Nonon uwarsa , janye jikina nayi Zan bar wajen ya rike min hannu tare da cewa pls Help me muje Part dina nasan me yake nufi, nace kasan fa Hajiyarmu tana jirana fa,zuciyarsa ta tunzura matuka da Jan ran da nake Masa,ya kalleni sosai yace daga yau bazan Kara tambayarki ba Inshallah Kuma Zaki zo ne kema,Dariya ya bani ma nace to ai Ni Zan nemeka in ma baka zo ba Ni zanzo ai,Zaki gani Ni kadai Zan koma kwana tunanina Wasa yake yace jeki na mike na tafi ban San gwada Ni yayi ba.
Tuni nayiwa yan aikina waya sun shirya abinci da gyaran ko Ina na gidan namu nace Anjima Zan zo da Yan uwana ai kuwa gida yasha gyara.

1:30pm munyi sallah mukayi wanka mota biyar akayi kusan gaba daya Yan gidan su Ice har kaka Hajjo,Ya Salman,Musa da Hajiyarmu motarsu daban,Abbu da Daddy suna tasu,Ni da Angon nawa motarmu daya yanda mukayi wankan kamar Ango ka rantse party zamuje na biki.
Tun daga unguwar kowa ya Zama Dan kallo kamar Yan kauye,Daddy Mashaallah kawai yake cewa tsarin gidan kawai ya gigita kowa duk zaga Duniyarsu sai da gidan ya firgitasu sabo da kyau da gani an narka dukiya ba kadan ba.
Basu Gama Shan mamaki ba sai da muka Shiga ciki tuni Mata an fara daukan selfie kyas..kyas,ko Ina kamshi da sanyi,Basu ko zauna ba sai da suka zagaye gidan ko Ina Ice Yana nuna musu, Hajiyarmu harda kukan murna yarta ce a wannan gida Haka,Abbu kuwa tare dasu Ya Salman kasa magana sukayi,Bayan an nutsu Daddy da Abbu suka dinga zuba Albarka da Addua sannan nasa Yan aiki aka kawo abinci iri iri Wanda shi kanshi Ice yayi mamakina dana tsara hakan Kuma yaji Dadi na Kara birgeshi,a Nan akayi lunch kowa yaci ya koshi Ana murna Hira da farin ciki.
Sai wuraren Magrib Daddy yace su taso a koma gida gaba daya,Abbu yace to Fadila mu munyi Sallama dake ki zauna dakin mijinki gobe mijinki ya siya Mana ticket na jirgi 9am zamu tafi sai kinzo ganin gida Kuma.

Fuska na hade nace haba dai ai tare zamu tafi mu kwana in kun tafi sai na dawo gobe,muna hada Ido da Danbature ya gasa min uwar Harara, Hajiyarmu ta bude Baki tace bakya Jin magana ko? ko Haka kika ga Mata nayi? Shuru nayi shi kuwa Ice Dadi yaji harda min gwalo, Daddy ka gani ko? Me ya faru ya tambaya nace gwalo yake min Yana tsokanata,Dariya akayi Baki daya yace kyaleshi idan kika je ganin gida sai kinyi 2wks, gwalo Nima na Masa na rama nace Allah kaimu kowa ya ce Ameen.
Har mota na rakasu mukayi sallama,Ya Salman yace baza kiyi kuka ba zamu tafi,Dariya nayi Ina jikin motarsu nace Ina tare da Danbaturena na nunashi da yatsa yana wurin Hajiyarmu da Abbu suna ta magana ban San me suke cewa ba,Hannu Musa ya Miko min muka tafa yace na tuna sanda yarinyar Nan take barka Mana kuka kullum sai mune muke zuwa mu zauna tare da ita,ga Abbu yace ba gidansa ba,sai tace shike Nan mutuwa zanyi ya Salman ya gwada muryata muka shekewa da dariya na zura Hannuna ta glass na mintsini Musa a wuya,yayi Kara kadan,Ice Yana kallonmu Yana magana da Abbu,Bayan sun Gama suka tafi driver yaja mota Ina daga musu hannu.

Danbaturena ya karaso inda nake yace to Allah ya kawo mu yau gaki gani daga Ni sai ke,Zaki San wa kika yiwa,dama na taraki da yawa,Bari naje gidan su Ayman dama yayi min sabuwar budurwa zamuje na ganta idan tayi min na karo Miki ita na huce takaicin mace daya sai Hawan jini kike sani.
Tsoro naji tunanina da gaske yakeyi sabo da yace dama zaiyi maganina, cumb ya zaro karami a aljihunsa ya sake taje gashinsa a gabana sannan ya Shiga Mota tare da janta cike da salon kwarewa ya tafi abinsa ya barni Nan tsaye.

Kishi ya turnukeni katsam sai ga wayar mutumin dake kirana ya Kira,da sauri na daga cike da balai nace dalla Malam ka daina kirana nafi karfinka me zanyi da Kai fasiki aikin banza kawai Kai dakikin Ina ne jahili,dabba,asararre anyi asarar haihuwa wlh matsiyacin banza duk yanda akayi a baya a goye aka zo dakai gidan ubanka Dan shege ne Kai ba ta halak aka sameka ba,marar zuciya Wanda Kare ya dauke.
Murmushi me Sauti ya saki yace kin jawowa kanki wlh sai na nuna Miki iyakarki, zuciyata Kuma ba Kare bane kadai ya dauke harda Zaki da damisa ne suka dauketa.
Tsaki naja tare da kashe wayata Baki daya na koma ciki abina tuni masu aiki sun gyara kitchen da ko Ina da Baki suka Bata.
Saman bed kawai na kwanta Ina tunanin Danbaturena ko da gaske wajen wata ya tafi,a fili nace kan uba ai wlh sai dai ya sakeni kawai Ina bazai yuwu ba.

AsmaBaffa
[9/4, 10:26 PM] Sis Asma: 🏕HADIN KAI🏕

96-100

Official

By
AsmaBaffa

FINAL

WANNAN PAGE NA DUKKAN MASOYA ASMABAFFA NE MAKARANTA NOVELS DINA.

WANDA BAN SAMU DAMAR BAKU PAGE BA KUYI HAKURI KUYI MIN AFWA INSHALLAH NAN GABA ZAN BAKU.

Muna kwance cikin dare zazzabi me zafi ya rufeni da kyar nake motsi,jikina zafi zau,sai Nishi nakeyi da rawar sanyi,karkawar da nakeyi itace tayi sanadin tashin Danbature daga baccinsa me Dadi, jikina ya taba yaji zafi zau kamar Zan Kama da wuta yace Innalillahi wannan zazzabi gwara kawai ya dawo jikina na huta Akan ya taba min lafiyar Beauty na,kullum sai yazo ya Hana min ke sakewa,duk da Ina cikin cuta naji dadi da sanyin kalamansa Wanda har ban San Ma nayi Dan dariya ba kadan,kayan jikina ya cire min kaf ya Shiga toilet ya ebo ruwa shi ba me sanyi ba baza Kuma ace me zafi ba,da towel ya Shiga goge min jiki na kamar yanda ya Saba min kullum,Magani nace ko zaka bani Paracetamol?

A'a Mahaukaci ne Ni na sani ko ciki kika samu na Baki magani bada sanin doctor ba ya zube,to Bari kiji gobe dole muje asibiti ko kina so ko ba Kya so,Shagwaba na fara Masa Ni Allura zasu yi min,Bari kiji ko bana nan karki sake Kisha magani sai dole Munje asibiti, zafin jikin nawa ya ragu sosai ya maida komai toilet ya dawo ya kwantar Dani saman jikinsa ya lullubemu Baki daya Yana shafa gashina tare da bayana Yana min sannu,duk ya damu sosai sai lallabani yakeyi,nace karka ji zafi kaima ka Shiga blanket Kuma ba a sanyi Danma da ac.
Ai Ina Jin halin da kikeji Nima Zazzabin ya kamani shi yasa na shige tare da ke,kin San kuwa irin son da nake miki,wlh da gaske akan ciwo ya kamaki gwara ya shigeni,kamar Zan dauke Miki ya dawo kaina Haka nake ji Allah ya Baki lfy kinji Yar balarabiyata,Ameen na Furta zuciyata fari Kal sai naji Ciwon ma duk ya gudu sabo da dadin kalamansa.

Washe gari fes muka tashi,kafin mu fito har Saddiqa tare da Mum sun shirya Breakfast lafiyayye,Muna ci Ina tsokanar Saddiqa yau zata koma gidan mijinta ita kanta murna takeyi ta Matsu ta koma ta rigada ta Saba da jikin mijinta,sai zumudi takeyi, Muna breakfast kuwa sai ga Dr yazo tafiya da Abarsa Babu Wanda yace komai ta fito da kayanta Wanda Meena ta ebo Mata a gidanta ta fito tayi Mana sallama muka rakasu Mota suka tafi Bayan Mum ta Kara Jan kunnensa.
Mu kuwa Shirin zuwa Hospital mukayi,Shadda muka sa Sea blue iri daya munyi anko,duk Wanda ya kallemu sai ya Kara,Asibitin Dr who katafare mukaje aka dauki fitsarina sukayi gwaji sai gashi an gano ina da ciki na wata biyu da Sati daya,Murna kamar zamuyi ihu musamman Ice,kafin ace me duk ya watsa labarin,shawarwari da Magunguna suka bani muka dawo gida,Mum murna kamar me,Haka Yan uwan Ice da dangina,Daddy kuwa tunda yaji labarin ya dinga murna Yana Mana Addua sannan yace Next month zai dawo zai je daurin auren su Ya Salman.
Kannan su Ice da yayye sai zuwa dubani sukeyi suna Murna.

Attine ma takanas tazo ta yini,sannan take sanar min an kusa bikin Safarau yarta,Ko da na sanarwa Ice cewa yayi ya dauke komai zaiyi kayan daki da komai,sannan ya bawa Attine jari me yawa,munji Dadi har ban San da me Zan saka Masa ba.yanzu dangin Mijina muna zaune lfy suna kawo min ziyara Nima Ina zuwa,yau saura kwana uku bikin Safarau zata auri manager na Company nasu,bikin Rana daya Dana Saad abokin Ice Wanda ya hadamu yayi Mijin karya.naci na fara yi Lallai sai ya barni naje biki nayi kwana biyu,shi Kuma yace muna gari daya bazai iya barina ba sai dai kullum ya kaini ya dakko Ni,fushi nakeyi dashi,da yamma Mum ta fita unguwa gidan kawarta ni kadai ce a gida Ina zaune nasha kyau,sabo da cikin jikina yasa na Kara wani fresh da kiba,Apple nake ci.
Chapter 48 · 0% Book details