Sashe 8
Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" to nidai ko shi'a asibiti ba likita ba billahillazi ya kiyayi had'uwarmu, bamai kyauta ba aha" sannan ya fita yana huci kamar zaki.
Laure dake gefe tunda ya shigo gidan batace uffan ba, hasalima ko inda yake bata kalla ba saboda tsabar takaici, yanzu idan ba rashin tunani ba taya za'ace gardi kamar Jauro ya ringa shigowa mutane gida kamar gidansu, siririn tsaki taja, Wanda yayi dai-dai da maganar Iya Hari.
"To isasshiya, tsigaggga, sai kitahi ki bashi hak'uri, ke wani lahe kamar d'iyar arziki, shegiya me bak'ar aniya."
Itakam bataga dalilin bashi hak'uri ba, koda kuwa an bada ita gareshi balle ba'a bayar ba...."kin tashi kin tafi kosai nayi mid'imid'i dake anan niya" iya Hari ta katse mata tunani aiko tana shirin d'aukar muciya, aiko a guje tayi soro gidan ba shiri.
Yana tsaye yana jiran fitowarta, dama yasan zata fiton dole, had'e girar sama da k'asa tayi, murmushi yayi yace "haba gimbiyata mi'a na huskar shanu, sakin ran mana".
Harara ta balla mai " haba Jauro missa zaka yimin haka? kasan shi waye gareni?"
"To meye shidin bayan masoyinki".
Dariyar takaici tayi dama hakan ya zamo gaskiya da taji dad'i " haka ar tunanin ka dama? Mizaiyi dani 'yar k'auye? Kabar wanga tunani ma, iyaka dashi mutunci sai kara2 da yake koyamin".
Haka dai ya tafi bawai dan ya yarda ba, sai dai baison ranta ya b'aci, shiyasa ya yadda ya tafi, tare da shan zasu had'u wata rana.
**************************
Zaune Suke kamar kullum bakin rafi ga littafi da Biro gefensu dan yanzu har sun fara koyon, sai kuma k'awa'idi da ka'ida na musulunci, dan har nan Suke tab'awa, bayan ya gama koyamatasu, ta maimaita sannan yace.
"Gud gul, yanzu sai mu koma karatunmu na wancen satin ina fatar kin hadda CE".
"Eh mana, Bari ma kaji" ta fad'a tare da mik'a mishi littafin, tiryen-tiryen ta kawo su ba gyara.
Jinjina yayi mata da hannun tare da tafa mata, yana jinjina saurin ganewa irin nata, da an gayamata abu ta haddace irin su ne gifted by nature, amma anaso a kashe mata dama ga banza.
"Aboki my glass?"
Saida yayi dariya saboda sunan da take kiransa dashi "um Ramlah luv, ya akayi".
" kacce love na nuhin soyayya ko?"
Cikin mamaki yace "eh meya faru?"
"To naji kana kemin Ramlah luv, yana nufin Ramlah soyayya kenan, ma'anar sunana soyayya kenan?"
Saida yayi Jim yama rasa me zaice mata gashi ta kifeshi da ido "Aa nadai had'a sunan naki da Kalmar soyayya, kinga kenan ke soyayyar kowa ce saboda kinada ganewa sosai" ya k'arashe tare da yi mata alaman wasa, saboda ta shanshance da zancen.
Aiko dariya tahau nan sukaci gaba da karatunsu cikin nishadi(kara2 yafi jiga idan ana had'awa da wasa)lol.
"Kan ubancen yau za'ayi kazar uban nan niya" sukaji an fad'a daga sama, a tare suka juya dan ganin wane hatsabibin ne.
Kallon wannan fa Abdool ya bishi dashi, Jauro kuwa sandar da ke wuyansa ya d'aga da niyyan kai mishi bugu.
Da hannu d'aya Abdool ya rik'eta tamau yadda ko motsata Jauro bazai iya yi ba, yanzu kam da kallon kama renani yake binsa, Laure ce ta mik'e a fusace cikin fulatanci take magana.
"Haba Jauro Wanga wace irin haukata? Na hidi maka mia tsakanina dashi, wai shin imma masoyina ne, mi zakayi? Hala an baka nina?"
Ba tare daya bata ansa ba, ya dawo da kallon sa ga Abdool.
Cikin muryan 'yan tasha, yana juye baki yake magana "Hai kad'o ina gargad'inka, daga hita hanyar Laure, da duk Ahalin ard'o idan ba haka ba Hmmm".
"Kai kuma waye kai? Kuma meka isa kayimin" Abdool ya fad'a cikin gadara da binsa da kallon renin hankali.
"au bata hwadama ni'a wa ba, toni zan fad'a maka, nina mijinda zata Aura, nina uban d'iyanta, kuma kiyayi had'uwarmu ta gaba" yana gama fad'i yaja sandarsa ya kama gabansa.
Abdool dake tsaye kamar Wanda aka dasa, haka yaji zancen kamar saukar aradu, cikin jarumta da dakewa ya tattaro sauran k'arfin halinsa, ya maida kallonsa ga Laure dake tsaye tana hawaye.
Idan ka kallesa zaka tsinkayo kishi da bacin rai kwance a fuskarsa, amma da yake akwai k'arancin shekaru gareta bata fahimci komai ba.
"Abinda ya fad'a gaske ne?" Tayi ya tambayeta, girgiza kai tayi "ba haka bane hasalima dagashi sai Iya Hari suke zancen, Baffa baice komai ba...." Nan tayi mishi bayani sosai, ya d'an samu nutsuwa amma kuma jin hali irin na Jauro yasa hankalinsa yad'an tashi, dan yana tsaoron yaje yayi mata illah, amma tunda yana sonta yasan kila ba zaiyi mata komai ba.
Shikam ko batason Laure bazaiso a aura mata wannan shashashan ba, balle kuma son nata yake, ganin hankalinta bai kwanta yasa yace suje kawai an k'are kara2.
Sallama yayi Ard'o, bayan sun dan tattauna, sannan ya gaya mishi zaije gida Hutu, fatar Alkhairi yayi mishi "don Allah in kaje ka gaidasu sosai, inji ka gayama mutuniyar taka?"
"Aa Baba".
"Ato bari tazo kuyi sallama, Ramlatuna karatu zai tsaya kenan." Ya fad'a yana murmushi tare da shigewa ciki.
Da zabi da k'wayak'wayi ta fito wai inji Baffa "aboki mai glass hala ina zakana nijji Baffa yace wai ka kai Musu?".
"Gurin Mamana zanje Ramlah luv".
"La ina Maman taka take hala?"
"Can da nisa kinsan Kaduna?"
Girgiza kai tayi cikin mamaki "dama ba Yabo an garinku ba?"
"Eh".
"To nima zan biyoka inda mamar ka".
Smiling yayi " kina son zuwa inda Mamana?"
Da sauri ta girgiza mishi kai alaman eh.
"To inshaa Allah, zanje dake, idan zan koma kinji".
" Aa nidai katahi dani yanzu" ta fad'a cikin shagwaba.
"Oh friend yaushe kika iya rigima, kiyi hak'uri kinji zanje dake next time" haka ya lallab'ata har saida ta hak'uri sannan ya tafi, bye ta ringa yi mishi har saida ya bacema ganinta sannan ta share hawayen da suka zubo mata, tabbas zatayi missing d'insa.
Tafe yake yana tuk'i amma yana tuno maganganun Jauro, "Nina mijinta, nima uban d'iyanta".
Da k'arfi ya daki sitiyari " no it can't happen ever".................
💄Meryerm Abdool💄
[7/22, 6:46 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
```Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yana cewa:-```
_Hak'ik'a Allah mad'aukakin sarki baya duba zuwa ga suffofin jikinku ko dukiyoyinku, saidai yana duba zuwa ga zukatanku da ayukanku._
*kyawu da dukiya, ba zasu taba zama guarantee na shiga aljannah, gareni, gareki, garesu ba, tsarkakakkiyar zuciya da kyawun hali, shine kad'ai zai kwacemu a gun Allah ranar gobe k'iyama, nidake dasu mu guji rud'in da sharrin kyawun halitta dana dukiya, mu tsarkake zukatanmu, muyi k'ok'ari mu gyara tsakaninmu da mahaliccinmu domin goben mu, duniya labari ce, komin dad'ewa zamu barta, Allah yasa mudace da rahamarsa👏🏽*
📝 *Episode* 61--65
A yau ne su Zainab suka kammala attachment d'insu, k'warya-k'waryar walima mai gari yasa aka had'a musu tare da taimakon likitocin asibitin, sun yaba musu tare da jinjina musu akan k'ok'arin da sukayi, tare dayi musu fatar Alkhairi.
A tare suka wuce Sokoto da Abdool, dan shima ya d'auki Hutu gobe sai wuce Kaduna, bayan ya sauketa fitowa yayi ya fito mata da kayanta dake booth, ita kuma gida ta shiga ta kira gate man da driver domin su shigo mata da kayan ciki, ta samu har ya shiga motar yana shirin tafiya, gurin k'ofar ta sunkuya cikin marairaicewa.
"Sir pls ka tsaya Ku gaisa da Momyna har nayi mata magana".
" Oh! No Zainab ki bari next time...." Katsesa tayi.
"Pls Sir kai kayi alk'awari fa" ba yanda zaiyi, haka ya fito dole, a parlour Dadynta ta saukeshi, ga kayan motsa baki an shirya kamar hauka, ciki ta shiga ta kira Mamanta, cikin girmamawa suka gaisa, yau dai taga Dr Abdulmajeed d'inda take shan labarinsa gurin Zainab, itama ta yaba sosai da yaron, godiya tayi mai da irin kulawar da yake bawa 'yarta, tare dayi musu fatar Alkhairi, shikam kunya yaji kardai Maman tasan Zainab na sonsa.
Bayan fitar haka k'anninta sukayi ta zuwa suna suna gaishesa kudi ya basu shima dak'ar suka ansa sunayi masa godiya ya yaba da tarbiyar yaran "Sir kaci wani Abu mana" ruwa kawai yasa yace zai wuce, ba taso hakan ba amma ba yanda zatayi, dan ita idan son ranta ne, su tabbata haka har abada, har mota ta rakashi.
Wani ring ta Ciro a yatsarta ta bashi "wannan d'in na meye Zainab"?
Murmushi tayi tasan yasan tana sonsa, saidai koda sonsa zaiyi ajalinta ba zata tab'a fad'a masa ba " Sir ka rik'eshi a gunka, idan ka kalla ka tuna dani, pls Sir kada manta dani".
Sosai ta bashi tausayi, ansa yayi yasa a k'aramin yatsarsa, tare dayi mata murmushi "bazan tab'a mantaki ba Zainab ki saka wannan a ranki".
Taji dad'i har k'ashinta koda ba har ransa ya fad'i zancen ba, itakam ya faranta mata, shikam yayi hakane kawai dan ya kwantar mata da hankali.
Saida ta daina hango motarsa sannan ta juya gida cikin farinciki harda tsallenta na murna (hohoho! So manya).
××××××××××××××××××××××
*Washe gari*
8:00am sukayi sallama da mutan Sokoto suka d'auki hanyar Kaduna garin gwanma, wannan k'aron Hakeem ne yaja motar sai sharara gudu yake, yayin da Abdool ya kebin k'ira'ar da ke tashi a cikin suratul Maryam, idonsa a lumshe.
12:00pm suka isa, gidansu Abdool suka sauka, sun samu Maamii ta tarbesu da tsararran girkinta ko office bata fita ba saboda d'okin dawowar Son d'inta ita Kanta tasan tayi missing d'insa sosai, su Abj ma sai murna dawowar Yaya Abdool Suke, suna nanik'e dashi suna mishi surutu, saida sukayi dam, sukayi fresh up, sannan Hakeem yayi musu sallama, da motar Abdool ya wuce gida, idan yaje ya dawo da ita.....
Hutun one month sukayi sannan sukayi shirin komawa, a wata d'ayan ba k'aramin dad'i hutun yayi ma Abdool ba duk kuwa da tunanin Ramlah na mak'ale a zuciyarsa, sukanyi waya da Zainab time to time, sai yaji inama da Ramlah ne, sai yanzu yakejin haushin rashin barma Ardo waya da baiyi ba, Aida sun rik'a gaisawa da sahibarsa.
Saura kwana uku su koma suna zaune da Maamii suna hira dan a duniya bashida abokiyar hira da shawara kamar ita, har suka gangaro kan hirar Ramlah.
Laure dake gefe tunda ya shigo gidan batace uffan ba, hasalima ko inda yake bata kalla ba saboda tsabar takaici, yanzu idan ba rashin tunani ba taya za'ace gardi kamar Jauro ya ringa shigowa mutane gida kamar gidansu, siririn tsaki taja, Wanda yayi dai-dai da maganar Iya Hari.
"To isasshiya, tsigaggga, sai kitahi ki bashi hak'uri, ke wani lahe kamar d'iyar arziki, shegiya me bak'ar aniya."
Itakam bataga dalilin bashi hak'uri ba, koda kuwa an bada ita gareshi balle ba'a bayar ba...."kin tashi kin tafi kosai nayi mid'imid'i dake anan niya" iya Hari ta katse mata tunani aiko tana shirin d'aukar muciya, aiko a guje tayi soro gidan ba shiri.
Yana tsaye yana jiran fitowarta, dama yasan zata fiton dole, had'e girar sama da k'asa tayi, murmushi yayi yace "haba gimbiyata mi'a na huskar shanu, sakin ran mana".
Harara ta balla mai " haba Jauro missa zaka yimin haka? kasan shi waye gareni?"
"To meye shidin bayan masoyinki".
Dariyar takaici tayi dama hakan ya zamo gaskiya da taji dad'i " haka ar tunanin ka dama? Mizaiyi dani 'yar k'auye? Kabar wanga tunani ma, iyaka dashi mutunci sai kara2 da yake koyamin".
Haka dai ya tafi bawai dan ya yarda ba, sai dai baison ranta ya b'aci, shiyasa ya yadda ya tafi, tare da shan zasu had'u wata rana.
**************************
Zaune Suke kamar kullum bakin rafi ga littafi da Biro gefensu dan yanzu har sun fara koyon, sai kuma k'awa'idi da ka'ida na musulunci, dan har nan Suke tab'awa, bayan ya gama koyamatasu, ta maimaita sannan yace.
"Gud gul, yanzu sai mu koma karatunmu na wancen satin ina fatar kin hadda CE".
"Eh mana, Bari ma kaji" ta fad'a tare da mik'a mishi littafin, tiryen-tiryen ta kawo su ba gyara.
Jinjina yayi mata da hannun tare da tafa mata, yana jinjina saurin ganewa irin nata, da an gayamata abu ta haddace irin su ne gifted by nature, amma anaso a kashe mata dama ga banza.
"Aboki my glass?"
Saida yayi dariya saboda sunan da take kiransa dashi "um Ramlah luv, ya akayi".
" kacce love na nuhin soyayya ko?"
Cikin mamaki yace "eh meya faru?"
"To naji kana kemin Ramlah luv, yana nufin Ramlah soyayya kenan, ma'anar sunana soyayya kenan?"
Saida yayi Jim yama rasa me zaice mata gashi ta kifeshi da ido "Aa nadai had'a sunan naki da Kalmar soyayya, kinga kenan ke soyayyar kowa ce saboda kinada ganewa sosai" ya k'arashe tare da yi mata alaman wasa, saboda ta shanshance da zancen.
Aiko dariya tahau nan sukaci gaba da karatunsu cikin nishadi(kara2 yafi jiga idan ana had'awa da wasa)lol.
"Kan ubancen yau za'ayi kazar uban nan niya" sukaji an fad'a daga sama, a tare suka juya dan ganin wane hatsabibin ne.
Kallon wannan fa Abdool ya bishi dashi, Jauro kuwa sandar da ke wuyansa ya d'aga da niyyan kai mishi bugu.
Da hannu d'aya Abdool ya rik'eta tamau yadda ko motsata Jauro bazai iya yi ba, yanzu kam da kallon kama renani yake binsa, Laure ce ta mik'e a fusace cikin fulatanci take magana.
"Haba Jauro Wanga wace irin haukata? Na hidi maka mia tsakanina dashi, wai shin imma masoyina ne, mi zakayi? Hala an baka nina?"
Ba tare daya bata ansa ba, ya dawo da kallon sa ga Abdool.
Cikin muryan 'yan tasha, yana juye baki yake magana "Hai kad'o ina gargad'inka, daga hita hanyar Laure, da duk Ahalin ard'o idan ba haka ba Hmmm".
"Kai kuma waye kai? Kuma meka isa kayimin" Abdool ya fad'a cikin gadara da binsa da kallon renin hankali.
"au bata hwadama ni'a wa ba, toni zan fad'a maka, nina mijinda zata Aura, nina uban d'iyanta, kuma kiyayi had'uwarmu ta gaba" yana gama fad'i yaja sandarsa ya kama gabansa.
Abdool dake tsaye kamar Wanda aka dasa, haka yaji zancen kamar saukar aradu, cikin jarumta da dakewa ya tattaro sauran k'arfin halinsa, ya maida kallonsa ga Laure dake tsaye tana hawaye.
Idan ka kallesa zaka tsinkayo kishi da bacin rai kwance a fuskarsa, amma da yake akwai k'arancin shekaru gareta bata fahimci komai ba.
"Abinda ya fad'a gaske ne?" Tayi ya tambayeta, girgiza kai tayi "ba haka bane hasalima dagashi sai Iya Hari suke zancen, Baffa baice komai ba...." Nan tayi mishi bayani sosai, ya d'an samu nutsuwa amma kuma jin hali irin na Jauro yasa hankalinsa yad'an tashi, dan yana tsaoron yaje yayi mata illah, amma tunda yana sonta yasan kila ba zaiyi mata komai ba.
Shikam ko batason Laure bazaiso a aura mata wannan shashashan ba, balle kuma son nata yake, ganin hankalinta bai kwanta yasa yace suje kawai an k'are kara2.
Sallama yayi Ard'o, bayan sun dan tattauna, sannan ya gaya mishi zaije gida Hutu, fatar Alkhairi yayi mishi "don Allah in kaje ka gaidasu sosai, inji ka gayama mutuniyar taka?"
"Aa Baba".
"Ato bari tazo kuyi sallama, Ramlatuna karatu zai tsaya kenan." Ya fad'a yana murmushi tare da shigewa ciki.
Da zabi da k'wayak'wayi ta fito wai inji Baffa "aboki mai glass hala ina zakana nijji Baffa yace wai ka kai Musu?".
"Gurin Mamana zanje Ramlah luv".
"La ina Maman taka take hala?"
"Can da nisa kinsan Kaduna?"
Girgiza kai tayi cikin mamaki "dama ba Yabo an garinku ba?"
"Eh".
"To nima zan biyoka inda mamar ka".
Smiling yayi " kina son zuwa inda Mamana?"
Da sauri ta girgiza mishi kai alaman eh.
"To inshaa Allah, zanje dake, idan zan koma kinji".
" Aa nidai katahi dani yanzu" ta fad'a cikin shagwaba.
"Oh friend yaushe kika iya rigima, kiyi hak'uri kinji zanje dake next time" haka ya lallab'ata har saida ta hak'uri sannan ya tafi, bye ta ringa yi mishi har saida ya bacema ganinta sannan ta share hawayen da suka zubo mata, tabbas zatayi missing d'insa.
Tafe yake yana tuk'i amma yana tuno maganganun Jauro, "Nina mijinta, nima uban d'iyanta".
Da k'arfi ya daki sitiyari " no it can't happen ever".................
💄Meryerm Abdool💄
[7/22, 6:46 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
```Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yana cewa:-```
_Hak'ik'a Allah mad'aukakin sarki baya duba zuwa ga suffofin jikinku ko dukiyoyinku, saidai yana duba zuwa ga zukatanku da ayukanku._
*kyawu da dukiya, ba zasu taba zama guarantee na shiga aljannah, gareni, gareki, garesu ba, tsarkakakkiyar zuciya da kyawun hali, shine kad'ai zai kwacemu a gun Allah ranar gobe k'iyama, nidake dasu mu guji rud'in da sharrin kyawun halitta dana dukiya, mu tsarkake zukatanmu, muyi k'ok'ari mu gyara tsakaninmu da mahaliccinmu domin goben mu, duniya labari ce, komin dad'ewa zamu barta, Allah yasa mudace da rahamarsa👏🏽*
📝 *Episode* 61--65
A yau ne su Zainab suka kammala attachment d'insu, k'warya-k'waryar walima mai gari yasa aka had'a musu tare da taimakon likitocin asibitin, sun yaba musu tare da jinjina musu akan k'ok'arin da sukayi, tare dayi musu fatar Alkhairi.
A tare suka wuce Sokoto da Abdool, dan shima ya d'auki Hutu gobe sai wuce Kaduna, bayan ya sauketa fitowa yayi ya fito mata da kayanta dake booth, ita kuma gida ta shiga ta kira gate man da driver domin su shigo mata da kayan ciki, ta samu har ya shiga motar yana shirin tafiya, gurin k'ofar ta sunkuya cikin marairaicewa.
"Sir pls ka tsaya Ku gaisa da Momyna har nayi mata magana".
" Oh! No Zainab ki bari next time...." Katsesa tayi.
"Pls Sir kai kayi alk'awari fa" ba yanda zaiyi, haka ya fito dole, a parlour Dadynta ta saukeshi, ga kayan motsa baki an shirya kamar hauka, ciki ta shiga ta kira Mamanta, cikin girmamawa suka gaisa, yau dai taga Dr Abdulmajeed d'inda take shan labarinsa gurin Zainab, itama ta yaba sosai da yaron, godiya tayi mai da irin kulawar da yake bawa 'yarta, tare dayi musu fatar Alkhairi, shikam kunya yaji kardai Maman tasan Zainab na sonsa.
Bayan fitar haka k'anninta sukayi ta zuwa suna suna gaishesa kudi ya basu shima dak'ar suka ansa sunayi masa godiya ya yaba da tarbiyar yaran "Sir kaci wani Abu mana" ruwa kawai yasa yace zai wuce, ba taso hakan ba amma ba yanda zatayi, dan ita idan son ranta ne, su tabbata haka har abada, har mota ta rakashi.
Wani ring ta Ciro a yatsarta ta bashi "wannan d'in na meye Zainab"?
Murmushi tayi tasan yasan tana sonsa, saidai koda sonsa zaiyi ajalinta ba zata tab'a fad'a masa ba " Sir ka rik'eshi a gunka, idan ka kalla ka tuna dani, pls Sir kada manta dani".
Sosai ta bashi tausayi, ansa yayi yasa a k'aramin yatsarsa, tare dayi mata murmushi "bazan tab'a mantaki ba Zainab ki saka wannan a ranki".
Taji dad'i har k'ashinta koda ba har ransa ya fad'i zancen ba, itakam ya faranta mata, shikam yayi hakane kawai dan ya kwantar mata da hankali.
Saida ta daina hango motarsa sannan ta juya gida cikin farinciki harda tsallenta na murna (hohoho! So manya).
××××××××××××××××××××××
*Washe gari*
8:00am sukayi sallama da mutan Sokoto suka d'auki hanyar Kaduna garin gwanma, wannan k'aron Hakeem ne yaja motar sai sharara gudu yake, yayin da Abdool ya kebin k'ira'ar da ke tashi a cikin suratul Maryam, idonsa a lumshe.
12:00pm suka isa, gidansu Abdool suka sauka, sun samu Maamii ta tarbesu da tsararran girkinta ko office bata fita ba saboda d'okin dawowar Son d'inta ita Kanta tasan tayi missing d'insa sosai, su Abj ma sai murna dawowar Yaya Abdool Suke, suna nanik'e dashi suna mishi surutu, saida sukayi dam, sukayi fresh up, sannan Hakeem yayi musu sallama, da motar Abdool ya wuce gida, idan yaje ya dawo da ita.....
Hutun one month sukayi sannan sukayi shirin komawa, a wata d'ayan ba k'aramin dad'i hutun yayi ma Abdool ba duk kuwa da tunanin Ramlah na mak'ale a zuciyarsa, sukanyi waya da Zainab time to time, sai yaji inama da Ramlah ne, sai yanzu yakejin haushin rashin barma Ardo waya da baiyi ba, Aida sun rik'a gaisawa da sahibarsa.
Saura kwana uku su koma suna zaune da Maamii suna hira dan a duniya bashida abokiyar hira da shawara kamar ita, har suka gangaro kan hirar Ramlah.