← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 31 OF 53

Sashe 31

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

```Nafeesa Nuhu(Sadnaf) here is ur page for ur support, thanks much momyn Affan, Allah ya raya Affan& Ikram kan tafarkin musulunci ameen #Ana mugun tare#🤝```

*Manzon Allah S.A.W yace "idan kayi imani da Allah da ranar karshe to kasowa d'an uwanka abinda kake sowa kanka" ingantaccen hadisi ne. 👌🏻*

📝 *Episode* 176-180

Babban mall Abdool ya kaisu sukayi provision, tare da Zainab sukaje itace ke tayasu d'ibar kayan, siyayya sosai, gidan Mami suka wuce direct da ita akayi gyaran kayan tsaf, sannan ta shiga K'ara musu haske game da rayuwar boarding dayake itama ita tayi, sosai sukaji dad'in bayaninta dan sun k'aru dashi, nan ta wuni sai bayan isha suka Abdool yazo d'aukarta nan wata firar ta ballewa.

"Um kasan me ya Abdool? Nifa inaga journalist zan zama dan gaskiya akwai ni da tambaya" cewar Ramlah.

Murmushi yayi "kema kin gane da kanki kenan, aini har tsoro tambayan ki nake kada na kasa ansawa, musamman lokacin da nike d'an binni mai glass".

Dariya aka kwashe da ita har ita sannan tayi mishi hararan wasa tare da turo baki "badai zaka daina ba ko yaya?"

"Kyalesa Aunty Ramlah sai munyi maganinsa d'an binni mai glass kawai dashi, kinga rabuda shi ki koyamin filatanci kinji" Zainab ta fad'a tana k'unshe dariya.

"Kai Aunty Zee da wayo kema kin k'ara fad'a ba" Nihal ta fad'a itama dariyar ce take k'asa-k'asa.

"Ba ruwana daku gaba d'aya ai duk na harbo jirginku" mik'ewa tayi da niyyan shigewa d'akin Mami da yake ita bata parlon, da sauri Abdool ya rigo hannunta yana fad'in "haba Ramlah love Ramlatun baffa wasa muke fa."

Abu ne ya tsayama Zee a mak'ogoro dak'ar ta had'iye da addu'a tare da murmushin yake "Eh Aunty Ramlah wasa muke fa".

Kwace hannunta tayi ba tare data juyo ba " naki nayi d'in " dai2 da fitowar Mami tana dariya itama "kai kun fa dami dota da tsokana banaso fa" janta tayi zuwa seat tana Shafa mata kai, su kuma sai rike dariya suke ganin yadda ta kumburo baki wai ita a dole fushi tane, Abdool sai kallonta yake cikin K'auna shikam komai tayi burgeshi takeyi "Ahhhh ina sonki 'yar K'anwata" ya fad'a a ransa..

Zainab na ankare dashi tuni abin ya motsa (oh wannan kishin Zee anya kuwa, um barin yi shiru kada Zee team suji).

Agogo Mami ta kalla har tara ta gota "kai Ku tashi Ku tafi haka nan mungode" dariya Abdool yayi "Mami abin harda kora"? " eh dai Ku tafi dai, Ku kuma kuje Ku kwanta kunsan gobe sammako zakuyi tunda in schools days ne".

Zainab da ta matsu su tafi kada ta k'asa controlling Kanta har a fahimta inda Ramlah taje tana murmushi tare da jan kumatunta "haba Aunty Ramlah saki fuskar mana daga yaune fa" had'i dayi mata chakulkuli aiko batasan lokacin da ta saki dariya ba.

Nan sukayi musu sallama har mota su Ramlah suka rakasu, nan sukace sai sunzo gobe rakiya da yake sune zasu kaisu, saida safe sukayi kana suka koma ciki, su Husna suka kai d'aki wad'anda bacci yayi gaba dasu a parlour...

Washe gari tun da sassafe su Zainab suka zo, anyi sa'a suma sun kintsa tsaf nan suka sallami Mami, suka wuce su Husna suka fara ajewa a school sannan suka Lula *F.G.C* su Ramlah hadda hawaye sai shagwab'a take zubuwa Abdool yana biye mata, Zainab dai d'aurewa kawai take amma kam abin tsikarta kawai yake.

Dak'ar ta barsu suka wuce, cike da missing nasu, dan zamansu sun saba sosai kamar kada su tafi sukeji musammam Abdool zai nisanta da mintin zuciyarsa.

( _Asha karatu lafia 'yan makaranta_ 🤣 )

********************

Abdool ne zaune cikin office yana rubuce-rubuce, turo k'ofa akayi da sallama ya shigo, ansa sallamar yayi ba tare daya d'ago ba "kaga mijin mata biyu fa, mijin Ramlatu angon Zainabu" Hakeem ya fad'a cike da tsokana.

Malalacin smiling yayi masa "kaji dashi dai imma da gatse ka fad'a haka abin yake dai, point of correct angon Ramlah zakace don itace uwargida kuma amaryar gaban goshi".

Dariya Hakeem ya kece da ita " ahaf ai kuwa saita gaban goshi shisa naga an rangad'a mata rival, kai yaron nan ko kunya bakaji k'arami dakai sai fitina har biyu gamu ko d'aya bamu ije ba".

"Kanka akeji kuma, nidai nasan menakeyi, hmm wani abun ma sai kaji an fara kirana Dady".

" Hhhhhhh, cool man muma fa muna hanya kuma ni matata da 2 zata fara".

"Ka tsaya wasa dai harna kai Ramlah gida itama ta aje nata, oh imma ka jinkirta ai sai na baka 'yata"

Harara ya banka mai "cuti amma kai baka sona wlh, saina zauna harka bani 'yar da ba'a haifa ba ma".

Dariya ya sheke da ita "naka wasa, kadaici gaba da ruwan ido kaga"hmmmm ba zaka gane ba amma I will give u much surprise, um ni kaga yaushe tafiyarka?"

"OK till u give it!, kaga ma file d'in wurina nakeso na hahhad'a nayi submitting nasu, ina ga dai zuwa upper week zan wuce" India aka turashi course na one year.

"OK but da Zainab zaka wuce ko?"

"Umm gaskiya saidai naje naga yanayin gurin in yaso daga baya saita biyo jirgi in naga akwai damar tazo saboda tsaro" ya k'ara sa fad'a yana dariya.

"Kaifa ka gama lalacewa fa yaron nan".

" lalalalah mutum da iyalinsa ana kira masa lalata" ya fad'a yana bud'e bakin tsokana.

"Kaji d'an tsari"

A cikin satin ya kammala komai, sallama yajema su Ramlah da yake time d'in suna school, aiko yaga kukan shagwab'a wai ita zata bishi can, tayi karatun a can shiko sai biyemata yake tabbas zaiyi missing nata sosai ya sani, Zainab ta tausaya musu dan tasan irin son da yake mata, baya iya boyesa ko kad'an ita kuma dole taso abinda yakeso tun balle Ramlah da takeji har ranta, saidai kasan zuciyarta sai zafi yake amma kuma tana Neman tsarin Allah da wannan kishin dan bata fatan cutar da Ramlah koda da fatar bakine, dak'ar suka rabu bayan ya cikasu da provision da pocket money.

Watan 2 a India ya turowa Zainab visa ta iskoshi, saboda tsaro inji shi, amma kuma kasan Ransa Ramlah yake missing sosai dan ko ganinta kad'ai ba k'aramin nutsuwa yake saukar masa ba.

Suna wasa time 2 time a wayar Mami in kuma suna school ta hanyar malamansu duk k'arshen wata yakan turo musu kud'i duk da Mami ta hanashi amma ganin yake ai nauyinta na kansa kuma dole ya sauke, zamansu a India zamane mai cike da nuna kulawa da tsantsan soyayya, kowa tattalin dan uwansa yake musamman Zainab har tausayi take bashi Sam bata gazawa da lalurarsa kullum cikin hidimarsa take.

B'angaren su Ramlah sun maida hankali sosai akan karatu, duk abinda ya shige mata duhu zata tambaya hakan yasa ta zama zakaran gwajin dafi malamai da dalibai kowa sonta yake....

********************

Suna SS1 aka kawo wata new comer class d'in su, 'yan class sukayi ruu kowa son magana yakeyi da ita ganin ta mai kyau ga class, amma banda Ramlah da Nihal sai sha'anin gabansu sukeyi, tsab ta kalle class d'in da mutanen ciki ganin kowa na welcome nata amma banda su yasa hankali ya koma garesu, gaban seat d'insu taje tare k'are musu kallo tayi tare da sakin malalacin murmushi.

"Hi" ta fad'a Nihal tago tare da cewa "hello" Ramlah kam kallon d'aya tayi mata ta maida kanta gun text book d'inta, smiling ta k'arayi tare da mik'awa Nihal hannu.

"I'm Sadeeya M Bashir, buh u can call me Sadee M bash"

Itama hannu ta bata "I'm Aisha Yusuf Besse, Nihal by family name"

"Wow nice 2 meet u" sannan ta juya gurin Ramlah ta mik'a mata hannu tare da gayamata sunanta kamar yadda ta gayama Nihal tana murmushi.

Itama murmushi tayi mata "Ramlah Abdulrahim modibbo by name".

"wow i like ur style, may I have a seat here?"

Kallon Nihal Ramlah tayi sannan tace "why not" ta fad'a tare da nuna mata seat...

Tun daga ranar suka zama k'awaye irin sosai d'innan akayi sa'a kuma itama House d'insu aka ajeta room d'insu d'aya, nan suka koma su uku komai tare sukeyi.

Sadee irin marasa jin nannan irin bata yadda d'innan ba, classy girl ce ta sosai ga rawar kai kaman me, saidai fa itama akwai kai shiyasa zamansu yayi kyau, a class kuwa ji yake dasu suke d'aukar 1,2,3 position, zamansu da sadee sun k'ara wayewa idonsu ya bud'e sosai musamman Ramlah.

Sun koyi saka k'ananun kaya a gurin ta, haka tazo dasu trolley guda haka ta shiga basu tana koya masu yadda zasu saka, nan fa suka shiga nuna Kala ko'ina suka wuce 3stars kakeji, har Senior burgewa sukeyi.

Har Mami tasan Sadee haka iyayenta har sun kulla zumunci suma, su Abdool ma daga India suna shan labarinta.

Yanzu su Ramlah anyi mastering gurin swag haka idan suka dawo Hutu a gida ma sun daina saka atampha ko less English wears kawai, mini skirt, top, tight, pencil, body hug, bomber short iri-irensu dai.

Haka idan zasu koma Hutu zasu shiga boutique su sissiya tare da M bash suke zuwa dake itama anan Kd take, Mami dai ta zuba musu ido ganin iya gidane kawai basa fita dasu.

B'angaren su Abdool kuwa tunda suka tafi basu zo ba, dan ba damar d'agawa nan da can amma har cikin ransa yana missing gida yana missing Ramlah sosai, abun haushin ma an k'ara musu rabin shekara abun ya bata masa rai saidai ba yadda ya iya dole ya jure.

Su Ramlah an zama sun zama cikakun 'yan mata sosai musamman ita dama gata kamar kajin Agric, komai na cikar mace ya cika gareta, 8 shape d'in nan ya fito sosai, dukiyarsu ta Fulani ma sun cika barakallah, duk namiji lafiyayye ya kalleta sai yaji wani Abu a ransa........

_to friends ya kamata fa mu waiwayi Iya Hari, muji wace wainar suke toyawa 😜🤣_

💄Meryerm Abdool💄
[9/10, 4:14 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
Chapter 31 · 0% Book details