Sashe 3
Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ka kiyaye gaba" koda ya duba har ta bar gurin, murmushi kawai yayi tare da k'arawa gaba.
_so kenan hana ganin laifi_
*Pls friend kuyi hak'uri dani ina fama da matsalan wayatane shiyasa bana typing da yawa.* love u all😘
💄Meryerm Abdool💄
[7/7, 8:42 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
```Where r u? Here is ur page, Momyn sultan, Sakwara, Iya Amima, Sadnap, Sadnas, kanwata jannart, Rukie kax and d rest. ur d best among besties. 💕```
*In dedicated 2 Abdool all over d world* 💘
📝 *Episode* 21--25
Bayan sun dawo da sallar asubah a d'akin kakan nasa ya yada zango, ya iskoshi zaune kan kujera tasbaha a hannunsa yana ja, hannu ya bashi sukayi musabaha tare da yimai barka da asuba sannan ya zauna k'asa dai2 kafarsa yace.
"Ina kwana Alhaji?"
"Lafia lau Abdulmajeed ya gajia?"
"Gajia ta tafi, ya girma ya kuma hak'uri da jama'a?"
"Alhamdullilah, zuwa yaushe zaka tahi yabon?"
"Um zuwa goma nakeso na tafi, shima Hakeem tare zamu fita yaje yayi report a Uduth d'in?"
"Amma anan zai zauna ko?"
"Aa zasu bashi gida to inaga acan zai zauna"
"Ikon Allah tahiya zakuyi gabad'ai?"
"Aa ai Hakeem zai ringa zuwa yana gaida ku, ni kuma zan ringa zuwa end of week inshaa Allah."
"Tau ba damuwa, Allah ya taimaka ya baku nasara a aikinku" sannan ya k'ara da cewa.
"Kaci gaba da hak'uri Abdulmajeed, dama nasan kai mai hak'uri ne, kowane bawa da yadda Allah yake tsara mishi rayuwarsa, idan aka d'auke shi a jarrabawa akayi hak'uri sai kaga ya wuce sai labari, Allah yayi maku Albarka."
"Ameen Alhaji nagode, zan shiga daga ciki nad'an kintsa kafin lokacin yayi."
"Tau yaushe zakaje Argungu can inda kakanninka?"
"Shima idan nayi clearing abubuwa zanje."
"Tau ka shiga ciki kayi sallama da iyayenka da kakarka kaji ko?"
"Inshaa Allah" ya fad'a tare ficewa yana share hawayen da suka zubo masa Wanda ni kaina bansan dalilin zubarsu ba, (tofa kona meye? Mubi a sannu zamu fahimci na meye nan gaba).
Tsaf ya kimtsa shida aminin nasa bayan sunyi sallama da mutan gidan, uduth suka nufa saidai ya tabbatar anyi komai daya kamata ayi sannan ya wuce yabar Hakeem tare cousin nashi su Isma'il, saboda a dalilin sa ya cika garin yaso su samu asibiti d'aya saidai hakan bai samu ba.
Hakeem aminine na kwarai ga Abdool Wanda bayada kamarsa amintarsu ta samo asaline daga secondary har jami'a Wanda har takai ga iyayensu, kullum Hakeem yana lura da akwai wata b'oyayiyar damuwa tattare da Abdool yasha tambayarsa amma kullum amsar d'aya ce ba komai, ya dad'e da sanin halin Abdool na zurfin ciki Sam baya bari damuwa tayi tasiri akansa yana k'ok'arin boyeta, dole shima ya hak'ura yasan in lokacin ya Sani yayi to tabbas zai gayamasa.
Shima dai ya isa garin Yabo kuma ya samu karb'a mai kyau daga mutanen garin amma kam asibitin na buk'atar ma'aikata da kayan aiki, a dalilin haka yayi alkawarin taimaka musu iya k'arfinsa Dana aljihunsa.
_wannan kenan_
^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
Tana tafe tana tunanin irin k'iyayyar da Iya Hari da Gwaggo Lanti ke nuna mata basu tab'a sonta ba, kullum cikin zaginta suke, k'arshe k'iyayya yakai su zab'a mata jauro a matsayin masoyi.......
"Ramlatuna" ko bata juyo ba tasan duk fad'in duniya bamai kiranta da wannan sunan sai shi kad'ai, juyowa tayi da murmushi akan fuskarka yana zaune bakin gidan yana duba littafi ashmawi Sam bata lura dashi ba ta tafi duniyar tunani.
Dawowa baya tayi tare da duk'awa tace "sannu Baffa, ban kula dakai ba."
Murmushi yai mata "daga ina kike da darenga?"
"Baffa daga Dandali tallen gujjiya."
"Bana hanaki zuwa Dandali da daddare ba?"
Duk'ar da kanta tayi ba tare da tace komai ba.
"Koda yake ba laihinki naba, kiyita hank'uri Ramlah da Hari inada tabbacin wata rana zata gane batai miki adalciba, kuma da yardar Allah inaji a raina sai ke zama abin alfahari a wanga karkara."
Wani k'unshi ya d'auko bayan shi ya mik'a mata "kici wanga nasan da wuya in keci abinci"
Ansa tayi zata shiga ciki tare da cewa "nagode sosai baffa" dakatar da ita yayi tare da nuna tabarma.
"Zauna nan kici" saboda sanin halin Hari idan ta gani ba barinta taci zatayi ba.
Ba musu ta zauna tare da kwance ledar nama ne agashe da zafinsa ci take hannu baka, kallonta Ardo yakeyi cike da tausayi yana mamakin hali irin na Hari, Sam batada zuciyar imani.
Cikin k'ank'anin lokaci ta cinye, ruwa ya bata tasha sannan yace ta shiga ciki, cike ta shiga zuciyarta wasai tana mai jin k'aunar Ardo har cikin ranta.
Shima d'auke kayansa yayi tare da shigewa ciki dama ita yake jira.
*Washe gari*
Kamar yadda ta saba tashinta da ruwan sanyi yauma hakane, dasu ta tasheta tare da binta da zagin k'are dangi kamar yadda ta saba.
Haka ta tashi tayi abinda ya zame mata dole sannan tayi shirin zuwa Yabo.
Zuwa karfe 9 sukaje titi don zuwa Yabo, sun kuwa yi sa'a sun samu mota, tunda suka fara tafia sai murmushi take kallonta Delu tayi "Laure missa meki na farinciki sai murmushi kikai ked'ai."
"Ni kaina bansani ba, nadaiji yau farinciki nikeyi Wanda bansan dalilin inaji a jikina wahalata ta kusa zuwa k'arshe."
"Tau Allah ya tabbatar."
"Ameen abukkiyata."
*A garin Yabo*
Abdool ne zaune kan mota bakin asibiti kasancewar yau ba aiki da yawa patients basuda yawa yaje yayi round shine ya fito waje yana shan iska, yau tunda ya tashi gabansa ke fad'uwa baisam me yasa ba, ya kira Maminsa yaji suna lafia, haka bangarensu Alhaji suma lafia.
Jin bugun zuciyarsa ya tsananta yasa ya rik'e gurin tare da yin Addu'a.
Jin ta sassauta yasa ya d'ago kansa karaf idanunsa suka sauka kan na NATA...........
Lokaci d'aya zuciyarsa ta buga kamar ta fito.....
_wacece wannan_
🤔
*Friend kuyi hak'uri da jina shiru da kukayi hakan ya farune a dalilin rashin nepa da mukayi 2days* love u❤
💄Meryerm Abdool💄
[7/10, 1:32 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
*Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa:-*
_baya shiga aljannah wanda mak'wabcinsa bai amincewa ha'incinsa ba._
*'yar uwa koda kafiri kike mak'otaka ya zama dole ki sauke nauyin hakk'in mak'otaka daya rayata akanci, makota abune mai girma saboda fadar manzonmu.*
"Jibrilu ya kasance yana yimin wasiyya da mak'oci har saida na d'auke idan na mutu zai gajeni".
_Allah yasa mu gyara_ 👏🏽
*Point of correction*
_Abdool service sukeyi ba internship ba, fatar kun gane frnds_.
📝 *Episode* 26--30
Sanye take da kaya irin na Fulani, fuskar nan tasha d'ige-d'ge ga k'waryar nono a kanta, kyakkyawace ba laifi farace ga mai tsayi da jiki, tanada kyawun fuska ba can sosai ba, fuskarta d'auke da murmushi amma zaka fahimci tana tare da damuwa, duk cikin sakan da bai wuce 50 ba Abdool ya karance yarinyar wacce ke tare da k'awarta, amma da alama yarinyace sosai saboda fuskarta ta nuna girman jikine kawai, amma abin tambayar meyasa yake ganin kamar ya Santa?, meyasa k'irjinsa ya harba saboda ganinta?
Ganin baida wad'annan ansoshin kuma gashi zasu wuce yana bukatar nonon yasa ya kirasu.
" 'yan fulani masu nono kuzo in siya".
Laure da saukarsu kenan, jin ance 'yan fulani yasa ta kalli, gurin me kiran nasu, k'irjinta ne ya buga ba shiri ta kalli k'awarta.
"Delu kega me kiranmu ko? Diba kigani kamar ba d'an nanniya ba, duba kalar idonsa abun tsoro, jishi d'an gaye, da kayan lifitoci irin na binni, muje ko kar muje"?
Me Delu zatayi inba dariya ba, saida tayi mai isarta ganin mutuniyar an fuske yasa ta sassauta.
" wlh Laure wani lokacin shirme ke dibarki yoni mi'arruwanmu da shi, nono yace zai saye fah, bayan shi mizaiyi muna? Nidai mutahi kar yace ya hwasa".
Tana gama maganar ta Kama hanya, ganin k'awar tata ta tafi yasa tabi bayanta da sauri.
Abdool kuwa dake kallonsu duk da baiji me suke fad'a yasan akansa ne, ganin suna zuwa yasa shi d'an d'aure fuska.
Suna zuwa yace "ke me kike fad'a mata, wato kikace a kalli idona ko"?
Cikin tsoro ta girgiza kai cikin siririyar murya irin ta Fulani " niya bance komi ba akanka".
K'ara d'aure fuska yayi yace "kinsha ba banji me kika fad'a ai naji komai kikace dan haka gun 'yan sanda zan kaiki"
Wayyo zanso kuga Laure kamar ta saki fitsari kunsan bafillace da tsoron d'an sanda, ba ita kad'ai ba har Delu saida ta tsorata jin an kira 'yan sanda, tuni suka fara da sun sani da basuzo inda yake.
Abdool ganin sunyi tuk'u tuk'u dariya suka bashi amma saiya danne yace.
"Nawa ne nonon"?
"Um...em.. Na nawa kakeso"? Suka had'a baki gurin tambayarsa.
D'an yatsina fuska yayi " nawane duka"?
Kallon juna zukayi sannan Delu tace " jikka talatin"
Maimata kalmar jikka yayi "meye jinka"? Ya tambaya yana kallon Laure.
Tsuru tai masa da ido dan batasan me zatace ba, suna hakane saiga wani nurse d'an garin ya taho gurin.
" Sir dama kanason nono"?
"Sosai nake shansa Jabir".
" Ayya ai bansani sir na d'auka bakasha da kullum na kawo maka shi, ke kutafi abinku zan kawo masa yanzu".
Ai su Laure dama kamar a k'aya suke tuni suka m'ike suna shirin d'ora nononsu.
"Aa bari nasiya tunda na tsaidasu" ya fad'a tare da mika musu 1k.
Delu CE ta ansa tare da zuba mishi "gashi mun gode, sai anjima" a lokaci d'aya ta fad'a tare da Dora nononsu sukabar gurin ba tare dajin ansa ba.
Jabir ne ya anshi nonon, shikam Abdool da kallon kawai ya bisu har suka bar gurin sannan ya kalli Jabir tare da cewa.
"Bari na shiga gida nad'an huta, idan an samu patient u should let me know".
"yes sir".
Gidanda aka bashi na cikin quarters d'in asibiti ya shige, murmushi kawai yake idan ya tuna yarinyar komai nata abin burgewa a fili yace " beautiful and silly girl" can kuma yace "meke shirin faruwa danine ni *Abdulmajeed*"?
"Kai no impossible".
(Tau kai kad'ai ne dai) lol.
_so kenan hana ganin laifi_
*Pls friend kuyi hak'uri dani ina fama da matsalan wayatane shiyasa bana typing da yawa.* love u all😘
💄Meryerm Abdool💄
[7/7, 8:42 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
```Where r u? Here is ur page, Momyn sultan, Sakwara, Iya Amima, Sadnap, Sadnas, kanwata jannart, Rukie kax and d rest. ur d best among besties. 💕```
*In dedicated 2 Abdool all over d world* 💘
📝 *Episode* 21--25
Bayan sun dawo da sallar asubah a d'akin kakan nasa ya yada zango, ya iskoshi zaune kan kujera tasbaha a hannunsa yana ja, hannu ya bashi sukayi musabaha tare da yimai barka da asuba sannan ya zauna k'asa dai2 kafarsa yace.
"Ina kwana Alhaji?"
"Lafia lau Abdulmajeed ya gajia?"
"Gajia ta tafi, ya girma ya kuma hak'uri da jama'a?"
"Alhamdullilah, zuwa yaushe zaka tahi yabon?"
"Um zuwa goma nakeso na tafi, shima Hakeem tare zamu fita yaje yayi report a Uduth d'in?"
"Amma anan zai zauna ko?"
"Aa zasu bashi gida to inaga acan zai zauna"
"Ikon Allah tahiya zakuyi gabad'ai?"
"Aa ai Hakeem zai ringa zuwa yana gaida ku, ni kuma zan ringa zuwa end of week inshaa Allah."
"Tau ba damuwa, Allah ya taimaka ya baku nasara a aikinku" sannan ya k'ara da cewa.
"Kaci gaba da hak'uri Abdulmajeed, dama nasan kai mai hak'uri ne, kowane bawa da yadda Allah yake tsara mishi rayuwarsa, idan aka d'auke shi a jarrabawa akayi hak'uri sai kaga ya wuce sai labari, Allah yayi maku Albarka."
"Ameen Alhaji nagode, zan shiga daga ciki nad'an kintsa kafin lokacin yayi."
"Tau yaushe zakaje Argungu can inda kakanninka?"
"Shima idan nayi clearing abubuwa zanje."
"Tau ka shiga ciki kayi sallama da iyayenka da kakarka kaji ko?"
"Inshaa Allah" ya fad'a tare ficewa yana share hawayen da suka zubo masa Wanda ni kaina bansan dalilin zubarsu ba, (tofa kona meye? Mubi a sannu zamu fahimci na meye nan gaba).
Tsaf ya kimtsa shida aminin nasa bayan sunyi sallama da mutan gidan, uduth suka nufa saidai ya tabbatar anyi komai daya kamata ayi sannan ya wuce yabar Hakeem tare cousin nashi su Isma'il, saboda a dalilin sa ya cika garin yaso su samu asibiti d'aya saidai hakan bai samu ba.
Hakeem aminine na kwarai ga Abdool Wanda bayada kamarsa amintarsu ta samo asaline daga secondary har jami'a Wanda har takai ga iyayensu, kullum Hakeem yana lura da akwai wata b'oyayiyar damuwa tattare da Abdool yasha tambayarsa amma kullum amsar d'aya ce ba komai, ya dad'e da sanin halin Abdool na zurfin ciki Sam baya bari damuwa tayi tasiri akansa yana k'ok'arin boyeta, dole shima ya hak'ura yasan in lokacin ya Sani yayi to tabbas zai gayamasa.
Shima dai ya isa garin Yabo kuma ya samu karb'a mai kyau daga mutanen garin amma kam asibitin na buk'atar ma'aikata da kayan aiki, a dalilin haka yayi alkawarin taimaka musu iya k'arfinsa Dana aljihunsa.
_wannan kenan_
^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^
Tana tafe tana tunanin irin k'iyayyar da Iya Hari da Gwaggo Lanti ke nuna mata basu tab'a sonta ba, kullum cikin zaginta suke, k'arshe k'iyayya yakai su zab'a mata jauro a matsayin masoyi.......
"Ramlatuna" ko bata juyo ba tasan duk fad'in duniya bamai kiranta da wannan sunan sai shi kad'ai, juyowa tayi da murmushi akan fuskarka yana zaune bakin gidan yana duba littafi ashmawi Sam bata lura dashi ba ta tafi duniyar tunani.
Dawowa baya tayi tare da duk'awa tace "sannu Baffa, ban kula dakai ba."
Murmushi yai mata "daga ina kike da darenga?"
"Baffa daga Dandali tallen gujjiya."
"Bana hanaki zuwa Dandali da daddare ba?"
Duk'ar da kanta tayi ba tare da tace komai ba.
"Koda yake ba laihinki naba, kiyita hank'uri Ramlah da Hari inada tabbacin wata rana zata gane batai miki adalciba, kuma da yardar Allah inaji a raina sai ke zama abin alfahari a wanga karkara."
Wani k'unshi ya d'auko bayan shi ya mik'a mata "kici wanga nasan da wuya in keci abinci"
Ansa tayi zata shiga ciki tare da cewa "nagode sosai baffa" dakatar da ita yayi tare da nuna tabarma.
"Zauna nan kici" saboda sanin halin Hari idan ta gani ba barinta taci zatayi ba.
Ba musu ta zauna tare da kwance ledar nama ne agashe da zafinsa ci take hannu baka, kallonta Ardo yakeyi cike da tausayi yana mamakin hali irin na Hari, Sam batada zuciyar imani.
Cikin k'ank'anin lokaci ta cinye, ruwa ya bata tasha sannan yace ta shiga ciki, cike ta shiga zuciyarta wasai tana mai jin k'aunar Ardo har cikin ranta.
Shima d'auke kayansa yayi tare da shigewa ciki dama ita yake jira.
*Washe gari*
Kamar yadda ta saba tashinta da ruwan sanyi yauma hakane, dasu ta tasheta tare da binta da zagin k'are dangi kamar yadda ta saba.
Haka ta tashi tayi abinda ya zame mata dole sannan tayi shirin zuwa Yabo.
Zuwa karfe 9 sukaje titi don zuwa Yabo, sun kuwa yi sa'a sun samu mota, tunda suka fara tafia sai murmushi take kallonta Delu tayi "Laure missa meki na farinciki sai murmushi kikai ked'ai."
"Ni kaina bansani ba, nadaiji yau farinciki nikeyi Wanda bansan dalilin inaji a jikina wahalata ta kusa zuwa k'arshe."
"Tau Allah ya tabbatar."
"Ameen abukkiyata."
*A garin Yabo*
Abdool ne zaune kan mota bakin asibiti kasancewar yau ba aiki da yawa patients basuda yawa yaje yayi round shine ya fito waje yana shan iska, yau tunda ya tashi gabansa ke fad'uwa baisam me yasa ba, ya kira Maminsa yaji suna lafia, haka bangarensu Alhaji suma lafia.
Jin bugun zuciyarsa ya tsananta yasa ya rik'e gurin tare da yin Addu'a.
Jin ta sassauta yasa ya d'ago kansa karaf idanunsa suka sauka kan na NATA...........
Lokaci d'aya zuciyarsa ta buga kamar ta fito.....
_wacece wannan_
🤔
*Friend kuyi hak'uri da jina shiru da kukayi hakan ya farune a dalilin rashin nepa da mukayi 2days* love u❤
💄Meryerm Abdool💄
[7/10, 1:32 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
*Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa:-*
_baya shiga aljannah wanda mak'wabcinsa bai amincewa ha'incinsa ba._
*'yar uwa koda kafiri kike mak'otaka ya zama dole ki sauke nauyin hakk'in mak'otaka daya rayata akanci, makota abune mai girma saboda fadar manzonmu.*
"Jibrilu ya kasance yana yimin wasiyya da mak'oci har saida na d'auke idan na mutu zai gajeni".
_Allah yasa mu gyara_ 👏🏽
*Point of correction*
_Abdool service sukeyi ba internship ba, fatar kun gane frnds_.
📝 *Episode* 26--30
Sanye take da kaya irin na Fulani, fuskar nan tasha d'ige-d'ge ga k'waryar nono a kanta, kyakkyawace ba laifi farace ga mai tsayi da jiki, tanada kyawun fuska ba can sosai ba, fuskarta d'auke da murmushi amma zaka fahimci tana tare da damuwa, duk cikin sakan da bai wuce 50 ba Abdool ya karance yarinyar wacce ke tare da k'awarta, amma da alama yarinyace sosai saboda fuskarta ta nuna girman jikine kawai, amma abin tambayar meyasa yake ganin kamar ya Santa?, meyasa k'irjinsa ya harba saboda ganinta?
Ganin baida wad'annan ansoshin kuma gashi zasu wuce yana bukatar nonon yasa ya kirasu.
" 'yan fulani masu nono kuzo in siya".
Laure da saukarsu kenan, jin ance 'yan fulani yasa ta kalli, gurin me kiran nasu, k'irjinta ne ya buga ba shiri ta kalli k'awarta.
"Delu kega me kiranmu ko? Diba kigani kamar ba d'an nanniya ba, duba kalar idonsa abun tsoro, jishi d'an gaye, da kayan lifitoci irin na binni, muje ko kar muje"?
Me Delu zatayi inba dariya ba, saida tayi mai isarta ganin mutuniyar an fuske yasa ta sassauta.
" wlh Laure wani lokacin shirme ke dibarki yoni mi'arruwanmu da shi, nono yace zai saye fah, bayan shi mizaiyi muna? Nidai mutahi kar yace ya hwasa".
Tana gama maganar ta Kama hanya, ganin k'awar tata ta tafi yasa tabi bayanta da sauri.
Abdool kuwa dake kallonsu duk da baiji me suke fad'a yasan akansa ne, ganin suna zuwa yasa shi d'an d'aure fuska.
Suna zuwa yace "ke me kike fad'a mata, wato kikace a kalli idona ko"?
Cikin tsoro ta girgiza kai cikin siririyar murya irin ta Fulani " niya bance komi ba akanka".
K'ara d'aure fuska yayi yace "kinsha ba banji me kika fad'a ai naji komai kikace dan haka gun 'yan sanda zan kaiki"
Wayyo zanso kuga Laure kamar ta saki fitsari kunsan bafillace da tsoron d'an sanda, ba ita kad'ai ba har Delu saida ta tsorata jin an kira 'yan sanda, tuni suka fara da sun sani da basuzo inda yake.
Abdool ganin sunyi tuk'u tuk'u dariya suka bashi amma saiya danne yace.
"Nawa ne nonon"?
"Um...em.. Na nawa kakeso"? Suka had'a baki gurin tambayarsa.
D'an yatsina fuska yayi " nawane duka"?
Kallon juna zukayi sannan Delu tace " jikka talatin"
Maimata kalmar jikka yayi "meye jinka"? Ya tambaya yana kallon Laure.
Tsuru tai masa da ido dan batasan me zatace ba, suna hakane saiga wani nurse d'an garin ya taho gurin.
" Sir dama kanason nono"?
"Sosai nake shansa Jabir".
" Ayya ai bansani sir na d'auka bakasha da kullum na kawo maka shi, ke kutafi abinku zan kawo masa yanzu".
Ai su Laure dama kamar a k'aya suke tuni suka m'ike suna shirin d'ora nononsu.
"Aa bari nasiya tunda na tsaidasu" ya fad'a tare da mika musu 1k.
Delu CE ta ansa tare da zuba mishi "gashi mun gode, sai anjima" a lokaci d'aya ta fad'a tare da Dora nononsu sukabar gurin ba tare dajin ansa ba.
Jabir ne ya anshi nonon, shikam Abdool da kallon kawai ya bisu har suka bar gurin sannan ya kalli Jabir tare da cewa.
"Bari na shiga gida nad'an huta, idan an samu patient u should let me know".
"yes sir".
Gidanda aka bashi na cikin quarters d'in asibiti ya shige, murmushi kawai yake idan ya tuna yarinyar komai nata abin burgewa a fili yace " beautiful and silly girl" can kuma yace "meke shirin faruwa danine ni *Abdulmajeed*"?
"Kai no impossible".
(Tau kai kad'ai ne dai) lol.