← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 53

Sashe 32

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

```Allah mad'aukakin sarki tsarkakakke ne kuma baya karb'a sai Abu tsarkakakke👌🏻```

Muyi k'ok'ari mu tsarkake tsakaninmu dashi.👌🏻

*Namecy ur a d most grateful ever meet ur d best namecy, ur ur ur hmmm am speechless dear, may Allah bless be wit u always namecy _Maryam Y Zango_ here is ur page.💋💋💋*

📝 *Episode* 181--185

Iya Hari tun ranar da aka d'aura ma Ramlah Aure aka kuma ga 'yan uwanta tasan lallai Ramlah tayi mata nisa, kuma tayi mata fintinkau saidai tsinka, musamman ganin irin dukiyarda ke garesu, amma saboda bak'ar zuciya irin tata da sharrin shed'an(Allah yayi mana tsari da kaidinsa) suka had'u suka yi mata b'akar hud'uba na yadda zatayi ta maida Ramlah baya taya zata maida ita k'auye taci gaba da musguna mata.

Duk masifa da bala'in Hari da d'ibar albarka irin tata bata zuwa gurin boka ko malamin tsibbu saidai tayi addabeka ka gwammace inama baka Santa ba a rayuwa, amma a yanzu ta fara tunanin zuwa inda boka domin ya lalata auren Ramlah sannan ya saka mata bak'in jini a idon dangin mahaifiyar tata su korota inda take daga nan taci gaba da musguna mata bayan tasa an rufe bakin Ard'o, wannan kullum shine tunanin amma ina zata samu kudin zuwa shine matsalar dan kudi sam baya zama ga Hari saboda shegen kwalama da kwad'ayin tsiya, ga Ard'o yanzu zama k'ankamo injita, dama can halinsa ne (Inji fa).

Tunda aka wuce da Ramlah Ard'o bai k'ara maganarta a gidan ba, ko tanaso ta tambaya ba dama duk zuwanda yake Kaduna da zuwan da Abdool keyi gurinsa bai taba gayamata, saidai taga kayan tsaraba kawai ko tambaya tayi ina, cewa kawai yake ba damuwarta bace.

Ganin zaman kad'aici ya isheta ita kad'ai a gida yasa ta d'auko Hinde d'iyar Lanti dan tayata zama da taimaka mata, amma kuma sai hakan bata samu dan Hinde gantalliyar yarinya ce, b'atacciya kuma 'yar iska irin ta k'auye nan.lol

Inta kwanta bacci sai hantsi ya dubi ludayi take tashi, ko tsince bata kawar mata hasalima ko Inda ta kwanta bata gyarawa da kuma ta samu abin kari ta fita bata gidan biki bata na suna bata dakin saurayi bata matattarar 'yan iska ba ita zata dawo ba sai bayan isha, shima tana zuwa taci abinta sai dandali daga ta dawo sai bacci, aikin sisi bata mata kuma datayi mata kallon banza ko fad'a rashin kunya take mata inta zageta ta rama, inta doketa kota hanata abinci taje ta gayama uwarta, haka Lanti ke kwaso jiki wai akan me zata dokar mata 'ya kota hanata abinci ko tana nufin yadda tayi Laure ne zatayi ma 'yarta, wallah bata yadda ba dan ba jaka ta haifar mata ba, haka zata tasata gaba da masifa akan 'yarta kuma ba halin kwab'arta dan tarbiyarta ai(kaikayi koma kan mashekiya) wani sa'in Ard'o na jinsu bai cewa k'ala, saidai yayi murmushi kawai yasan farawane ma indai alhaki ne.

Haka Hinde ta zamewa Hari wani bala'i kadangaren bakin tulu a kar ka akai tulu a barka ka bata ruwa, gefe d'aya kuma Jauro ruwa a jallo yake Neman Hari, dan Ard'o ya masa kashedi da gidansa shiyasa bai sameta a can ba, amma yasa alwashin idonsa idonta ba'a mai kyau.

( _Sorry Iya Hari, farawa ne ma_ )..😏😂

******************

Komai aka masa rana tau za'a cimmata a yaune Dr Abdulmajid tare da Zainab suka diro Nigeria cike da nasarori ciki hadda tsulelen cikinsu d'an 8months, sunyi fresh abinsu musamman Dr Majeed idan ka kallesa saika k'ara kaman wani saurayi d'an 20 ya hade cikin suit ash, yasha cover ga glass as usual ya zauna daram, sumar sai sheki take, man pride nasa yasha gyara, Zainab kuwa cikin Arabian gown ja tayi rolling da gyalenta ga cikinta daya fito tutsu dashi, tad'anyi jiki irin na cikin nan.

Sale driver ne yazo d'aukar su, direct gidan Mami suka wuce wacce ta shirya musu better tana jiran isowarsu, tayi murna da ganin su musamman ganin Zainab da ciki cikin ranta fad'a tace "Ashe gwanda da akayi auren nan gashi har rabo ya samu zanga jikana" sai nan da nan take da Zainab ina zan saka ina zan d'auke, itakam sai sunne kai take alaman kunya, Abdool kam sai murmushi yake gaskiya no place like home.

Yanzu babban burinsa ganin Ramlah yasan ta k'ara girma yanzu, anyi sa'a kuwa end of week ne visiting, surprise yakeso ya musu....

Ranar visiting su Ramlah ne zaune kan bench su 3 sai fira suke sama-sama, lokaci zuwa lokaci zata kalli gate, duk da tarasa dalilin hakan, sai smiling take tana felling special.

Can ta hango su Husna d'auke da basket, zame jiki tayi sallat ba tare dasu Nihal sun sani ba sunyi nisa da hiran Uncle lukman wani Cooper da aka kawo musu dake bala'in son Ramlah, itakam Sam bata bashi fuska ba, dan tasan ba kyau ko a musulunci and then yanzu tasan ma'anar so kuma mutum d'aya takewa so shi kad'ai yayanta mijinta, shine fa Sadee ta d'age wai tasoshi ya had'u...

"Husna, Abj ina Mamin ne" ta fad'a tana isowa gunsu, ita Sam bata kula dasu Dr Majeed ba, inama zatayi tunanin ganinsu tunda tasan basa k'asar kuma ko jia sunyi waya.

Rungume hannayensa a k'irji yayi, tabbas girman d'an mutum ba wahala, ta canja gaba d'aya, badan yayi mata Sanin kwarai ba ai kila bazai ganeta ba.

"Aa ya ina magana kunmin shiru kodai Ku kad'ai ne?" Smiling Husna tayi tare da nuna mata inda su Abdool suke.

Idonta ne ya sauka kan na Abdool dake mata murmushi, cikin ihu ta daka tsalle "Lah Yaya what bunch of surprise" ta fad'a tare da fad'awa jikinsa, wani shock ne ya ziyarcesa tun daga yatsar kafa zuwa brain d'in sa.

Wani bak'on lamari wanda bai saba ji game da Ramlah shine ya ziyarcesa a yau, duk kuwa ba yau ne lokaci na farko da ta saba rungumesa ba, cikin wayau ya zameta daga jikinsa, Zainab na ankare da halin da ya shiga saurin d'auke kanta tayi zuciyarta sai harbawa take, ba abinda take ambato sai "innalillahi wa'inna ilairajiun" sannan ta samu nutsuwa, murmushi ta k'irk'iro "wato Aunty Ramlah Dr kawai kika gani".

" laa Aunty Zee ba haka bane ai kune kunyi min bazata Allah " ta fad'a tana isa gunta, rungume juna sukayi suna dariya.

"Um um" Abdool yace, inda yake suka kalla, tuni Zainab ta gane yaren wato ayi masa a hankali da baby, hararan wasa ta jefa masa, Ramlah tace "wani abun ne yaya?"

"Um ba komai Ramlatun Yaya, ina su Nihal ne?" Ka gansu can, basu ma San nazo ba" nuna musu gun bench d'in tayi, can suka nufa a tare sai tambayan su take game da India (kunsan dai Ramlatun baffa da tambaya).

"Kinaji ko besty ni banga illar uncle Luku ba kawai ki amince masa" Sadee ta fad'a saidai me ba Ramlah da takema magana a gun.

Baza ido sukai suna nemanta can ta hangota tafe tare da wasu da bata sani ba sai su Husna "la haula Yaya Abdool ne da Aunty Zee yaushe suka dawo bamu sani ba" Nihal ta mik'e tana fad'a.

"Nihal wai wannan shine ya Abdool d'in?"
"Eh wlh shine kinga matarsa Aunty Zainab"

"Kai Amma wlh ya had'u ba k'arya gashi Dr, wow gaskiya I love him"

Zaro ido Nihal tayi "me? Rufamin asiri kafa matarsa can" to meye ba sai naje ata biyu ba"

"To ai.." Shiru tayi.

"To ai me?"

"Uhmm share kawai Sadee" zata yi wata magana suka k'ara so hakan ya tilasta yin shiru.

Anan suka shimfid'a darduma, lunch sukayi as usual bayan an gaisa sun gabatar musu da Sadee, firan Yaushe rabo suka shigayi da Aunty Zainab ta yaushe rabo, jefi-jefi Abdool ke saka bakinsa, duk hankalinsa ya tattara ya tafi ga Ramlah sai kallon ta yake in style, mamakin girmata kawai yake, Zainab na ankare dashi, dama tasan za'a rina tun tana kwaila ya kalla balle kuma yanzu data cika fam, Sadee ma ta kula da kallon ta dai share ne kawai.....

**************

Sokoto sukaje suka kai musu tsarabansu, har gidan Alhaji Sada sunje, momyn zee tayi murnar ganin hankali kwance harda albarkar aure.

Sunje Kilgore inda Ard'o shima yayi murnar ganin su, daga nan suka wuce Argungu, nan fa Mama ta shiga tsokanar Zainab wai daga zuwa India sai dawowa da babbar tsaraba ita dai sai sunne kai take kunya, Abdool ne mai shige mata.

*2 weeks later...*

Wayarsa ce tayi k'ara my Zee ya bayyana a screen, da sauri ya d'aga "yadai Zee ko jikin ne?"

Cikin walahalalliyar murya ta ansa "Dr kazo gida banda lafia".

" u see saida da na gaya miki bazan fita ba labour kika saboda naga syn nata kikace lafia qlau kike, koma dai ba shine ganinan in d next 2mnt" saida ya gayama wani Dr abokinsa sannan ya d'aukota dan shi duk b'angarensa ne, bazai iya k'arbar haihuwarta ba, balle yanda yaga tayi wujiga-wujiga da ita, Mami ya kira tuni ta dira a asibitin.

Suna nan Zaune tun abin safe har har rana ana Abu d'aya, sai fitowa nurse keyi suna cewa ta kusa dai, yanaso yaje saidai zuciyarsa ta gama tsinkewa, ya tausaya mata sosai irin doguwar nak'udar nan ce, ganin tasha wahala tayi har k'arfinta ya k'are, yasa suka yanke hukuncin yi mata C/S.

"Dr ka yafemin bana tunanin tashi daga gadon nan, don Allah ka yafemin duka laifuka na" ta fad'a da muryan rad'a Wanda shi kad'ai yaji dan yakai kunnensa dai dai bakinta, cikin wahala take maganar, kama hannun Mami tayi amma ta kasa magana sai bakinta dake motsi.

Mami sarkin tausayi har da hawaye ganin yadda surukar tata ta koma "Aa Zainab bakiyimin komai ba, Allah ya fito dake lafia, Allah ya saukeki lafia" daganan aka shiga da ita
Operation room.

One hour...

Jariri ne kato kaman ka lashe don kyau aka fito dashi, an shirya shi tsaf cikin Round up Red, cikin murmushi Mami ta amshi babyn tare da cewa "Mashaa Allah, barakallah".

Dr kam tambayan uwan kawai yake kota kan babyn baibi ba, kasha nurse tayi dakai " sorry sir...." What "ya katseta tare da tafiya luu k'asa a some.

_😭🙆🏾 Zee bazan iya ci gaba ba_

💄Meryerm Abdool💄
[9/12, 4:05 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
Chapter 32 · 0% Book details