← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 53

Sashe 6

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zata k'ara magana sai gashi ya fito da kallo ya bita Wanda yake na raini, yawu ta had'iye, gefen Laure ya kalla ta rabe Kanta cikin cinyar ta, girgiza kai yayi alaman tausayi.

Shatu dariyace ta k'onota saidai ba damar yi ganin yadda uwarta ke raba ido alaman tsoro, dan Hari akwai masifa amma tsoro kamar farar kura, haka take tsoron Jauro kamar ranta.

"Dofto ya ake ciki"?Malam Garba ya tambayesa.

" zaku iya tafiya sai a kiyaye b'ata masa rai, sannan a ringa kula da shan maganin pls Ku kiyaye".

"Inshaa Allahu dakata" Iya Hari ta fad'a don Neman sulhu.

"Madallah dofto za'a kiyaye inshaa Allah, mungode da hidima fa, takardar magani fa? Wanda za'a siya".

" no ku barshi kawai na kai masa maganin, adai kula sosai".

"Kai madallah mun gode sosai Allah yayi Albarka, Bari intai in samo mota, Ku kutai ku kimtsa" yace dasu Shatu.

"Ameen, amma indai wannan Ku had'a kayanku zan kaiku, sai kumin magana idan kun shirya" ya fad'a tare da wucewa.

Da Zainab ya had'u yana daf da shiga office "morning Sir".

" morning Zainab, am kiyima Dr bakori magana yayi replaced d'ina zan fitane".

"OK Sir".

" koda maganan?" ganin ta mishi tsaye ta kashesa da ido.

"No" ta fad'a tare da wucewa, girgiza kai yayi tare da smiling ya Shafa sumarsa "ciwon mu iri d'aya ne, son maso wani" ya fad'a tare da shigewa office d'insa..........

Har k'ofar gida ya kaisu, wannan karon harda su Iya Hari sai godiya ake zubawa (su iya ansha A/c) lol.

Fura zallah Ardo yasa aka damo masa wacce tasha kindirmu damun kyale mod'a(ba'a saka ruwa a ciki) yaji dad'in hakan sosai dan dama Abdool ma'aboci shan furane da nono, nan waje suka zauna da Ardo suna d'an fira, yara kuwa sun zagaye mota sai shafata Suke sunga irin wacce basu saba gani ba, mata kuwa sai lek'e Suke ta Katanga, mutane sai kwararowa suke gaida Ardo da jiki.

Har ya shiga mota zai tafi sai ga Laure ta fito, nono ne da kwan zabi tace Ardo ya bata, tsayawa tayi ta k'asa magana Kanta k'asa, kallo ya k'are mata tsaf komai nata mai kyaune yanzun ma da take yarinya to inaga ta girma Hmmm.

Ganin tak'i magana ga lokaci na tafiya yasa yace "yadai da damuwa ne"?

" Um nagode sosai Allah ya saka da Alkhairi" still Kanta a k'asa itakam har yanzu tsaronsa takeyi da gaske.

"Hmm damefa"?

Bata ansa ba sai Ledar da ta Mik'a mishi " gashi ka kaima Aunty Zainab ina gaida ita sosai " duk cikin sanyayyiyar murya take maganar.

"Allah ya kiyaye" tana fad'a ta juya ba tare dataji me zaice ba, binta yayi da kallo harta shige, Shafa Kansa yayi tare da smiling harda lumshe ido (tofa me kenan Dr?)...........

Zainab taji dad'in kyautar Laure kuma ta nuna hakan a fuskarta wanda hakan ba k'aramin dad'i yayi ma Abdool ba, amma kuma k'asan ranta tanajin kishi sosai saboda zuwa yanzu ta gane itace dai 'yar fillon da yake magana, to amma meyasa ta damu da yawa batada tabbacin sonta yake ko tausayinta, dan tasan Abdool da tausayi a d'an zaman da sukayi yana d'aya daga cikin hayensa dake k'ara nutsata a k'aunarsa, amma kuma tanaji a jikin ta na Laure ya wuce tausayi to amma meye mafita saboda a gaskiya tana matuk'ar k'aunar sa tare da kishinsa (tofa Zee u say something oo).

"Sir pls idan zakaje Skk dis week zan bika ka ragen hanya"?

Saida yayi Jim sannan yace "OK".....

*End of week....*

Har k'ofar gidansu ya taho d'aukar ta, sanye ta fito cikin Arabian gown black tayi rolling da light blue d'in kashka, light make up tayi, tayi kyau ba k'arya.

Tunda ta fito ya bita da ido for d first time daya k'are mata kallo, tayi masa kyau amma kuma bata a zuciyarsa maganan gaskiya, dan ya dad'e da harbo jirginta musamman a d'an lokacin nan da take shige masa yasan sonsa takeyi, kuma har cikin ransa yana tausaya mata saboda yanzu shima yasan dafin so.

Tunda suka gaisa suka d'auki hanya bamai cewa uffan kowa da abinda yake sak'awa a ransa.

K'ira'a ya kunna musu ta *Shaik sudais* cikin suratul bak'ara, cikin kwarewa yake tuk'in yana bin karatun a hankali cikin daddad'ar muryarsa mai killing d'in Zainab, aiko lup tayi a kujera tanajin inama su couple ne, direct gidansu zasu wuce yanzu sai imagining takeyi a ranta tana murmushi( boyar Allah).

Batama san sun iso ba saida taji yana fad'in " ina muka nufa" cikin kasala tace.

"Mabera" gidane mai kyau madaidaici dan Baban ta yana da hali dai2 gwargwado, saboda ma'aikacin gwannati ne kuma ba laifi yanada salary, Zainab CE babba 'yarsa sai k'annenta 4, yana ajeta har zai ja mota tace "pls sir ka shigo Ku gaisa da Momy na".

"Oh! Sowie Zainab I'm urgent now but i promise zanzo when I'm free".

Godiya tayi masa sannan yaja motarsa zuwa family house nasu.............

*na shiga busy, ga matsalan b3, kuci gaba da hak'uri Dani* one love friends❤👍🏻

💄 Meryerm Abdool💄
[7/17, 12:08 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

*Annabi Muhammad (S.A.W) yana cewa:-*

_baya shiga aljannah mai yankewa(yana nufin mai yanke zumunci)_

*to 'yar uwa nidake dasu muyi k'ok'ari muga mun sada zumunci, musamman wanda yayi nisa, ba wai sai zumunci na jini, Aa harna musulunci saboda dukkan musulmi d'an uwan musulmi ne.*

Allah yasa mudace 👏🏽

```Double love belong 2 u, ina yinku 😍 momma (Ayshat garkuwa, neighbour(zee Yabour), indon kauye, Fashuna, swerry, Husna, ummyn yusrah, momyn ihsan, Maman khadija, Seemaluv, Rufy, ummimi, eshat asym, ummu safwan, ummi garkuwa, zarah adami, maskurah, Ayshat hanwa, shukrah, ummihaneefa. Pls wad'anda ban fad'a su tsumayeni next page love u all dearest😍😍```

📝 *Episode* 46--50

'Yan dubiya sai zuwa Suke ciki harda jauro anzo kamar mutumin kirki hadda wani duk'awa waishi a dole ladabi yake, Ardo dai kallonsa kawai yayi, yasan dai ba Wanda ya isa ya Aurar da Laure sai shi, ya barsu da shirmensu, 'yar ledar dubiya sai ciki yaje da ita ya bawa Iya Hari, dan ya k'asa ba Ardo.

Ita kuma mai kwadayi baki har kunne ta ansa tana shi masa Albarka, ita da Lanti sai rawar kai Suke, Shatu dai idone kawai nata, Laure ita harta manta dashi d'an kwana daya da basu had'u ba, data ganshi kamar ta hadi zuciya, shiko gogan naka dad'i kasheshi yaga rayuwarsa gata cikin kayan 'yan birni ji yake awa ya d'auke ta ya tafi, ba laifi shima yayi shigar arziki yau anzo dubiyar suruki cikin manyan kaya hadda hula, kamar abin arziki, saidai idonnan kam nanan kamar garwashi (chain! d'an kwaya baiyi ba, Allah ya karemu da zuri'armu Ameen).

Abdool yana isa b'angaren kakansa ya shige, yana zaune kamar kullum yana duba littafan musulunci, gaisawa sukayi cikin fara'a tare da tambayarsa yanayin aiki ya ansa da komai qlau, nan sukayi barkwancinsu da suka saba tare da tab'a hira, sannan ya shiga ciki ya gaidasu kamar kullum kakarsa fuska ba annuri suka gaisa, sannan ya dawo ya gayama Alhaji zai isa inda Hakeem dan zasuje Argungu ne.

"Madallah Hakeem yaron kirkine kullum sai yazo dubani ga dawainiya, Allah dai ya sanyama abotarku Albarka kuci gaba har abada ".

" Ameen Alhaji, ai indai Hakeem zaiyi abinda yafi haka" ya fad'a da murmushi dan yasan abokin nasa sarai akwai kirki matuk'a (shi akeso aboki na gari Allah yasa mudace).

~~~~~~~~~~~~~~~~~~

Hakeem ne kwance parlour gidansa sai bacci yake cikin kwanciyar hankali, Ac sai sanyaya sa takeyi, Abdool tsaye kansa ya kama k'ugu kamar mace yana tunanin kalar tasuwar da zai masa.

Saidai ya daddage yakai mishi bugu a baya, aiko sai gashi zaune yana Sosa bayan saboda yaji bugun sai raba ido yake kamar Wanda yayi k'arya.

Abdool kuwa dariya yake masa, dariyarce ta sanar da shi mai aikin, harara ya watsa masa "kaidai anyi mugu wallahi, mutum na baccinsa kazo ka tashesa fisabilillah".

"Kaiko idan ba wauta ba, meyasa ka kwanciya a parlour kuma k'ofa a bud'e salon a saceka ka bani aiki".

Dariya ya basa " imaging a saceni fa? Meye amfanin securitys d'in? A side ma waya kwanciyar bakai ba tun ten na shirya ina jiran ka, amma shiru kaman an aiki bawa garinsu" ya fad'a tare da K'ara da dalla mishi harara.

Siririyar dariya yayi tare kwanciya a seat hadda lumshe ido "hmm ka Bari kawai dude d things are much fa".

" Hmmm ba wani things lover boy, kadai kace love na nuk'urk'usarka period, wai ina labarin 'yar fillo taka"?

"Hmm! Wani bunch of surprise, ina last time da muke waya nace maka ina guest? Kakanta aka kawo emergency....." Nan dai ya bashi labarin duk abinda ya faru.

Hakeem hadda buga k'afa saboda dariyar k'eta "I told oo ur in love, lallai makashin maza, mazane ke kashesha, ina zanga Shukrah da Memzy alhakinsu ya fita.

" kaifa matsala dakai kenan! Ana maganan arziki kanata tsiya, ai kaima kasan ban musu walak'anci ba, an rabo lafiya wata kil ma sunyi aure, whatever dai yanzu meye way out"?

"Hmm kana sonta ka Aureta kawai".

" what! In aureta fa kace, kasan me kake fad'a kuwa?"

"Na sani mana, meye ribar soyayya idan ba aure?"

"Abinda nakeso ka gane, yarinya ce sosai inaga ko sa'ar Nihal batayi ba, sannan gata tsorona takeyi, abar maganar wannan ma ina matuk'ar tausayinta da alama tana cikin damuwa kamar yadda na gayamaka kullum cikin damuwa zaka ganta koda kuwa tana fara'a ne zaka tsinkayo damuwarta".

"Kaji Smart! Well tunda kakanta Nada saukin kai inaga ka fake da zuwa dubashi daganan sai kud'an saba, kaga kamai zaizo da sauk'i".

" wow good idea friend, hakan za'ayi".

"Hhhhhh toya maganan Zee kuma?"

"Kaji wata kuma ai ina gayamaka tare muka taho da ita nayi dropping din ta, hmm taso ta kaimi cikin gida na zille mata".

Dariya sosai yaba Hakeem yanayin yadda yayi maganan " kaji na 'yar fillo da Zainab".

"Fad'i ka k'ara ai gwandani nayi kasuwa kaifa?"

"Hhhh ba komai dai".

" amma kasan me? Ina tausayawa Zainab fa, saboda yanzu nasan rad'ad'in so".

"To ka auresu duka mana".

" caff! God forbid, bazan Iya ba".
Chapter 6 · 0% Book details