← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 53

Sashe 51

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kayi hak'uri Alhaji dole ce tasa dan Rafia tana cutar damu matuka" nan ya shiga zayyana musu yadda take shan kwayoyin rashin haihuwa har zuwa da tayi aka cire mata mahaifa da yanda take bin wasu mazaje, ba Wanda yayi mamaki a ciki dan sun san zata aikata abinda yafi wannan ma, nan dai aka shiga jajantawa kowa da San barka na rabuwa da Annoba, musamman Amaryar Rabi'u tafi kowa farinciki na rabuwa da sukayi da Rafia dan tana cin azaba a hannun ta.

"Kai kuma kaje Allah ya shiryeka" Alhaji Sada yace da gurgun".

"Alhaji na gane kuskure tuni, Allah bai bani bashi ba ya halakar duk k'azamar dukiyar da na Tara, kuma ya jarabceni da rashin k'afafu shi kad'ai ya isheni ishara" sannan ya gungura kekensa ya fice yana godiya, shiru ne ya ratsa kafin Alhaji yace.

"Tau inaso mu duka mu d'auki wannan al'amari a matsayin jarabawa daga Allah, Auwal kai kuma ina ka shige wannan tsawon lokaci ba tare daka waiwayemu ba, wannan yarinyar kuma wacce ce ita?" Alhaji sada ya fad'a, hankalin kowa anan ya dawo suna sauraron suji daga gareshi.

"Ameena sunan ta amma muna kiranta da meenal 'yata wacce taci sunan Ameena, bayan nabar nan direct Abuja na nufa bayan na share sati ina tunanin wace k'asa zan dosa dan na nisanta kaina da Ameena, daka k'arshe na yanke shawarar zuwa saudiya, zamana Saudiya bani aikin yi daya wuce zama a masallaci kullum ina can bacci kawai ke maidani gida, ganin guzurin hannuna ya d'auki hanyar k'arewa yasa na tuntub'i mak'ocina inaso zan fara Sana'a hakan kuwa akayi ya je dani kasuwa ya d'orani akan Sana'a, tun zuwana garin da malam Ikbal kad'ai nayi sabo wato wannan mak'ocin nawa, suna da matuk'ar kirki kullum zasu kawomin abincin safe rana dare basu gajia, sun jani a jiki sosai duk da ban tab'a gaya musu komai game dani ba, suna da 'ya d'aya wato Ahlam sannu a hankali sha kuwa ta shiga tsakanin mu, har takanzo ta gyaramin gida idan munje kasuwa, tana zuwa ta tayani hira a idan naje gidansu kullum taga tana ganina da foton Ameena da Abdool Dana Alhaji da Momy har dai ranar ta nuna tanason taji tarihina irin shakuwar mu tasa na k'asa b'oye mata labari na, Ahlam ta girgiza dajin labarina har da kukanta ta tausayamin, kullum bata da magana saita Abdool da Ameena irin k'aunar da take nunawa ga iyalina ne yasa na k'ara ganin kimar ta a zuciyata" nisawa yayi sannan yaci gaba.

" a haka shekaru suka ja har Ahlam ta kammala karatunta iyayenta suka bijiro mata da maganar Aure, haka Ahlam ta had'a Kai da fata tace idan bani ba ba zata auri kowa ba, tsananin k'aunar da iyayenta ke mata yasa suka amince da ta aureni d'in, bawai dan sunaso ba dan kowa yasan larabawa da nuna banbancin launin fata da tak'ama da nasaba, nidai bansan abinda ake ciki, sai kirana malam Ikbal yayi ya gayamin yadda sukayi da Ahlam, nan na gaya masa komai game dani kamar yadda na gayama Ahlam Ashe itama ta gaya musu jin banyi musu k'arya ba, yasa shima ya bada goyon baya, wannan shine silar aure na da Ahlam mutuncinta da kirkinta da kuma nuna damuwarta akan dukkanin al'amari na ne ya janyo mata k'auna ta, a haka muka zauna tsawon shekara 4 sannan Ahlam ta samu juna biyu, na bata dukkanin kulawa har lokacin haihuwar ta, ta haifo Ameena itace ta zabawa Meenal sunan Ameena, Meenal Nada shekara biyu ciwo ya kama Ahlam Wanda yayi sanadin rasuwarta, tun Ahlam na raye tayi tayi dani mu zo Nigeria, har Cikin raina inason zuwa saidai ina fargabar zuwa in samu labarin Ameena ta auri wani kuma inga inda muka rayu da Ameena amma yanzu babu ita, kullum kuna a raina musamman Abdool da bansan wace rayuwa yake ba, saidai na kasa zuwa, a haka naci gaba da renon Meenal shakuwa ce mai girma a tsakanina da ita, nina reneta da hannuna dan duk yada kamannin ta sukazo ta dawo inda suke k'i tayi ko kasuwa da ita nake zuwa muddin taje gidan kakanninta to tare dani ne"

"Har zuwa yanzu da Meenal keda shekaru sha shida bata yadda da kowa ba saini, ina yawan bata labaru game da gida hakan yasa tasan labaru game daku, kuma na koyar da ita Hausa tana jin Hausa saidai hausar tata kamar ta k'abila take don bataji ga kowa sai guna, a wannan lokacin ne gida ya dawo min a rayuwa kullum cikin mafarkin Abdool Nike yana kirana hakan ya tayar min da hankali naji dole sai na dawo gida hakan yasa naje ma su malam Ikbal da maganar tafiya ta sukace ba damuwa amma zanbar Meenal anan dan tana cire musu kewar tilon 'yarsu, ba musu nace na amince amma Meenal tayi fir tace kafarta kafata, haka suka hak'ura ba yadda suka iya amma sunce zasuzo daga baya" kallon iyayensa yayi "ina Neman gafararku iyayena akan barinku da nayi don Allah Ku yafemin"

"Mun yafeka Auwal kaima ka yafemin da abinda nayi maka kai da Ameena akan wani dalili nawa Mara asali da tushe, na gane kuskure na Alhaji dan Allah ka yafemin na tuba nabi Allah"

"Alhamdulillah nagode Allah daya ganar dake gaskiya, Allah zaki roka afuwa akan karan tsaye da kikayi akan dokarsa kin manta cewa shi yayi talaka da mai azziki ba tare daya nemi shawarar su akan kasancewarsu haka, sannan ki nemi yafiyar Ameena da Abdool akan hakkinsu da kika tauye Allah ya yafe mana baki d'aya" Ameen kowa ya amsa, kiran Meenal Alhaji yayi ya sanya mata albarka haka Hajia, nan yan uwa da iyayenta kowa ya shiga nuna mata so da gabatar da kansa a gareta.

"Alhaji ina labarin Ameena da Abdool?" Auwal ya tambaya.

Nan akayi zaman sabon labari, "Allah sarki Ameena ta, Abdool dina ya zama babban mutum harda iyali har haka, Baba ya kamata muje Kaduna a yau inaso inga Ameena da Abdulmajid" itama Hajia yanzu ba wad'anda takeson gani kamar su, haka Meenal tana cike da burin ganin takwarar ta da kuma tilon yayan nata, Alhaji cewa yayi su bari zuwa gobe sai suyi sammako suma sun d'an huta.

Da muradin ganin Ameenarsa da Abdool d'in sa, yayi farincikin jin Ameena bata da Aure yanzu kila rabon su sake zama ne.

***********

02:00pm

A garin Kaduna tayi musu, kasancewar Weekend ne, duk suna gidan Mami, k'ofar gidan suka tsaya, Hajia sai mamaki take yanzu Gidan Ameena ne nan lallai duk abinda ya baka tausayi wata rana sai ya baka tsoro, mota had'u suka ciko, waya Alhaji ya zaro tare da kiran Abdool, ring 2 ya d'aga yana fad'in "tsoho mai ran k'arfe yau soyayyar ta motsa ne" cike da zolaya.

Dariya Alhaji yayi "kamar kana kusa ko Likkita bokan turai, shiyasa ma gani k'ofar gida kazo kamin iso" dariya Abdool yayi shima.

"Banda zolaya fa Alhaji" ba zolaya fito ka gani".

"Saidai fa gani gidan Mami" ai tazo da sauk'i dan nima nan nake nufi ba dajin Ku ba"

"Naji dai ganin nan zuwa " kowa k'ofa ya zubawa ido don ganin fitowar Abdool da yake a hands free Alhaji saka wayar.

Auwal yafi kowa zakuwa son ganin gudan jinin nasa.

Fitowa yayi cikin tafiyar nan tasa ta mai nutsuwa, turus ya tsaya yana bin motocin dake gurin da kallon mamaki dan a zatonsa Alhaji kawai ne............

💄Meryerm Abdool💄
[10/23, 9:23 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Real Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

*#[email protected]*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*

```An karb'o daga Abu huraira(R.A) yace daga Manzon Allah (S.A.W) yace "duk Wanda ya yayewa wani mumini bak'in ciki daga cikin bakk'an cikin duniya, Allah zai yaye masa bak'in ciki daga bak'in cikin ranar tashin Alk'iyama, Wanda ya sawwak'awa wani anan duniya, Allah zai sawwak'a masa duniya da lahira Wanda ya rufe asirin wani Allah zai rufe asirinsa duniya da lahira, Allah yana cikin taimakon bawansa muddin bawa yana taimaka wa d'an uwansa, Wanda ya kama hanyar neman ilimi, Allah sai sawwak'a masa hanyarsa zuwa aljannah, wasu mutane ba zasu taru a wani d'aki daga cikin d'akunan Allah ba, suna karanta littafin Allah suna mai bitarsa a tsakaninsu har sai ya saukar musu da nutsuwa, rahamarsa ta lullub'esu, mala'iku sun zagaye su, Allah ya kirasu cikin mutanen da ke gurin sa.```

Allah yasa mudace.

( _Arba'una hadith, rawahul Muslim_ )

❤❤❤ *kuna raina at any cost, Fatyy Azland, Maman ussey, Abdool AAG, Sumee Homa, thanks for ur love and support*😘👌🏻👍🏻

📝 *Episode* 256--270

Bai gama mamaki ba sai ganin mutum na dosa inda yake yayi, ko da bai tab'a ganinsa a foto ba kamar da sukeyi kad'ai ta isa ta shaida masa Dadyn sa ne, bai San lokacin da murmushi ya sub'uce masa tare da fad'in "Alhamdulillah" shima Auwal murmushi yake farincikinsa bazai misaltu ba wai Abdool ne daya bari a shekara d'aya, shine ya zama complete man, abin alfahari wa kowa "mashaa Allah" shima ya fad'a, rungume juna sukayi cikin tsananin farinciki wata k'auna na ratsasu.

Da gudu Meenal ta fito itama tayi joining nasu "Abdulmajid Ahih" ta fad'a tana jin farincikin ganin tilon yayan nata da kullum take mafarkin gani, d'ago ido yayi ya kalleta tare da kallon Auwal "sister kace My Son, kada kace komai nasan ban kyauta maka ba ka gafarceni, baice komai ba sai k'ara rungume su da yayi yana jin k'aunarsu na ratsasa yau mai zai kira wannan rana mai daraja wacce ya dad'e da cire ran zuwanta.

Gyaran murya Alhaji yayi " umm likita an manta damu ko" ya fad'a yana murmushi dan shi kansa farincikin sa bazai misaltu ba, kallon yabi mutanen dasu, tun daga Haj, Kaltume, uncle Ayuba, Sani, Salisu, Rabi'u, Aunty Maryam da zuriarsu gaba d'aya hadda Ismail da amaryarsa Amal sai murmushi sukeyi suma Hajia CE kad'ai ke sunkuyar da kai cikin farinciki da kunya.

Nan aka shiga gaggaisawa sannan yace suzo su shiga ciki, Auwal yace yaje dai yayi musu iso, yace ai sanda ya gaya musu sannan ya fito.
Chapter 51 · 0% Book details