← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 53

Sashe 53

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 9 min read

"To idan ba damuwa munaso muji tarihin jarumar tamu a tak'aice, gwagwar mayar da tayi da rayuwa har zuwa yau data zama mai nasara?"

Anan ta shiga bata labarin ta a tak'aice mai cike da tausayi, koda ta kammala daga ita har mai tambayan kuka suke, handcart tasa ta share hawayen tana murmushi sannan ta mik'a wa mai tambayan tata d'aya ta goge nata itama.

Gyaran murya tayi "na dad'e banji labari mai tab'a irin wannan ba, lallai Mrs A.A kinga gwagwar mayar rayuwa, saidai kuma hak'uri da kikayi ya zame miki alkhairi, Allah ya sauya miki rayuwa ya d'aukaka ki ya maye miki gurbin duk wani rashi da kikayi, hak'ik'a labarin ki ya isa misali, ishara ga mutane, Allah ya jikin magabata yakai haske k'abarinsu ya kyautata tamu bayan tasu"

"Ameen ya Allah nagode"

"Shin ko zamu iya sanin dalilin da yasa kika zabi ki karanci aikin jarida? me yaja ra'ayinki a aikin jarida? Ko akwai Wanda ya k'arfafa maki akan haka? meye nasarar da kika samu cikin aikin? Shin kin tab'a fuskar wani k'alubale ko barazana a wannan aikin?"

"To a gaskiya tun farko ina sha'awar zama journal and inaso na wanke rad'e-rad'in da akeyi game da journalist akan suna rubutu ne kawai don 'yan siyasa wato ya basu amma basa tono gaskiya akansu suna cover na laifukansu, in fact an d'auki d'an jarida baisan me yake ba sai abinda aka saka shi, to wannan yana d'aya cikin abinda yasa na zabi harkar"

"Dukkanin 'yan uwa sun k'arfafa min kuma sunyi supporting d'ina ta ko'ina musamman mijina abin alfahari na ba abinda zance sai Allah ya saka musu da mafificin Alkhairinsa"

"A gaskiya nasarorin da na samu ba zasu k'irgu ba, mafi girma irin Addu'o'in da nake sha gun jama'a shima wani babbar nasara ce gareni, k'alubale ba'a rasa ba, don akwai time d'in da aka tare ni na d'auko yara daga school, Allah ne dai ya karemu a ranar, barazana kuma ina samu a kowacce rana, saidai na wannan bai tab'a karya min gwuiwa ko yasa naji jikina yayi sanyi ba, saima k'arfafamin da yake akan ina ba k'asa ta gudummawa kenan"

"Hakane kam, tabbas kin kawo canji Sosai a harkar jarida, kuma an samu ci gaba sosai a harkar jarida, ba abinda zamuce sai Allah ya kara dafa mana ya kuma k'ara shige mana gaba, ya kuma karemu daga sharrin mak'iya da mahassada"

"Ameen"

"Yau fa masu abune da abunsu to tambayoyi sai kin ture, ko zaki iya gama mana meye ma'anar " Mr A.A d'in nan"ta fad'a tana dariya.

"Hmmm kada ki damu zaki samu amsar kowacce tambaya taki" smiling tayi mai sauti "Mrs na belonging ga miji to A.A na nufin Abdulmajid Auwal wato Yayana mijina"

"Kai mashaa Allah, lallai Dr Abdulmajid ya taka babban matsayi a rayuwar ki, to Allah ya raya zuria ya k'ara k'auna a tsananin Ku madawwamiya"

"Sosai Yaya Abdool shine duniya, Ameen Ameen nagode"

"Ko zaki iya gaya mana matsayin Abdool a gurinki? Kamar yadda koma komai da kika mallaka yana d'auke da tambarin Abdool kamar irinsu Abdool oil&gas naki, Abdool supermarket, Abdool Islamic scholars da dai maka mantansu"

"Hhhhhh! Abdool uba ne, Abdool yayane, Abdool miji ne, Abdool k'anine, Abdool d'ane kuma inshaa Allah har jika sai nayi Abdool, so kinga kenan Abdool na nufin Ramlah, da ina damar zama Abdool kacokam to tabbas zan zama, Abdool shine rayuwar Ramlah" (nima dai nace Abdool ne rayuwar Meryerm).

"Tofa lallai Mrs A.A kin tara Abdool koma ince ke zama Abdool ko zaki bani d'aya ne?"

"Hmm idan kinada k'ari zaki iya bani, dan ko zan tara haifi yara d'ari bazan gaji da saka musu Abdool ba, inason Abdool sosai musamman *Abdulmajid* Yayana mijina, jigon rayuwa ta, abin alfahari na, farincikin rayuwa ta, Allah ya barmu tare har mutuwa" ta fad'a cikin shaukin soya year mijin nata.

"A gaskiya kin burgeni, inama kowace mace zatayi koyi dake, taso mijinta kamar yadda kikeson Dr Abdulmajid da an samu zaman lafia sosai a gidaje da ana soyayya domin Allah, Allah ya barku tare cikin Aminci"

"Ameen nagode"

"Ko zaki iya gaya mana me kikafi so a rayuwa?"

"Yayana mijina *Abdulmajid* mijin da babu kamar sa yayan da babu irinsa, mafi tausayi a cikin mutane, mai karanci da mutunci a gurin kowa mai tausayin iyayensa mai kyautata wa iyalansa, guda d'aya tak tamkar da dubu"

"Ya ilahi da fatar Dr Abdulmajid yana gaban tibinsa yana kallon wannan hirar tamu, yana kallon yadda matarsa ke Koran ta ka da yaba ka nasan ka tsuma da zantukan ta, ina fatar Allah ya raya wannan k'auna har abada"

"Ameen ya Allah"

"Munaso ki mik'a godiyarki da gaisuwar ki zuwa ga wasu mutane masu muhimmanci a gareki"

"Tofa! Hmm da farko ina mik'a godiya ta ga Allah mad'aukakin sarki, wanda ya samar dani daga babu, ya sanyoni cikin al'ummar musulmi ba tare da iyawata ba sannan zan godewa iyayena da suka zamu sune silar zuwana duniya, ina godiya ga kakana Ard'o Wanda ya reneni cikin soyayyar da k'auna, ina mik'a godiya ta ga mamata uwar goyona kuma surukata Mami tare da Dadyn mu Allah ya saka musu da alkhairi, dole na mik'a gaisuwar had'e da godiya ga gimshik'in rayuwa Yayana Mijina Dr *Abdulmajid* gaisuwa zuwa ga Aminan Arziki 'yan uwa na jinin jiki Nihal, Sadee, Amal Meenal, Aunty Zee Allah yayi mata rahama dama sauran wad'anda ban ambata ba duk ina mik'a gaisuwa, gaisuwa zuwa ga manyan gobe 'ya'yana abin alfahari Allah yayiwa rayuwa albarka"

"Kai madallah da fatar duk kunji sak'on Mrs A.A kuma kunyi farinciki"

"Daga k'arshe meye sakonki, ga masoyanki harma da mak'iyanki, meye shawarar ki zuwa garesu? A gurguje dan na fahimci idan muka barki ba gajia zakiyi ba" tace tana dariya.

Itama dariyar tayi "sak'ona zuwa ga masoyana har mak'iyana shine ina sonsu gaba d'aya, shawara ta itace ayi hak'uri da komai na rayuwa mai wucewa ne kuma duk abinda akayi hak'uri a kansa inshaa zai wuce muddin anyi hak'uri mai kyau, hak'uri bai tab'a zama cuta saidai alkhairi ayi hak'uri nothing is parmanent even our live and world so be patients, behind every success there ris many obstacles but at d end there ris way inshaa"

"Wannan haka yake dan rayuwar ki kad'ai ta isa misali gamai lura, mun gode da wannan lokaci da kika bamu muna miki fatar alkhairi a rayuwa, muna mik'a jarumin maza Wanda ya ciri tuta a mazaje angon gurin jarumar mace mai kishin k'asarta wato Dr *Abdulmajid* likita na talaka Allah ya k'ara girma"

"madallah nima ina godiya da wannan karramawar da akayi Mani, nagode sosai da Addu'a da muka sha yau sai mun k'ara had'u wa wani lokaci, nagode"

"To jama'a duka duka anan muka kawo k'arshen firarmu da fittacciyar 'yar jarida jaruma, hazik'a Mrs A.A Wanda ni Hafsat mai sharrif na gabatar fatar kunyi farinciki da wannan firar mai cike da darasin rayuwa, saduwar alkhairi......."

********""

Abdool dake zaune kan sofa cikin d'akin sa tun da aka fara firar ko motsin kirki bayayi saboda yadda bada duka Attention nasa, hakan yasa yabar yaran parlour su kalla ya keb'e kansa saboda muhimmancin da bawa firar...

"Oyoyo Maa, oyoyo Maa..." Yaran ke fad'a cikin murna ganin mahaifiyar tasu da jin dad'in firar da akayi da ita da suka gama kallo.

"Maa u done it perfect" Junior ya fad'a tare da d'aga mata yatsa, peck takai masa tare da Shafa kansa "really Son?"

"Really Maa" suka fad'a a tare, murmushi tayi tana kai musu Peck daya bayan d'aya, K'amarar 'yarta ce wacce ba zata wuce five years ba, ita kebin su Amatullah, tak'i zuwa gunta ta koma gefe ta lab'e jikin gini tana fushi, murmushi tayi dan tasan rigimar Zainab da daru kullum k'aruwa yake.

"Lalala! Wayata tab'a min Aunty Zee na waya tab'a min autana" ta fad'a tana sunkuyawa tare da janta jikinta, turo baki gaba tayi just like Ramlah "ba Aunty Amatu bace wai baca cona cu Ya Abdool kawai kike cu, cu katai kika fad'a cunancu"

"Ya ilahi Ama zata kwanto min kura ta fad'a a ranta" a fili kuwa tace "kyaleta tsokana ne kawai ai itama ban kira sunanta ba, maza ne fa kad'ai na fad'a ina kinji"?

" to aini 'yar aunty Meenal ce, satin nan ma zanje mata weekend lololo" Amatullah ta fad'a tana yiwa Zee gwalo, "ni kuma gidan Aunty Husna zanje" itama Amaturrahman ta fad'a.

"Allah Ama zan muku duka banason tsokana fa, kinga Auta na ke kad'ai nakeso sai su ya Junior bana son su Ama" gwalo ta shiga yi musu tana dariya jin ba'a sonsu kuma za'a musu duka.

"Ash!" Ta fad'a tare da sauke Zainab, "na gaji sosai, paa na ciki"?

" eh"

Da Sallama ta shiga, duka hankalinsa ya dawo Kanta yana mata murmushi bayan ya amsa sallamar, a jikin sa ta zube "I really tired my half"

"U done it so Amazing, barin miki messenge" ya fad'a yana mata tausa, cire mata higab d'in yayi tare da zuge zip d'in, sai wani lumshe ido take, yanda take jin dad'in tausar.

Murmushi keta yayi tare da canja tasha, zaro ido tayi "haba Yaya hospital zamuje fa duba patients d'in, barin yi wanka nama ware"

"Not now it Skip, letter 2morrow" ya fad'a yana ci gaba da abinda yake.

"Zamuje gidan Mami fa, duba Dady ka tuna?"

Murmushi mai sauti yayi "ke nifa su Dadyn nakeso na samar so yau ranata ce a barni na huta"

Ganin iya gaskiya yake yasa ta samo wata dubara " yawwa barin nuna maka abinda suka bani na girmamawa sai a Samar da su Dadyn ai nima am eager "

"Serious! Nuna min" ya fad'a tare da sakinta mik'ewa tayi ta gyara rigar ta sannan ta bud'e baka kamar zata d'auko abu, sai ganin yayi ta kwasa da gudu saida takai k'ofa ta tsaya tana mishi gwalo "an maka wayon manya"

Yunkurawa yayi kamar zai tashi aiko ta ida fita da sauri tana masa gwalo.

"Zan kamaki ne ya fad'a da k'arfi yadda zata jiyoshi, smiling yayi mai k'ayatarwa tare da lumshe ido " Sam bata girma, hoho Ramlatun baffa ta mai gilashi" ya fad'a yana rungume filo tare da tuno baya...........

*ALHAMDULILLAH* *ALHAMDULILLAH*
*ALHAMDULILLAH*

*dukkanin yabo da godiya su tabbata ga ubangijin da bai Haifa ba ba'a haifesa ba, Wanda ya kad'aita cikin mulkinsa da ikonsa, Wanda ya tsarkaka a sunayensa da sufofinsa, Kamar yadda ka bani ikon farawa da gama wannan littafin lafia, ya Allah ka bani ladar da ke ciki ka shafe zunubai a rubuce da zuciya, Allah kasa nayi hujja da wannan littafin kada yayi hujja dani, Allah ka bamun ikon rubuta dai2 da aikata dai2 Ameen* 👏🏽

Sai kun jini a littafina na gaba *A dalilin pre weeding pics* just keep following my fans😘💋

Taku ce dai

💄Meryerm Abdool💄
Chapter 53 · 0% Book details