← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 53

Sashe 16

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

👌🏻 *d best way 2 love is love for d sake of Allah. And tell d one u love d fact about him, show him d true faith, never tell him lies just 2 make him happy, hmm day he/she find d true u will become his biggest enemy, may Allahu (S.W.T) show us true way of life ameen👏🏽*

Small quote👌🏻

_Aunty Khaleesat Haiydar ur r so grateful, Aunty Ummi shatu wishing oll d best in ur exams👌🏻_ #heart u aunty's😘#

📝 *Episode* 111--115

Saida aka kai ruwa rana kafin Baba ya yadda da komawar Asma'u makaranta, dan yace ta dawo tayi NCE kawai, dak'yar ya amince amma da sharadin zata kare mutuncin Kanta, ranar da zata tafi da kuka suka rabu da Abdool dan lik'e mata yayi sai taje dashi, Mansur ya fita dashi sannan ta samu ta wuce kice da kewar gida da Son d'inta, dan tasan zatayi missing nashi, Hostel ta koma da zama inda ta dage da karatunta baji ba gani, tayi mamakin rashin ganin Maryam sai daga baya takeji ga k'awayensu an canja Mata school, Hajia ce tasa aka canja mata, a cewarta kada Asma'u ta lalata mata d'iya, tunda tasan muddin suna school d'aya Maryam ba fita hanyar Asma'u zatayi ba, hakanan bataso aka maida ita nursing.

B'angare guda kuwa shakuwa ce ta k'ara shiga tsakanin Asma'u da Abdulrahim kullum zaka Kansu tare yana koya mata karatu musamman yanzu data dawo hostel dama shi a hostel yake dan ba dan garin bane, tun basujin komai a ransu game da juna har takai yanzu sunajin zukatansu sunaso su zama d'aya.

( *Tofah wai waye Abdulrahim?*)

Abdulrahim dan asalin kilgori ne wadda ke k'arkashin Yabo local government dake jahar Sokoto, D'ane ga Malam Umar wadda akafi Sani da Ard'o, sarautace irin ta Fulani wato mai gari kenan, Ard'o ya zamo mai garin kilgori ne bayan rasuwar mahaifinsa wato tsohon Ard'o, yana da matar Aure d'aya Hadizatu wacce akafi sani da Iya Hari, auren zumunci ne akayi musu, Ard'o mutum ne na mutane mai sanyin hali, kowa nasane, yayin Iya Hari ta kasance masifaffiyar mace, Mara mutunci kullum cikin masifa take da bala'i, tunda Ard'o ya aureta bai taba k'arda dad'in ta ba, anadai zaune ne zaman hak'uri, bai isa ya sata tayi ba haka bai isa ya hanata ta hanu ba, amma a haka sukaci gaba da zama da yake Allah ya zuba mishi hak'uri, komai tayi kauda kai yake kamar bai gani ba, sunada 'ya'ya uku Abdulrahim ne na d'aya Wanda take kira da Modibbo saboda kasancewarsa d'an fari, sai Lantana wacce ake kira Lanti sai Aisha wacce ake kira Shatu, sam halin Aisha da Abdulrahim ba irin nata bane halin babansu suka d'auko, kai harma kamar dansu farare ne sirara dogeye, kyawawa dasu, yayin da lantana ta biyo kama da halin uwar sak.

Tun Abdulrahim yana k'arami yake sha'awar boko, mahaifinsa kuwa ganin yana sha'awa yasa ya sakashi A yabo dan lokacin ba'ayi anan garinsu ba, haka yake tafiya kullum zuwa yabo don daga k'arshe da mahaifinsa yaga wahalar zatayi yawa sai ya had'ashi da wani malami, yake zama gidansa sai Hutu yake dawowa, Wanda hakan Sam baiyima Iya Hari dad'i ba, rigima ta tada akan ba inda zaiye ya tsaya yayi kiwo in zaiyi, rokonta yayi tayi akan ta barshi, amma tak'i amincewa, dama Abdulrahim baisan dad'in ta ba Sam, dan bata janshi a jiki, wai d'an fari ne, ba wani sabo a tsakaninsu yafi sabawa da Ard'o, haka kuwa ta dage akan ba inda zaije, saida Ard'o ya nuna b'acin ran yaje ya gayama iyayenta, ganin tunda take dashi bai taba nuna Mata bacin ransa haka ba balle har aje ga kai k'ara yasa ta shiga taitayinta ta amince akan dole.

Hakan Abdulrahim yayi ta karatunsa tun daga primary har secondary duk anan Yabo yayi su, gashi kanshi naja(dama Fulani akwai kai) tunda ya fara harya k'are bai tab'a yin na 3 saidai na 1 ko 2 hakan yasa malamansu bawa Ard'o shawarar kaishi university hakan kuwa ta kasance inda yake karatun medicine, ita dai Iya Hari akan dole yake karatun badon son ranta ba, dan ita gani take lalata yara kawai boko keyi, shiyasa ta hana a saka Lanti Shatu, Abdulrahim kuwa ya goge idan ka ganshi bakace dan k'auyen bane, hakan yasa 'yan matan garin kowa sonsa take, 'yar k'anwar Iya Hari ganin kowa sonsa yasa hankalinta ya tashi, ba kunya taje ta gayama Iya Hari itafa shi takeso, dama itama sunada burin hakan itada k'anwarta na had'a su aure, nanta tabbatar mata da Abdulrahim baida matar aure sai ita, shikam Abdulrahim Sam yarinyar bata mishi ba saboda batada nutsuwa Kanta rawa yake, itakam Saude sai d'aga kai take a garin da tak'ama zata auri d'an boko.

_wannan kenan_

B'angaren Ameena kuwa ganin Asma'u ta koma makaranta, Mansur ma ya koma dake boarding school yake, gidan ba dad'i duk da Asma'u na zuwa duk k'arshen sati, yasa tayima Baba magana tanason itama ta koma makaranta bai musa mata ba, saidai yake ba zataje nursing kamar yadda ta buk'ata ba, dan ko lokacin da Auwal ya kawo mata form abinta ta cike kenan, wannan burinta ne tun suna secondary, amma dole ta hak'ura da ita dan dalilan da Baba ya gayamata na hanata zuwa wani gari kara2, ya gayamata 'yan uwansa zaginsa zasuyi suce a maimakon yayi mata Aure ya turata karuwanci, hakan yasa ta hak'ura zatayi NCE anan *Adamu Augie college of Education Argungu* da kanshi ya anso mata form ta cike inda aka bata Agric/education, nan Baba ya sakata gaba yayi mata nasiha akan taci gaba da tsare mutuncinta tayi abinda ya kaita kawai banda bin k'awaye barkatai, itama Mama tayi tata, nan Ameena ta fara zuwa school cikin nasara, ba abinda takeyi sai kara2 ba ruwanta da kowa haka zatayi shigarta ta kamala taje data gama lec, ba wani tsaye-tsaye direct gida take wucewa dama can daga gida sai makaranta, sai kuma bikin yan uwa ko barka shima akan tilas take zuwa kada ta yanke zumunci, saidai abinda ke kona mata rai data had'u da taubasanta yanzu zasu fara takanarta da kiranta bazawara ina zawarawanta, yake kawai take musu amma Kalmar ba k'aramin k'onata takeyi ba, saidai ba yadda zatayi k'addara ta riga fata, shisa sam bata cika son shiga mutane ba.

Zuwa yanzu ta kwantar da hankalinta ta maida kamarta ta kuma rungume k'addarar ta, saidai Aure ya fita ranta gaba d'aya, shiyasa duk Wanda yazo da sunan yana sonta hak'uri kawai take bashi dan bataji zatayi aure yanzu.

Lokaci zuwa lokaci takan tuna Auwal da rayuwarsu ta baya, koyana ina yanzu oho!, Abdool zuwa yanzu ya manta da Dadynsa yayinda ya d'auki Baba a matsayin Babansa, yana 1¼ ta yayesa dan komai ci yake ga kafafu har gudu yake hak'ora ne kawai bai cika ba, bata sha wahala a yayensa ba, dan wani sa'in sauya wuni baisha ba sai dare, tunda ta aka yayesa ya koma hannun Mama can yake baccinsa.

Ta dage sosai da karatunta k'awa d'aya tayi mai suna Sakina mungadi, department d'insu d'aya, tasu ce tazo d'aya shiyasa sukayi k'awance dan itama sakina ba ruwanta da sha'anin kowa abinda ya kaita kawai takeyi(a kowanne lokaci muyi k'ok'ari muyi mu'amala da mutanen kwarai, dan kuwa har lahira kana tare da abinda kakeso, kuma zama da mad'auki kanwa shika haddasa farin kai) a hostel take zaune dan a bk suke zaune da iyayenta, kullum suna tare idan ka gansu gwanin sha'awa cikin shiga ta kamala, Sakina tasan komai gane da Ameena dan har gidansu tana zuwa, tana kuma son Abdool sosai, haka rayuwa taci gaba da tafiya yau dad'i gobe sabanin haka, rayuwar duniya kenan haka ta gada, a gefe d'aya kuma Ameena naci gaba da kasuwancinta kuma duk k'arshe wata har Alhaji Sada na zuwa dubasu da hidima sosai kamar yadda yayi alkawari, su Baba ma na iya k'ok'arin su, so batada matsala a yanzu saidai wacce ba'a rasa ba.....

Suna NCE 2 wani malami na education ya basu Assignment to group discussion ne, kuma each group ten people ne, shiya rabasu da kanshi, from d different faculty, anan aka hadasu da wani Yusuf normally tasanshi saboda suna had'uwa GSE da EDU saidai magana bata tab'a had'asu ba, shine team leader nasu ita kuma assistant, shi d'an ENG/ISS, wannan Had'uwarne ta zama sanadin shakuwa tsakaninta da Yusuf, dan Yusuf social man ne, kokai waye ka zauna dashi sati yayi wuya Baku saba ba, dan akwai barkwanci gareshi burinshi bai wuce yasa mutane cikin farinciki ba, Sam shima ba ruwan sa da shashanci, kara2 kawai ya saka gaba kuma ga kwakwalwarsa tana ja ba dama, dan 3point kawai yake bugu ga G.P, hakan yasa ya saba dasu Ameena ko bayan gama assignment d'insu saiya kasance duk lokacin da basu da lectures sukan zauna suyi discussion a tsakaninsu based on their studies.

Yauma Zaune suke suna tattaunawa sai wayanta tayi k'ara, dauka tayi basuji me aka fad'a a d'ayan b'angaren, sun daiji tace.

"Subhanallah Asma'u meya sameshi?"

Still suka k'ara jin tace "tau ganinan zuwa" mik'ewa tayi a rud'e, tare da musu zataje gida, amma yanzu zata dawo, Sakina CE ta tambayeta meya faru, nan take gayamata Abdool ba lafia.

"Aa to inzo muje kawai".

Murmushi tayi Mata " kada ki damu Besty is not so worst fa, nima I will be back soon inshaa Allah " sannan ta wuce.

Duka sun tausaya mata ganin yadda ta rude har Yusuf ke tambayarta halan k'aninta ne, nan Sakina ta gayamishi a yaronta, ba k'aramin mamikine ya Kama shi ba danshi duk kallon budurwa yake mata ba Wanda zai ganta yace tanada aure hadda d'a, yace

"Amma fa bantaba tunanin matar aure bace, duk da kuwa naga tanada kamun kai".

"Hakane amma yanzu bata tare da mijin" nan dai Sakina ta bashi labarinta, sosai ya tausaya mata, hadda k'wallarsa, tare da sak'awa ransa wani tunani.

*life goes on......*
Chapter 16 · 0% Book details