Sashe 18
Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunda suka d'auki hanya, take kuka bil hakk'i da gaskiya, kuka take mai tab'a zuciyar mai sauraro, suma mutane cikin motar duk zuciyoyinsu a tsince suke, tausayin yarinyar ya lullub'e musu zuciya, shiru kake ji ba abinda ke tashi sai sautin kukanta, ba Wanda yayi yunk'urin dakatar da ita dan wani lokaci kuka rahama kana jin sauk'i a ranka, sanda tayi mai isarta, sannan ta tsagaita, hakan yasa Ard'o fara bata baki.
"Kiyi hakur'i 'yata duk da bansan ainihin abin da kikayima mahaifinki ba, yayi miki wanga hukunci, a gaskiya hukuncin yayi tsauri, saidai ki Sani su iyaye komai suka yima d'ansu to ya zama dole yayi hak'uri dasu kuma yayi musu biyayya mudin baici karo da Umarnin ubangiji ba, saboda sun riga sun gama dashi tunda suka haifesa, inaso ki rik'eni a matsayin mahaifi a gareki ni kuma nayi miki alkawarin zan zamo uba a gareki, kuma bawai ina nufin kibar iyayenki ba aa sunanan a iyayenki ba Wanda ya isa ya maye gurbinsu a gareki, kuma inaso ki d'age da Addu'a Allah ya sassauto zuciyar mahaifinki ya yafe miki kuma ya nemeki, muma zamu tayaki da Addu'a inshaa Allah".
Sosai taji dad'in maganar Ard'o, hakan yasa hankalinta yad'an kwanta, ganin tayi sa'ar suruki na gari, cikin nutsuwa ta gayamusu abinda ya faru, sun jinjina abun a ransu tare da gayamusu kuskurensu daga ita har Abdulrahim d'in, sannan kowa ya bata baki da kalamai masu dad'i, tare da gaya mata ta d'aukeshi a matsayin k'addararta domin rabon ayi auren ne yasa hakan ta faru, tare da sanya ma Auren Albarka, Abdulrahim dake jan motar shima jiki a sanyaye duk sonsa da Asma'u baiso Auren su ya kasance haka ba, amma ba yadda zasuyi dama tun ran gini tun ran zane sai fatar Allah yasan hakan shine mafi Alkhairi a garesu, Ard'o ko tuni yaji yarinyar ta kwanta masa a rai da alama zatayi hak'uri, haka dai suka doshi kilgori kowa da abinda yake sak'awa a ransa, kowa zuciyarsa ba dad'i......
***********************
Baba kuwa yana ganin sunja mota ya buga babbar rigarsa yayi cikin gida, anan ya jefar da takardar da suka bashi nan iska yayi gaba da ita, yanda ya barsu haka ya samesu suna kuka, kallonsu yayi cikin b'acin rai yace.
"Yanzu kunaga banyi muku dai2 ba ko? Baku dubi irin abin yarinyar tayi ba, ta nuna bata buk'atar mu a rayuwarta ta zabi wad'anda takeso amma Ku duk Baku gani ba, to bari kuji duk Wanda ya yadda ya kusanceta koda hanyar bani bashi, kuma ban yafema koda kuwa keda kike uwarta ne" ya fad'a cikin b'acin rai tare da nuna Inna, sannan ya buga rigarsa yayi waje.
Bai zame ko'ina ba sai gidan aminin nasa Malam Musa, dan gayama abin ya faru da Kansa kada yaji a wani gu, yayi sa'a kuwa ya samesa bayan sun gaisa ne yake bashi labarin abinda ya faru tare da bashi hak'uri.
"Kai amma Abu baiyi kyau ba, dama ko bakazo ba inada niyyan zuwa akan maganan, dama na samu Mustapha da maganan to shine yace shi gaskiya yana wacce yakeso abar zancen kawai, to shine naso inzo in fad'a maka sai kuma ban samu zuwa ba har ka taho.
Tsananin mamaki da imani ne yayi mishi yawa, yama k'asa magana lallai kowa ya daka ta mutane toya rasa turmin daka nashi, saida sukayi da mutumin nan komai lafia amma yanzu yace ba haka ba, shiya salawantar tashi 'yar akan farinciki wasu, yayin shi kuma ya bawa d'an shi abinda yakeso, nan take nadama ta rufesa lokaci na farko d'aya yi tir da (zuciya irin tasa na Ayusher).
"Alh, Abubakar bakace komi" boye damuwarsa yayi tare dayin murmushi yake Wanda yafi kuka ciwo "ba komai Alhaji Allah ya kyauta, sai anjima" ya tashi ya wuce ba tare dayace komai ba...
Gida kuma bayan fitar baba zaune saukai jugum suna jajanta wannan Abu d'aya samesu, wannan shine ga duka ka kuma tsunka jaka, Abdool Ameena takai d'aki Wanda yayi bacci sai ajiyan heart yake, sannan ta dawo inda Mama suna tattauna wad'annan ibtila'i dake bibiyarsu a d'an tsakanin, lallai Allah shike jarabtar bawansa suna fatar su zamo cikin masu cinye ta, Ameena gani take tafi kowa ganin rayuwa, Asma'un da ta rage mata mai bata shawara sa d'auke mata kewa gashi k'addara tazo ta rabasu, yanzu ma ta ina zasu samu labarin Asma'un bayan ko waya batada ita yanzu, dan daga ita sai kayan jikinta tabar gidan komai bata d'auka, gashi ta manta sunan garin dan tabbas ta fad'a Mata amma bazata iya tunawa ba, ko wacce irin rayuwa zatayi a gidan Aurenta a wannan yanayi sa taje musu zasu karb'eta kosu wulak'anta ta? Nan tayi saurin nema mata sauk'i gurin Allah, haka suka wuni gidan ba dad'i kowa sai jimami yake.
_such is life_
Baba kuwa k'asa komawa gida yayi bayan yazo gaf k'ofar gidan ya dudduba kozai ga wannan takardar amma ina bata ba labarin ta, jin yayi komai baya mishi dad'i, sai gashi hadda k'wallarsa sam baiyima Asma'u adalci ba, yafi kowa sanin biyayya irin ta 'ya'yansa amma ya rufe idonsa, lallai zuciya mugun nama CE, kowa ya biye mata zata kaishi ta baro ne, lallai kowa yahau dokin fushi k'arshen sa nadama ne (yana daga cikin karantarwar manzo S.A.W idan kana cikin fushi kada kayi magana sannan kada ka yanke hukunci cikin fushi dan k'arshen sa dana sani ne) Allah yasa mudace.
Sai dare ya samu sukunin komawa gida, shima jiki ba k'wari ya shiga, kamar yadda Inna ta saba tarbonsa haka ta tarbesa ba tare data nuna mai komai ba, kamar ba abinda ya faru, k'ara jinjina hak'uri irin na Inna yayi sau da yawa yakan tauye mata hakki shikansa ya sani amma bata taba nuna mishi damuwar, lallai mace tagari ni'imace(haka yake duniya d'an jin dad'i ce amma mafi jin dad'in ta Wanda ya dace da mace ta gari).
Haka suma su Ameena sukazo suka gaishe shi kamar yadda suka saba, zasu tashi yace su tsaya yanada magana, ayan da yayi maganan cikin taushin murya, abun har mamaki ya basu, nan dai ya labarta musu yadda sukayi da Abokin nasa, tare da nuna musu nadamarsa.
"Alhaji ka dad'e kana tauyeni sau da yawa kana maida damuwar kowa ba damuwa, damuwarka kad'ai kake dauka damuwa, kama rayuwa da fushi kana yankewa mutane cikin fushi, to yanzu gashi wagari ya waya, ka salwantar mana da yarinyar akan son ran wasu, me kayi kenan" Inna ta gayamai magana cikin nutsuwa.
"Baba shiyasa ake son bawa mutum uziri a rayuwa, lokacin da ka shigo nida Asma'u munaso muyi maka bayani amma haka rufe ido kak'i bamu dama" nan ta basu labarin abinda ya faru a lokacin da Asma'u ta kira Abdulrahim" Amma kayi hak'uri In na fad'i ba dai-dai ba".
"To kaji ma abinda ya faru ko amma saboda rashin bata uzirunka a rayuwa kak'i sauraren kowa".
Shiru baba yayi nadama na k'ara lullub'esa, duk abinda suka fada gaskiya ba karya, sai hango lokacin da Asma'u take rik'e mishi kafa takeyi amma yayi biris yak'i saurarenta, tuni tausayinta ya kamashi lallai baiyi Mata adalci ba.
Hak'uri ya basu tare da tabbacin inshaa Allah zai nemota duk inda take.
Kwana ki sun shura watanni sun wuce kullum Baba yawon Sokoto da garuruwanta saidai kuma ba'a dace ba, ganin abin yayi yawa duk ya dami Kansa yasa Mama cewa.
"Ka hak'ura da yawon nan haka idan da rabon mu gaba zaka ganta ta kawo Kanta har gida, idan kuma babu rabo zafin nema bazai kawo samu ba, hakan ya hak'ura dole tare da bibiyarta da Addu'ar fatan Alkhairi aduk inda take.
Ameena kuwa zuwa yanzu zaman gida ya gama isanta gaba d'aya saukinta ma tana teaching da Baba ya samo mata yanzu tsawon shekara biyar kenan da rabuwarsu gashi duk masu zuwa sun d'auke kafarsa, a halin yanzu ba abinda takeso irin tayi aure shine akwai kwanciyar hankalinta (dan Mace komai kamewarta, idan batada aure to mutuncinta ragaggene a idon mutane, balle kuma wad'anda suka d'auki zawarci a lasisin iskanci suka samu tunda yanzu su zawarane ba namijin da zai Aure yace yana Neman budurci, to ai ba anan gizon yake saka ba, walla d more kikayi zina kina bazawara bakida wani hukunci daya wuce a jefeki, ba riba kenan, a tunani zawarci wata damace da mace zata K'ara sanin rayuwa, ta kuma gyara halayenta, kowanne aure yanada sila a rabuwarsa saiki duba meya kashe miki aure dan gyarawa gaba, bawai ki lalace ba, Allah yasa mudace) ayuwar zawarci rayuwace mai cike sa kalubale da tashin hankali, zaman gida ya gama isarta yau idan mace takai munzali tofa da batayi Aure ba, zaman sai kasance gashi nan dai na ganin laifi ne keda iyayenki, shiyasa Ameena ta damu sosai da rashin Auren, sai ba yadda zatayi dan tasan komai lokaci ne.
Yau kamar kullum Mansur ne yaje ya d'auko Abdool daga school, da gudu ya shigo yana murna "Mami kinga Nina yi na d'aya" ya fad'a yana nuna mata result d'in da gift d'inta aka bashi.
"Iyye yaron Inna kaifa akwai rashin ji amma akwai k'ok'ari" Jan tayi zuwa jikinta tana duba idonsa "waini kam idon nan naka Abdool anya lafia ko?"
Inna dake fitowa tace "me idon yayi?"
"Kiga farin yana surkawa da pink," duba idon Inna "tabbas ya kamata kuje asibiti" shikam sai k'ok'arin nunama inna report sheet yake, ba abinda ya damesa....
Likitan ya tabbatar musu ba wata babbar matsala bace, ciwon a jininsa yake so yayi inherited ne saidai ya kamata a nema mishi medical saboda idon yayi lasting, sai yanzu Ameena ta tuna tana ganin idon Auwal suna irin hakanan sometimes, no wonder shiyasa yake amfani da glass always Ashe medical ne.
**************
Har k'ofar gida suka sauke malam Garba da k'annin Ard'o sannan suka isa gida suma.
Da kallon mamaki iya Hari ta bisu sannan tace "malam ina kuka shige tun safe, wagga kuma fa?"
"Ai dai kin kawo tabarma tukun" tabarma tasa Shatu ta kawo tare da shimfida sannan ta kawo musu ruwa.
Zama sukayi sannan Baba yace Asma'u tasha ruwa ba musu tasha, guri ya nunawa Hari da tayi musu tsaye k'erere tana musu kallon dibar arziki, tuni jikin Asma'u yayi sanyi.
"Kiyi hakur'i 'yata duk da bansan ainihin abin da kikayima mahaifinki ba, yayi miki wanga hukunci, a gaskiya hukuncin yayi tsauri, saidai ki Sani su iyaye komai suka yima d'ansu to ya zama dole yayi hak'uri dasu kuma yayi musu biyayya mudin baici karo da Umarnin ubangiji ba, saboda sun riga sun gama dashi tunda suka haifesa, inaso ki rik'eni a matsayin mahaifi a gareki ni kuma nayi miki alkawarin zan zamo uba a gareki, kuma bawai ina nufin kibar iyayenki ba aa sunanan a iyayenki ba Wanda ya isa ya maye gurbinsu a gareki, kuma inaso ki d'age da Addu'a Allah ya sassauto zuciyar mahaifinki ya yafe miki kuma ya nemeki, muma zamu tayaki da Addu'a inshaa Allah".
Sosai taji dad'in maganar Ard'o, hakan yasa hankalinta yad'an kwanta, ganin tayi sa'ar suruki na gari, cikin nutsuwa ta gayamusu abinda ya faru, sun jinjina abun a ransu tare da gayamusu kuskurensu daga ita har Abdulrahim d'in, sannan kowa ya bata baki da kalamai masu dad'i, tare da gaya mata ta d'aukeshi a matsayin k'addararta domin rabon ayi auren ne yasa hakan ta faru, tare da sanya ma Auren Albarka, Abdulrahim dake jan motar shima jiki a sanyaye duk sonsa da Asma'u baiso Auren su ya kasance haka ba, amma ba yadda zasuyi dama tun ran gini tun ran zane sai fatar Allah yasan hakan shine mafi Alkhairi a garesu, Ard'o ko tuni yaji yarinyar ta kwanta masa a rai da alama zatayi hak'uri, haka dai suka doshi kilgori kowa da abinda yake sak'awa a ransa, kowa zuciyarsa ba dad'i......
***********************
Baba kuwa yana ganin sunja mota ya buga babbar rigarsa yayi cikin gida, anan ya jefar da takardar da suka bashi nan iska yayi gaba da ita, yanda ya barsu haka ya samesu suna kuka, kallonsu yayi cikin b'acin rai yace.
"Yanzu kunaga banyi muku dai2 ba ko? Baku dubi irin abin yarinyar tayi ba, ta nuna bata buk'atar mu a rayuwarta ta zabi wad'anda takeso amma Ku duk Baku gani ba, to bari kuji duk Wanda ya yadda ya kusanceta koda hanyar bani bashi, kuma ban yafema koda kuwa keda kike uwarta ne" ya fad'a cikin b'acin rai tare da nuna Inna, sannan ya buga rigarsa yayi waje.
Bai zame ko'ina ba sai gidan aminin nasa Malam Musa, dan gayama abin ya faru da Kansa kada yaji a wani gu, yayi sa'a kuwa ya samesa bayan sun gaisa ne yake bashi labarin abinda ya faru tare da bashi hak'uri.
"Kai amma Abu baiyi kyau ba, dama ko bakazo ba inada niyyan zuwa akan maganan, dama na samu Mustapha da maganan to shine yace shi gaskiya yana wacce yakeso abar zancen kawai, to shine naso inzo in fad'a maka sai kuma ban samu zuwa ba har ka taho.
Tsananin mamaki da imani ne yayi mishi yawa, yama k'asa magana lallai kowa ya daka ta mutane toya rasa turmin daka nashi, saida sukayi da mutumin nan komai lafia amma yanzu yace ba haka ba, shiya salawantar tashi 'yar akan farinciki wasu, yayin shi kuma ya bawa d'an shi abinda yakeso, nan take nadama ta rufesa lokaci na farko d'aya yi tir da (zuciya irin tasa na Ayusher).
"Alh, Abubakar bakace komi" boye damuwarsa yayi tare dayin murmushi yake Wanda yafi kuka ciwo "ba komai Alhaji Allah ya kyauta, sai anjima" ya tashi ya wuce ba tare dayace komai ba...
Gida kuma bayan fitar baba zaune saukai jugum suna jajanta wannan Abu d'aya samesu, wannan shine ga duka ka kuma tsunka jaka, Abdool Ameena takai d'aki Wanda yayi bacci sai ajiyan heart yake, sannan ta dawo inda Mama suna tattauna wad'annan ibtila'i dake bibiyarsu a d'an tsakanin, lallai Allah shike jarabtar bawansa suna fatar su zamo cikin masu cinye ta, Ameena gani take tafi kowa ganin rayuwa, Asma'un da ta rage mata mai bata shawara sa d'auke mata kewa gashi k'addara tazo ta rabasu, yanzu ma ta ina zasu samu labarin Asma'un bayan ko waya batada ita yanzu, dan daga ita sai kayan jikinta tabar gidan komai bata d'auka, gashi ta manta sunan garin dan tabbas ta fad'a Mata amma bazata iya tunawa ba, ko wacce irin rayuwa zatayi a gidan Aurenta a wannan yanayi sa taje musu zasu karb'eta kosu wulak'anta ta? Nan tayi saurin nema mata sauk'i gurin Allah, haka suka wuni gidan ba dad'i kowa sai jimami yake.
_such is life_
Baba kuwa k'asa komawa gida yayi bayan yazo gaf k'ofar gidan ya dudduba kozai ga wannan takardar amma ina bata ba labarin ta, jin yayi komai baya mishi dad'i, sai gashi hadda k'wallarsa sam baiyima Asma'u adalci ba, yafi kowa sanin biyayya irin ta 'ya'yansa amma ya rufe idonsa, lallai zuciya mugun nama CE, kowa ya biye mata zata kaishi ta baro ne, lallai kowa yahau dokin fushi k'arshen sa nadama ne (yana daga cikin karantarwar manzo S.A.W idan kana cikin fushi kada kayi magana sannan kada ka yanke hukunci cikin fushi dan k'arshen sa dana sani ne) Allah yasa mudace.
Sai dare ya samu sukunin komawa gida, shima jiki ba k'wari ya shiga, kamar yadda Inna ta saba tarbonsa haka ta tarbesa ba tare data nuna mai komai ba, kamar ba abinda ya faru, k'ara jinjina hak'uri irin na Inna yayi sau da yawa yakan tauye mata hakki shikansa ya sani amma bata taba nuna mishi damuwar, lallai mace tagari ni'imace(haka yake duniya d'an jin dad'i ce amma mafi jin dad'in ta Wanda ya dace da mace ta gari).
Haka suma su Ameena sukazo suka gaishe shi kamar yadda suka saba, zasu tashi yace su tsaya yanada magana, ayan da yayi maganan cikin taushin murya, abun har mamaki ya basu, nan dai ya labarta musu yadda sukayi da Abokin nasa, tare da nuna musu nadamarsa.
"Alhaji ka dad'e kana tauyeni sau da yawa kana maida damuwar kowa ba damuwa, damuwarka kad'ai kake dauka damuwa, kama rayuwa da fushi kana yankewa mutane cikin fushi, to yanzu gashi wagari ya waya, ka salwantar mana da yarinyar akan son ran wasu, me kayi kenan" Inna ta gayamai magana cikin nutsuwa.
"Baba shiyasa ake son bawa mutum uziri a rayuwa, lokacin da ka shigo nida Asma'u munaso muyi maka bayani amma haka rufe ido kak'i bamu dama" nan ta basu labarin abinda ya faru a lokacin da Asma'u ta kira Abdulrahim" Amma kayi hak'uri In na fad'i ba dai-dai ba".
"To kaji ma abinda ya faru ko amma saboda rashin bata uzirunka a rayuwa kak'i sauraren kowa".
Shiru baba yayi nadama na k'ara lullub'esa, duk abinda suka fada gaskiya ba karya, sai hango lokacin da Asma'u take rik'e mishi kafa takeyi amma yayi biris yak'i saurarenta, tuni tausayinta ya kamashi lallai baiyi Mata adalci ba.
Hak'uri ya basu tare da tabbacin inshaa Allah zai nemota duk inda take.
Kwana ki sun shura watanni sun wuce kullum Baba yawon Sokoto da garuruwanta saidai kuma ba'a dace ba, ganin abin yayi yawa duk ya dami Kansa yasa Mama cewa.
"Ka hak'ura da yawon nan haka idan da rabon mu gaba zaka ganta ta kawo Kanta har gida, idan kuma babu rabo zafin nema bazai kawo samu ba, hakan ya hak'ura dole tare da bibiyarta da Addu'ar fatan Alkhairi aduk inda take.
Ameena kuwa zuwa yanzu zaman gida ya gama isanta gaba d'aya saukinta ma tana teaching da Baba ya samo mata yanzu tsawon shekara biyar kenan da rabuwarsu gashi duk masu zuwa sun d'auke kafarsa, a halin yanzu ba abinda takeso irin tayi aure shine akwai kwanciyar hankalinta (dan Mace komai kamewarta, idan batada aure to mutuncinta ragaggene a idon mutane, balle kuma wad'anda suka d'auki zawarci a lasisin iskanci suka samu tunda yanzu su zawarane ba namijin da zai Aure yace yana Neman budurci, to ai ba anan gizon yake saka ba, walla d more kikayi zina kina bazawara bakida wani hukunci daya wuce a jefeki, ba riba kenan, a tunani zawarci wata damace da mace zata K'ara sanin rayuwa, ta kuma gyara halayenta, kowanne aure yanada sila a rabuwarsa saiki duba meya kashe miki aure dan gyarawa gaba, bawai ki lalace ba, Allah yasa mudace) ayuwar zawarci rayuwace mai cike sa kalubale da tashin hankali, zaman gida ya gama isarta yau idan mace takai munzali tofa da batayi Aure ba, zaman sai kasance gashi nan dai na ganin laifi ne keda iyayenki, shiyasa Ameena ta damu sosai da rashin Auren, sai ba yadda zatayi dan tasan komai lokaci ne.
Yau kamar kullum Mansur ne yaje ya d'auko Abdool daga school, da gudu ya shigo yana murna "Mami kinga Nina yi na d'aya" ya fad'a yana nuna mata result d'in da gift d'inta aka bashi.
"Iyye yaron Inna kaifa akwai rashin ji amma akwai k'ok'ari" Jan tayi zuwa jikinta tana duba idonsa "waini kam idon nan naka Abdool anya lafia ko?"
Inna dake fitowa tace "me idon yayi?"
"Kiga farin yana surkawa da pink," duba idon Inna "tabbas ya kamata kuje asibiti" shikam sai k'ok'arin nunama inna report sheet yake, ba abinda ya damesa....
Likitan ya tabbatar musu ba wata babbar matsala bace, ciwon a jininsa yake so yayi inherited ne saidai ya kamata a nema mishi medical saboda idon yayi lasting, sai yanzu Ameena ta tuna tana ganin idon Auwal suna irin hakanan sometimes, no wonder shiyasa yake amfani da glass always Ashe medical ne.
**************
Har k'ofar gida suka sauke malam Garba da k'annin Ard'o sannan suka isa gida suma.
Da kallon mamaki iya Hari ta bisu sannan tace "malam ina kuka shige tun safe, wagga kuma fa?"
"Ai dai kin kawo tabarma tukun" tabarma tasa Shatu ta kawo tare da shimfida sannan ta kawo musu ruwa.
Zama sukayi sannan Baba yace Asma'u tasha ruwa ba musu tasha, guri ya nunawa Hari da tayi musu tsaye k'erere tana musu kallon dibar arziki, tuni jikin Asma'u yayi sanyi.