Sashe 15
Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
```Wannan page d'in nakune 'yan makarantar madarasatul nurul Islam littahafizil Qur'ani
Kareem,kabino area,Argungu```🕌
_Irinsu Nafisa muh'd, Fareeda Nana b/mashaya, Mamu Aliyu, Saudat yahya, Meena dikko, Amina Garba, Bilkis, Hajjo, Aina'u Idris and rest kuna raina koda yaushe#❤❤❤#_
📝 *Episode* 106-110
Maryam wacce tana mik'awa Hajia sak'on Auwal ta shige bedroom room d'inta, sai jin k'aran fad'uwar abu tayi aiko da gudu ta fito ganin mahaifiyarta kwance ba numfashi yasa tayi Kanta cikin kid'ima tana jijjigata, amma ko alaman tashi batayi ba, aiko da gudu tayi part d'in Rafia tayi sa'a Ayuba nanan, jin abin ya faru yasa suka biyota cikin tashin hankali, Rafia ce tayi Kanta ta rungume ta yayin Auwal yace a kawo ruwa, da sauri Maryam ta kawo ruwa Shafa mata akayi, nan take ta sauke ajiyar zuciya, bud'e ido tayi a hankali ta sauke a kansu sannan ta maida kallonta ga takardar da ke jinke a hannunta, wani kuka ta rushe dashi "why Auwal, meyasa zakayimin haka".
Ayuba ne yayi k'arfin halin cewa " Momy me kuma Auwal yayi miki?" Takardar ta mik'a masa, ansa yayi tare da karantawa a fili.
_"kiyi hak'uri momynah nasan koda wasik'ata zata sameki ba zakiyi farinciki da ita ba, sai ba yadda zanyi dole ce tasa zan barku, bazan iya ci gaba da zama kusa da inda zanji labarin Ameena ba, alhalin bama tare, dole zan nisanta kaina daku da kowa nawa, kada ku wahalda kanku nemana danni kaina bansan inda na dosa ba, pls kiyafemin Momy kiyimin fatan Alkhairi, kada ki tsinemin, idan kikayi haka rayuwa zata ga garari, ma'assalam_
D'anki *Auwal Sada*
Koda ya gama karantawa zuface ke keto masa duk da fanka da na'oural sanyi dake aiki, yama kasa magana, Maryam tuni hawaye ya wanke mata fuskarta, Rafia ma tashin hankali taf fuskarta dan batasan haka abin zai zama ba.
Momy kuwa sai sambatu takeyi tana kiran Auwal dan Momy akwai son d'iya, hakan yasa wutar k'iyayyar Ameena da d'anta ta k'ara ruruwa a ranta dan duka ita d'orama laifi, wai ba a banza tabar Auwal ba, wannan son ya wuce hankali, tunda harya kasa ganin girman laifinta ya barsu saboda ita.
Nan dai suka wuni cikin jimami ga tsoro fal ranta na idan Alhaji ya dawo me zatace masa, gashi gobe Suke tsumayen dawowar sa, dak'yar ta kira Maman su Rafia ta gayamata abinda ya faru, Ummita kuwa da raji rud'ewa tayi, dan ita harta fara shirye,-shiryen Amarcewa(tab to ai sai aje a rungumi big sowie Ummita) lol.
****************************
*Washe gari*
*12:00pm.........*
Jirginsu Alhaji Sada ya sauk'a a Sakkwato birnin shehu, Sani, Hajia, Maryam ne sukaje tarbonsa, yayi farincikin ganinsu amma yafi k'osawa yaje yaga 'yan jikokinsa musamman Abdool dan yaron ya shege masa ransa, sonsa yake sosai bada wasa ba, saidai baya nunawa gudun tashin hankali, sanda suka isa kowa saida yazo gaidashi amma ba Auwal da familyn sa, k'asa daurewa yayi ya tambaya ko sunyi tafiya ne.
Ganin yayi kowa yayi shiru, hakan yasa jikinsa yin sanyi dan yafi ba, lafiya a jikinsa, Hajia ce tayi k'arfin halin cewa "Alhaji ka bari kaci abinci ka huta tukunna sai ayi maka bayanin komai" jiki a sanyaye tayi maganar.
Ba shida zabi hakan akayi bayan yaci ya huta haka ta kora masa bayanin komai daya faru, har zuwa tafiyar Auwal, shiru yayi nad'an lokaci kafin ya dago idonsa da suka rine sukayi ja ya nuna Hajia da yatsa.
"Ke bani mamaki kaltume duk da babu mamaki in ankai la'akari da rashin son da kike nunama Ameena, tau burinki ya cika Ameena tabar miki gida Auwal ma ya bita yanzu sai kije ki zauna da wad'anda kikeso" ta bud'e baki zatayi magana, ya dakatar da ita "bannson jin komai daga gareki tashi ki tafi" ya fad'a yana nuna mata k'ofa dama daga ita sai shine a d'akin, tashi tayi ta fice jiki ba k'wari, dan tasan hak'uri irin na Alhaji duk yakai gayin fad'a to an kureshi ne, amma ai bai kamata yaga laifinta ba, komai ya faru au Ameena ce sila, itakam wannan shine adakeka a hanaka kuka.
Alhaji sai safa da marwa yakeyi ransa a jagule, tabbas Auwal bai kyauta ba, koma meye ya faru bai kamata yabar gida, duk da iya cuta an Riga an cucesa, dan wannan dagaji sharri ne akayi mata, dan yasan Ameena ba zata tab'a aikata wannan danyen aikin ba, kuma yasan Hajia nada tsananin zafi da ak'ida Mara tushe da asali, amma yasan ba zata aikatawa Ameena wannan aikin ba, to abin tambaya anan waye ya aikata? Babu ansa "Allah ya sawwaka" ya fad'a a fili, dama iya zaman da Allah ya d'ibar musu kenan, koda wannan koba sa wannan ba tabbas sai sun rabu dai2 wannan lokacin
Bud'e wardrobe yayi dan d'aukar Abu kawai sai Leda ta
Fad'o takardune na bud'e account da komai daya k'unsa sai diary da wasik'u guda biyu, bud'e d'ayar yayi yaga ansa *zuwa ga Ameena* rufewa yayi ya bud'e d'ayar Wanda ta kasance tashi ce.
Shima dai ban hak'urin ne da Neman gafara, sai Amanar *Abdulmajeed* daya d'anka masa da kuma bayanin diary da information na Account ya aje hannunsa har sai Abdool ya mallaki hankalinsa ya mallaka masa, sai wasik'a da yake rokon ya bayar a kaiwa Ameena, bayan ya gama karantawa yace "na yafeka Auwal duk da baka kyauta min a matsayina na mahaifi ba, wannan dalilin bai isa yada ka tafi ba, amma ba komai Allah ya tsareka a duk inda kaje ya kuma dawo mana dakai lafia wuri kusa kazo ka kula da d'anka da kanka".......
B'angaren Ameena kuwa kokai waye idan ka ganta dole ka tausaya mata, ta fita hayyacinta gaba d'aya tayi bak'i ta rame sosai kullum cikin kuka take musamman ganin an kwaso kayanta, yanzu shikenan ta zama bazawara, abin tafi tsana a rayuwarta ada sai takega duk matar da ta zama bazawara a dalilin saki to laifinta ne, ita tayi abinda yasa aka saketa, amma a yanzu ta gane ba haka abin yake k'addara wacce bata wuce fata, ta gane Ashe ba matar da ke son a saketa koda kuwa ita tayi laifi, balle irin su da basuji basu gani(to in banda Ameena wake so yayi aure yau gobe ace ya dawo gidansu ai saida k'addara wacce ba'a fata Allah ya kyauta).
Ga Abdool kullum kukan Dadynsa yakeyi Abu duk ya had'e yayi mata yawa, danma ga Asma'u kusa ita ke d'auke masa kewar Dadynsa, Mama da Baba kullum cikin kwantar mata da hankali suke, Mansur kullum yana cikin kawo Abdool kayan wasa da kayan kwalama irin na yara idan yaje School 'yan Kud'insa duk can suke tafiya duk dan su kwantar Mata da hankali, Firdausi ma tazo lokacin da taji, itama Sam abin baiyi Mata dad'i, musamman ma sharrin yafi komai cin rai, inda Allah ya sota duk Wanda yaji kai tsaye yake k'aryatawa, saboda sanin halin kirkinta(tau zama dan kwarai Nada rana dan wata rana ake gujewa mu d'aure mu k'are mutuncinmu).
Alhaji washe gari yazo Argungu, Baba ya tarbesa kamar ba abinda ya faru dan yasan ba laifinsa bane, hak'uri ya k'ara bashi akan abinda ya faru, tare da tabbatar masa Sam koda abin ya faru bashi gari, saida ya dawo yakeji nan yake gayamai tafiyar Auwal, nan Baba ya jajantamai tare da fatar Allah ya bayyana shi, tsaraba Ameena da Abdool ya fito dasu hadda ma Asma'u yayima dan yasan tana gidan lokacin da ya tafi, tare da kayan buk'atar Ameena da Abdool na yau da kullum, dan yayi Alkawarin kula dasu har sai tayi Aure.
Baba saida Alhaji ya nuna b'acin ransa tukun ya anshi kayan dan yace bazai Ansa ba, saida Alhaji yace bai hak'ura da abin da yw faru ba kenan, ai sun Riga sun zama d'aya tunda har rabo ya shiga tsakani, hakan dai dole ya ansa, har Mama saida ta fito suka gaisa sannan ya bata hak'uri itama.
Lokacin da Ameena tazo nasiha sosai yayi mata tare da bata hak'uri sannan ya tabbatar mata har yanzu shi ubane gareta komai ya sameta ta sanar da shi, kud'i ya bata tare da wasik'ar Auwal, saida yayi mata fad'a sannan ta Ansa, haka ya tafi yana tausayawa mata dan bazaiso hakan ra faru akan Maryam ba.
Sosai ya k'ara daraja da girma akan idon Ameena da iyayenta.
Sai dare ta d'auko wasik'ar Auwal da tunda aka bata ta kaita ta ajiye, dan ita yanzu lamarin maza ya fita Kanta kuma duk haushi Suke bata(dama ai duk macen da aka saka tofa duk maza haushi zasu rik'a bata zata d'auka duk Wanda ta aura zai iya sakinta komai soyayyar da yake mata kuwa.
Bud'ewa tayi ta fara karantawa..
_"gareki masoyiyata tahar abada, Ameena nasan zanyi bak'i a gurin ki dan duk wacce aka saka saki uku kai tsaye tabbas zata girgiza kuma zata tsani wannan mijin, harga Allah duk da abinda idanuwana suka ganemin, zuciyata ta k'asa yadda da abinda wani barinta ke gayamata akanki, saidai ki sani dole ne na shiga rud'u dan nina gani ba ji nayi ba, amma inaso ki d'auki wannan a matsayin k'addarar muce, ki tausayawamin ki tausayawa d'ana *Abdulmajeed* ki zame masa uwa da uba agareshi ki bashi dukkanin tarbiya ta gari, dan kuwa ke uwace ta gari a gareshi, pls kada kibar rayuwarsa tayi garari koda kinyi aure ne, ki zama majib'incin lamurransa a dai2 gab'ar da ya rasa dukannin kulawata a matsayina na uba agareshi, na tafi bawai dan bana k'aunar sa ba Aa sai dan samun maslaha a gareni, ina miki fatan Alkhairi, ki saka a ranki zan rayu da sonki a kowanne second na rayuwa"._
*naki Auwal Sada*.
Koda ta gama karantawa hawaye sun wanke mata fuska, zuciyarta sai rad'ad'i take mata da suya, Abdool ta rungume tsam a k'irjinta tana tausayawa rayuwarsa, yaro k'arami ko wace rayuwa zaiyi nan gaba.
"Allahumma ajirni fi musiba"..................
*ina mai Baku hak'uri sa babbar murya, akan jina da kukayi shiru kwana biyu, na shiga busy ne, amma Ku sani kuna raina#1❤#*
💄Meryerm Abdool💄
[8/8, 7:45 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
```Wannan page d'in nakune 'yan makarantar madarasatul nurul Islam littahafizil Qur'ani
Kareem,kabino area,Argungu```🕌
_Irinsu Nafisa muh'd, Fareeda Nana b/mashaya, Mamu Aliyu, Saudat yahya, Meena dikko, Amina Garba, Bilkis, Hajjo, Aina'u Idris and rest kuna raina koda yaushe#❤❤❤#_
📝 *Episode* 106-110
Maryam wacce tana mik'awa Hajia sak'on Auwal ta shige bedroom room d'inta, sai jin k'aran fad'uwar abu tayi aiko da gudu ta fito ganin mahaifiyarta kwance ba numfashi yasa tayi Kanta cikin kid'ima tana jijjigata, amma ko alaman tashi batayi ba, aiko da gudu tayi part d'in Rafia tayi sa'a Ayuba nanan, jin abin ya faru yasa suka biyota cikin tashin hankali, Rafia ce tayi Kanta ta rungume ta yayin Auwal yace a kawo ruwa, da sauri Maryam ta kawo ruwa Shafa mata akayi, nan take ta sauke ajiyar zuciya, bud'e ido tayi a hankali ta sauke a kansu sannan ta maida kallonta ga takardar da ke jinke a hannunta, wani kuka ta rushe dashi "why Auwal, meyasa zakayimin haka".
Ayuba ne yayi k'arfin halin cewa " Momy me kuma Auwal yayi miki?" Takardar ta mik'a masa, ansa yayi tare da karantawa a fili.
_"kiyi hak'uri momynah nasan koda wasik'ata zata sameki ba zakiyi farinciki da ita ba, sai ba yadda zanyi dole ce tasa zan barku, bazan iya ci gaba da zama kusa da inda zanji labarin Ameena ba, alhalin bama tare, dole zan nisanta kaina daku da kowa nawa, kada ku wahalda kanku nemana danni kaina bansan inda na dosa ba, pls kiyafemin Momy kiyimin fatan Alkhairi, kada ki tsinemin, idan kikayi haka rayuwa zata ga garari, ma'assalam_
D'anki *Auwal Sada*
Koda ya gama karantawa zuface ke keto masa duk da fanka da na'oural sanyi dake aiki, yama kasa magana, Maryam tuni hawaye ya wanke mata fuskarta, Rafia ma tashin hankali taf fuskarta dan batasan haka abin zai zama ba.
Momy kuwa sai sambatu takeyi tana kiran Auwal dan Momy akwai son d'iya, hakan yasa wutar k'iyayyar Ameena da d'anta ta k'ara ruruwa a ranta dan duka ita d'orama laifi, wai ba a banza tabar Auwal ba, wannan son ya wuce hankali, tunda harya kasa ganin girman laifinta ya barsu saboda ita.
Nan dai suka wuni cikin jimami ga tsoro fal ranta na idan Alhaji ya dawo me zatace masa, gashi gobe Suke tsumayen dawowar sa, dak'yar ta kira Maman su Rafia ta gayamata abinda ya faru, Ummita kuwa da raji rud'ewa tayi, dan ita harta fara shirye,-shiryen Amarcewa(tab to ai sai aje a rungumi big sowie Ummita) lol.
****************************
*Washe gari*
*12:00pm.........*
Jirginsu Alhaji Sada ya sauk'a a Sakkwato birnin shehu, Sani, Hajia, Maryam ne sukaje tarbonsa, yayi farincikin ganinsu amma yafi k'osawa yaje yaga 'yan jikokinsa musamman Abdool dan yaron ya shege masa ransa, sonsa yake sosai bada wasa ba, saidai baya nunawa gudun tashin hankali, sanda suka isa kowa saida yazo gaidashi amma ba Auwal da familyn sa, k'asa daurewa yayi ya tambaya ko sunyi tafiya ne.
Ganin yayi kowa yayi shiru, hakan yasa jikinsa yin sanyi dan yafi ba, lafiya a jikinsa, Hajia ce tayi k'arfin halin cewa "Alhaji ka bari kaci abinci ka huta tukunna sai ayi maka bayanin komai" jiki a sanyaye tayi maganar.
Ba shida zabi hakan akayi bayan yaci ya huta haka ta kora masa bayanin komai daya faru, har zuwa tafiyar Auwal, shiru yayi nad'an lokaci kafin ya dago idonsa da suka rine sukayi ja ya nuna Hajia da yatsa.
"Ke bani mamaki kaltume duk da babu mamaki in ankai la'akari da rashin son da kike nunama Ameena, tau burinki ya cika Ameena tabar miki gida Auwal ma ya bita yanzu sai kije ki zauna da wad'anda kikeso" ta bud'e baki zatayi magana, ya dakatar da ita "bannson jin komai daga gareki tashi ki tafi" ya fad'a yana nuna mata k'ofa dama daga ita sai shine a d'akin, tashi tayi ta fice jiki ba k'wari, dan tasan hak'uri irin na Alhaji duk yakai gayin fad'a to an kureshi ne, amma ai bai kamata yaga laifinta ba, komai ya faru au Ameena ce sila, itakam wannan shine adakeka a hanaka kuka.
Alhaji sai safa da marwa yakeyi ransa a jagule, tabbas Auwal bai kyauta ba, koma meye ya faru bai kamata yabar gida, duk da iya cuta an Riga an cucesa, dan wannan dagaji sharri ne akayi mata, dan yasan Ameena ba zata tab'a aikata wannan danyen aikin ba, kuma yasan Hajia nada tsananin zafi da ak'ida Mara tushe da asali, amma yasan ba zata aikatawa Ameena wannan aikin ba, to abin tambaya anan waye ya aikata? Babu ansa "Allah ya sawwaka" ya fad'a a fili, dama iya zaman da Allah ya d'ibar musu kenan, koda wannan koba sa wannan ba tabbas sai sun rabu dai2 wannan lokacin
Bud'e wardrobe yayi dan d'aukar Abu kawai sai Leda ta
Fad'o takardune na bud'e account da komai daya k'unsa sai diary da wasik'u guda biyu, bud'e d'ayar yayi yaga ansa *zuwa ga Ameena* rufewa yayi ya bud'e d'ayar Wanda ta kasance tashi ce.
Shima dai ban hak'urin ne da Neman gafara, sai Amanar *Abdulmajeed* daya d'anka masa da kuma bayanin diary da information na Account ya aje hannunsa har sai Abdool ya mallaki hankalinsa ya mallaka masa, sai wasik'a da yake rokon ya bayar a kaiwa Ameena, bayan ya gama karantawa yace "na yafeka Auwal duk da baka kyauta min a matsayina na mahaifi ba, wannan dalilin bai isa yada ka tafi ba, amma ba komai Allah ya tsareka a duk inda kaje ya kuma dawo mana dakai lafia wuri kusa kazo ka kula da d'anka da kanka".......
B'angaren Ameena kuwa kokai waye idan ka ganta dole ka tausaya mata, ta fita hayyacinta gaba d'aya tayi bak'i ta rame sosai kullum cikin kuka take musamman ganin an kwaso kayanta, yanzu shikenan ta zama bazawara, abin tafi tsana a rayuwarta ada sai takega duk matar da ta zama bazawara a dalilin saki to laifinta ne, ita tayi abinda yasa aka saketa, amma a yanzu ta gane ba haka abin yake k'addara wacce bata wuce fata, ta gane Ashe ba matar da ke son a saketa koda kuwa ita tayi laifi, balle irin su da basuji basu gani(to in banda Ameena wake so yayi aure yau gobe ace ya dawo gidansu ai saida k'addara wacce ba'a fata Allah ya kyauta).
Ga Abdool kullum kukan Dadynsa yakeyi Abu duk ya had'e yayi mata yawa, danma ga Asma'u kusa ita ke d'auke masa kewar Dadynsa, Mama da Baba kullum cikin kwantar mata da hankali suke, Mansur kullum yana cikin kawo Abdool kayan wasa da kayan kwalama irin na yara idan yaje School 'yan Kud'insa duk can suke tafiya duk dan su kwantar Mata da hankali, Firdausi ma tazo lokacin da taji, itama Sam abin baiyi Mata dad'i, musamman ma sharrin yafi komai cin rai, inda Allah ya sota duk Wanda yaji kai tsaye yake k'aryatawa, saboda sanin halin kirkinta(tau zama dan kwarai Nada rana dan wata rana ake gujewa mu d'aure mu k'are mutuncinmu).
Alhaji washe gari yazo Argungu, Baba ya tarbesa kamar ba abinda ya faru dan yasan ba laifinsa bane, hak'uri ya k'ara bashi akan abinda ya faru, tare da tabbatar masa Sam koda abin ya faru bashi gari, saida ya dawo yakeji nan yake gayamai tafiyar Auwal, nan Baba ya jajantamai tare da fatar Allah ya bayyana shi, tsaraba Ameena da Abdool ya fito dasu hadda ma Asma'u yayima dan yasan tana gidan lokacin da ya tafi, tare da kayan buk'atar Ameena da Abdool na yau da kullum, dan yayi Alkawarin kula dasu har sai tayi Aure.
Baba saida Alhaji ya nuna b'acin ransa tukun ya anshi kayan dan yace bazai Ansa ba, saida Alhaji yace bai hak'ura da abin da yw faru ba kenan, ai sun Riga sun zama d'aya tunda har rabo ya shiga tsakani, hakan dai dole ya ansa, har Mama saida ta fito suka gaisa sannan ya bata hak'uri itama.
Lokacin da Ameena tazo nasiha sosai yayi mata tare da bata hak'uri sannan ya tabbatar mata har yanzu shi ubane gareta komai ya sameta ta sanar da shi, kud'i ya bata tare da wasik'ar Auwal, saida yayi mata fad'a sannan ta Ansa, haka ya tafi yana tausayawa mata dan bazaiso hakan ra faru akan Maryam ba.
Sosai ya k'ara daraja da girma akan idon Ameena da iyayenta.
Sai dare ta d'auko wasik'ar Auwal da tunda aka bata ta kaita ta ajiye, dan ita yanzu lamarin maza ya fita Kanta kuma duk haushi Suke bata(dama ai duk macen da aka saka tofa duk maza haushi zasu rik'a bata zata d'auka duk Wanda ta aura zai iya sakinta komai soyayyar da yake mata kuwa.
Bud'ewa tayi ta fara karantawa..
_"gareki masoyiyata tahar abada, Ameena nasan zanyi bak'i a gurin ki dan duk wacce aka saka saki uku kai tsaye tabbas zata girgiza kuma zata tsani wannan mijin, harga Allah duk da abinda idanuwana suka ganemin, zuciyata ta k'asa yadda da abinda wani barinta ke gayamata akanki, saidai ki sani dole ne na shiga rud'u dan nina gani ba ji nayi ba, amma inaso ki d'auki wannan a matsayin k'addarar muce, ki tausayawamin ki tausayawa d'ana *Abdulmajeed* ki zame masa uwa da uba agareshi ki bashi dukkanin tarbiya ta gari, dan kuwa ke uwace ta gari a gareshi, pls kada kibar rayuwarsa tayi garari koda kinyi aure ne, ki zama majib'incin lamurransa a dai2 gab'ar da ya rasa dukannin kulawata a matsayina na uba agareshi, na tafi bawai dan bana k'aunar sa ba Aa sai dan samun maslaha a gareni, ina miki fatan Alkhairi, ki saka a ranki zan rayu da sonki a kowanne second na rayuwa"._
*naki Auwal Sada*.
Koda ta gama karantawa hawaye sun wanke mata fuska, zuciyarta sai rad'ad'i take mata da suya, Abdool ta rungume tsam a k'irjinta tana tausayawa rayuwarsa, yaro k'arami ko wace rayuwa zaiyi nan gaba.
"Allahumma ajirni fi musiba"..................
*ina mai Baku hak'uri sa babbar murya, akan jina da kukayi shiru kwana biyu, na shiga busy ne, amma Ku sani kuna raina#1❤#*
💄Meryerm Abdool💄
[8/8, 7:45 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽