Sashe 20
Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
_Allahumma inni astahiruka bi ilmika, wa'astagfiruka bik'udratika, wa'as'aluka min fadlikal azim, fa'innaka tak'dir wala ak'dir, wata'alam wala a'alam, wa anta allamul guyuwbu, in kunta ta'alamu anna hazal amru(saika fad'i buk'atar ka) khairun liy fiy deeniy wama'ashi wa'akibatu amri, fak'durhu liy wayassirhu liy summa barak liy fiyhi, wa'in kunta ta'alamu Anna hazal amru sharrun liy fih deeniy wama'ashi wa'ak'ibati amri, fasrifhu anni wasrifni anhu wak'dul liy khairan haisu kana summa raddani bihi._
Fassara
*ya Allah ina Neman zabinka domin iliminka, kuma ina Neman ka bani iko domin ikonka, kuma ina rok'onka daga falalarka mai girma, domin Kaine mai iko ni kuma bani da ikon, kuma kaine masani ni kuma bani da sani, kuma Kaine masanin abubuwan fake, Ya Allah! Idan kasan cewa wannan al'amari (ka ambaci buk'atar) Alkhairi ne a gareni cikin addinina da rayuwata da k'arshen al'amarina (wata rayuwar ) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka k'addara mini shi, kuma ka sauk'ak'e mini shi, sannan ka Albarka ce ni a cikinsa, kuma idan kasan wannan al'amari sharri ne, gareni a cikin, addinina da rayuwa da k'arshen al'amarina (a wata rayuwar) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka kawar da shi daga gareni, kuma ka kawar dani daga gareshi, ka k'addara mini Alkhairi a duk inda yake, ka kuma sani in yarda dashi*
(Cikin husnul Muslim take, yana da kyau komai bawa zai gabatar a rayuwa ya nemi zabin Allah a ciki. Allah yasa mudace)
Bayan ta kammala ta nad'e dadduma tare da kwantawa kan bed, tana tunanin wannan al'amarin,sannu a hankali natsuwa ta fara shigarta, a haka bacci mai dad'i yayi gaba da ita.................
_masoyana ina Neman addu'o'inku, I really in need of it👏🏽 ina muku fatar Alkhairi a duk inda kuke_
💄 Meryerm Abdool💄
[8/12, 6:07 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
🙏🏻 *From he we are, and 2 he we return, oh! Allah forgive our dead one, that find their self in absence of no one to pray 4 them, ya Allah have mercy on them, and make our dead day the day of happiness 2 us, ya Allah don't take our souls until urs happy with our souls ameen🙏🏻*
📝 *Episode* 126--130
Koda Yusuf ya jema iyayensa bai samu matsala da yake yayi dace da iyaye masu hangen nesa, sunce tunda shi yake sonta in har anyi bincike 'yar kirki ce to su basu da matsala, amma 'yan uwansa sunce sudai basu amince ya auri bazawara ba yana saurayi dashi, saida Baban yayi musu fad'a yace "meye naku a ciki tunda a hakan yakeson abarsa, kuma ma in banda abinku, fiyayyen halitta ma da bazawara ya fara, to meye dan yace zaiyi koyi dashi idan har ba zaku bashi k'warin gwuiwa ba bai kamata Ku hanashi dan haka kar in sake jin wani daga cikinku ya soki wannan tafiyar" da haka Baban ya kwabesu dole suka hak'ura badan ransu yaso ba.
Koda ya fad'ama Ameena tayi farinciki sosai a ranta amma bata wani nuna mishi cewa kawai tayi "to yayi" sauke numfashi yayi "Haka kawai zakice Ameena tah, kamar bakya farinciki".
" um inayi mana tome kakeso ince ne".
Smiling yayi kamar tana kallon sa harda lumshe ido " cewa ya kamata kiyi yaushe zaka turo my love".
Dariya zancensa ya bata dama tasan Yusuf da barkwanci kamar me "au dariya KO, ai gara ma ki gayama Baba dan kada ayi mai ba zata, dan bazan tsaya kallon ruwa ba kwado yazo yamin kafa" nan ma murmushi kawai tayi dama Ameena ba yawan surutu...
"Um nidai bana Abdool dan naga yau miskilancin ya motsa" nan ta ba Abdool sukayi ta fira kamar wani babba dama Abdool badai wayau ba, in yayi wata magana ka d'auka fad'a mishi akayi.
Malam Sa'id mahafin Yusuf yayi duk binciken da ya dace ya kuma tabbatar da Tarbiyar Ameena, hakan yasa ya gaya ma 'yan uwansa domin Suje su nema nasa auren.
Lokacin da Ameena taje ma su Baba da labarin sunyi farinciki Sosai dama babban burinsu kenan Ameena tayi aure, shima yayi nashi bincike kamar yadda addini ya tsara, hakan yasa saka shiga cikin maganar har an tsaida rana wata uku masu zuwa.
Suma su Yusuf ba wasu masu arziki bane akwai dai rufin asiri, nan family house d'insu, aka gyara wasu dak'una biyu aka maida mata room and parlour sai toilet, ba laifi zaman dai mutum d'aya a talauce ba sarauce ba.
Alhaji Sada ma da yaji maganan Auren yayi mata murna Sosai, kuma yace ko bayan tayi Aure Abdool zaici gaba da zama gurin su Mama, dan yasha alwashin saidai in Abdool ya girma yakai Kansa Sokoto da kansa tunda dai sun nuna basa ra'ayinsa har gara iyayensa maza suna zuwa dubashi sa'in sai kuma Maryam kafin tayi aure duk da Hajia ta hanata zuwa hakan bai hana in Alhaji zaije ba, ta bishi wani sa'in kuma ta bada Abubuwa akai masa.
Cikin ikon Allah Anyi Aure lafia cikin farinciki ranar Ameena tasha kukan rabuwa da iyayenta uwa uba kuma Abdool shima dai yasha naji kukan dakyar aka banbareshi jikinta, a son Yusuf ma yaso abasu shi amma Baba yace Aa a barshi nan yayi karatunsa lokacin yana 6years yana primary 1, haka dai Ameena ta tare cikin aminci a gidan Angonta Yusuf.
Farkon Auren ta had'u da kalubalen dangin miji haka zasuzo suna yad'a mata magana, da yake macece mai matuk'ar hak'uri hakan yasa sam bata nuna tamasan sunayi, Amma kam surukarta suna zaune lafia, yawan kyautata Mata da dawainiya da take Mata, haka zata saka Yusuf ya d'auko kayansu ita da Abbansa su had'u su wanke su goge, komai ta dafa da nasu, suma 'yan uwan nasa da yake yayin nashi Mata ne duka suna gidan mazajensu sai dai in sunzo, shine namiji babba sai k'annin sa, hakan yasa in sukazo tana yawan kyautata musu gada Sam batada rowa ko kyashi tuni suma ta saye zukatansu(dangin miji saida kyautata ake zama lafia note women).
Taci gaba da teaching d'inta dan an samo mata transfer haka tana business d'inta, shima dai Yusuf teaching yake yana kuma zama kasuwa inda mahaifinsa da haka suka rufama junansu asiri Sam bakajin Kansu, zaman k'auna da soyayya suke dan sai yanzu tasan lallai Yusuf son gaskiya yake mata, kullum cikin tattali da nuna mata k'auna yake, Sakina ma anzo bikin tayi murna sosai dama ta dad'e tana hango son Ameena a idon Yusuf.
Tana zuwa Argungu lokaci zuwa lokaci har yanzu dai ba labarin Asma'u abin kullum yana ranta "oh ina zamu ganki Asma'u, Allah ka bayyana mana ita ka tsareta a duk inda take" kullum shine Addu'arta, Abdool na zuwa mata idan anyi Hutu.
Shekararsu 2 da Aure Yusuf ya samu Aiki a NNPC KADUNA, ba k'aramin farinciki sukayi da cigaban da ya samesu ba, haka yaje yayi interview aka bashi upper, watansa uku sannan ya dawo, nan ya gayama iyayensa zai wuce da Ameena dan an bashi gida, nan sukaje Argungu sukayi musu sallama, nan ma Yusuf saida ya tada maganar son abasu Abdool, hak'uri Abba ya basu yace kada su katse mai karatu, hakan suka wuce badan ransu yaso ba, irin kulawarda Yusuf ke bama Abdool shiyasa Ameena k'ara sonsa da ganin girmansa, haka sukayi bankwana da yan uwa da abokan arziki suka lula garin gwamna...
_safe trip_ 🚗
~~~~~~~~~~~~
Lokacin da labarin Auren Abdulrahim ya bazu a k'auye Kilgore mutane sai tururuwa sukeyi gidan dan ganin amarya da 'yan gulma da 'yan ganin kwam, da masu yabawa da masu tsinewa, su Lanti anzo sai yatsine take dan Uwar ta kitsa mata tana yad'a bak'ak'en maganganu, Abdulrahim ko dayaji tass yayi Mata sannan yace karta k'ara zuwa gidan muddin ba abin kirki zai kawo ba, aiko iya Hari ina wuta in fad'a inda take shiga banan take fita ba, cin mutunci gaske tayi masa, wai karya kuskura ya takurawa 'yarta akan wannan korarriyar wanda iyayenta suka sallama, cin fuska dai sai Wanda ta manta, ranar Asma'u tasha kuka tare da kewar gidansu lallai kowa yabar gida ya barshi, gata ana mata gori ba yadda zatayi, hakan ya k'ara ba Lanti kwarin gwiwar yi Mata iskanci son ranta, saidai batayi in Abdulrahim nanan dan tana shakkarsa, Saude kam haukane kawai batayi ba, da taji Auren Abdulrahim haka tazo har gida tayima iya Hari rashin kunya, wai ai ita tayi mata alk'awari amma tsabar munafurci ta bari ya auri wata ba ita ba, itako Sam bataga laifinta ba saima hak'uri ta bata akan lallai zai aureta ta shigo ta biyo, tace Allah ya kiyaye ta zama ta biyu ta d'auki sauran wata, ta yafe, dama ba sonsa take ba sha'awa ce kawai.
Kamar yadda Ard'o yace haka kuwa akayi an Gina mata ciki da falo hadda bayan gida. Lol
Shanu biyu Ard'o ya Ware yayi Mata kayan d'aki a matsayin sa na uba gareta, an gyara d'aki ba laifi, nan kuma wani gorin ya tashi habaici kam tasha harta gode Allah, zuwa yanzu ta fara sabawa da cin mutuncin Iya Hari da Lanti, amma kullum abin na kona ranta bata dai yadda zatayi ne, ga uban aiki gidan da yanzu ya dawo Kanta, komai ita danma Shatu na kamata inba idon Iya Hari, dan tuni tayi Mata iyaka da Asma'u, in kaga Asma'u saika tausaya mata duk tayi baki ta rame danma ta Saba da aiki a gida da sai tafi wahala, Abdulrahim baida halin magana a balbaleshi da bala'i itama Asma'u tace ya dena magana kada ya had'u da fushin mahaifiyarsa tunda ita ta haifeshi ya zama wajibi yayi mata biyayya, Ard'o ma yayi fad'a harya gajia amma a banza da maganan sa da babu duk d'aya suka ha Hari, saidai in ya samu tanayi yace ta aje inya fita ace tazo tayi dan ubanta (oh Asma'u kina ganin rayuwa).
Fassara
*ya Allah ina Neman zabinka domin iliminka, kuma ina Neman ka bani iko domin ikonka, kuma ina rok'onka daga falalarka mai girma, domin Kaine mai iko ni kuma bani da ikon, kuma kaine masani ni kuma bani da sani, kuma Kaine masanin abubuwan fake, Ya Allah! Idan kasan cewa wannan al'amari (ka ambaci buk'atar) Alkhairi ne a gareni cikin addinina da rayuwata da k'arshen al'amarina (wata rayuwar ) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka k'addara mini shi, kuma ka sauk'ak'e mini shi, sannan ka Albarka ce ni a cikinsa, kuma idan kasan wannan al'amari sharri ne, gareni a cikin, addinina da rayuwa da k'arshen al'amarina (a wata rayuwar) da magaggaucin al'amarina da majinkircinsa, ka kawar da shi daga gareni, kuma ka kawar dani daga gareshi, ka k'addara mini Alkhairi a duk inda yake, ka kuma sani in yarda dashi*
(Cikin husnul Muslim take, yana da kyau komai bawa zai gabatar a rayuwa ya nemi zabin Allah a ciki. Allah yasa mudace)
Bayan ta kammala ta nad'e dadduma tare da kwantawa kan bed, tana tunanin wannan al'amarin,sannu a hankali natsuwa ta fara shigarta, a haka bacci mai dad'i yayi gaba da ita.................
_masoyana ina Neman addu'o'inku, I really in need of it👏🏽 ina muku fatar Alkhairi a duk inda kuke_
💄 Meryerm Abdool💄
[8/12, 6:07 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
🙏🏻 *From he we are, and 2 he we return, oh! Allah forgive our dead one, that find their self in absence of no one to pray 4 them, ya Allah have mercy on them, and make our dead day the day of happiness 2 us, ya Allah don't take our souls until urs happy with our souls ameen🙏🏻*
📝 *Episode* 126--130
Koda Yusuf ya jema iyayensa bai samu matsala da yake yayi dace da iyaye masu hangen nesa, sunce tunda shi yake sonta in har anyi bincike 'yar kirki ce to su basu da matsala, amma 'yan uwansa sunce sudai basu amince ya auri bazawara ba yana saurayi dashi, saida Baban yayi musu fad'a yace "meye naku a ciki tunda a hakan yakeson abarsa, kuma ma in banda abinku, fiyayyen halitta ma da bazawara ya fara, to meye dan yace zaiyi koyi dashi idan har ba zaku bashi k'warin gwuiwa ba bai kamata Ku hanashi dan haka kar in sake jin wani daga cikinku ya soki wannan tafiyar" da haka Baban ya kwabesu dole suka hak'ura badan ransu yaso ba.
Koda ya fad'ama Ameena tayi farinciki sosai a ranta amma bata wani nuna mishi cewa kawai tayi "to yayi" sauke numfashi yayi "Haka kawai zakice Ameena tah, kamar bakya farinciki".
" um inayi mana tome kakeso ince ne".
Smiling yayi kamar tana kallon sa harda lumshe ido " cewa ya kamata kiyi yaushe zaka turo my love".
Dariya zancensa ya bata dama tasan Yusuf da barkwanci kamar me "au dariya KO, ai gara ma ki gayama Baba dan kada ayi mai ba zata, dan bazan tsaya kallon ruwa ba kwado yazo yamin kafa" nan ma murmushi kawai tayi dama Ameena ba yawan surutu...
"Um nidai bana Abdool dan naga yau miskilancin ya motsa" nan ta ba Abdool sukayi ta fira kamar wani babba dama Abdool badai wayau ba, in yayi wata magana ka d'auka fad'a mishi akayi.
Malam Sa'id mahafin Yusuf yayi duk binciken da ya dace ya kuma tabbatar da Tarbiyar Ameena, hakan yasa ya gaya ma 'yan uwansa domin Suje su nema nasa auren.
Lokacin da Ameena taje ma su Baba da labarin sunyi farinciki Sosai dama babban burinsu kenan Ameena tayi aure, shima yayi nashi bincike kamar yadda addini ya tsara, hakan yasa saka shiga cikin maganar har an tsaida rana wata uku masu zuwa.
Suma su Yusuf ba wasu masu arziki bane akwai dai rufin asiri, nan family house d'insu, aka gyara wasu dak'una biyu aka maida mata room and parlour sai toilet, ba laifi zaman dai mutum d'aya a talauce ba sarauce ba.
Alhaji Sada ma da yaji maganan Auren yayi mata murna Sosai, kuma yace ko bayan tayi Aure Abdool zaici gaba da zama gurin su Mama, dan yasha alwashin saidai in Abdool ya girma yakai Kansa Sokoto da kansa tunda dai sun nuna basa ra'ayinsa har gara iyayensa maza suna zuwa dubashi sa'in sai kuma Maryam kafin tayi aure duk da Hajia ta hanata zuwa hakan bai hana in Alhaji zaije ba, ta bishi wani sa'in kuma ta bada Abubuwa akai masa.
Cikin ikon Allah Anyi Aure lafia cikin farinciki ranar Ameena tasha kukan rabuwa da iyayenta uwa uba kuma Abdool shima dai yasha naji kukan dakyar aka banbareshi jikinta, a son Yusuf ma yaso abasu shi amma Baba yace Aa a barshi nan yayi karatunsa lokacin yana 6years yana primary 1, haka dai Ameena ta tare cikin aminci a gidan Angonta Yusuf.
Farkon Auren ta had'u da kalubalen dangin miji haka zasuzo suna yad'a mata magana, da yake macece mai matuk'ar hak'uri hakan yasa sam bata nuna tamasan sunayi, Amma kam surukarta suna zaune lafia, yawan kyautata Mata da dawainiya da take Mata, haka zata saka Yusuf ya d'auko kayansu ita da Abbansa su had'u su wanke su goge, komai ta dafa da nasu, suma 'yan uwan nasa da yake yayin nashi Mata ne duka suna gidan mazajensu sai dai in sunzo, shine namiji babba sai k'annin sa, hakan yasa in sukazo tana yawan kyautata musu gada Sam batada rowa ko kyashi tuni suma ta saye zukatansu(dangin miji saida kyautata ake zama lafia note women).
Taci gaba da teaching d'inta dan an samo mata transfer haka tana business d'inta, shima dai Yusuf teaching yake yana kuma zama kasuwa inda mahaifinsa da haka suka rufama junansu asiri Sam bakajin Kansu, zaman k'auna da soyayya suke dan sai yanzu tasan lallai Yusuf son gaskiya yake mata, kullum cikin tattali da nuna mata k'auna yake, Sakina ma anzo bikin tayi murna sosai dama ta dad'e tana hango son Ameena a idon Yusuf.
Tana zuwa Argungu lokaci zuwa lokaci har yanzu dai ba labarin Asma'u abin kullum yana ranta "oh ina zamu ganki Asma'u, Allah ka bayyana mana ita ka tsareta a duk inda take" kullum shine Addu'arta, Abdool na zuwa mata idan anyi Hutu.
Shekararsu 2 da Aure Yusuf ya samu Aiki a NNPC KADUNA, ba k'aramin farinciki sukayi da cigaban da ya samesu ba, haka yaje yayi interview aka bashi upper, watansa uku sannan ya dawo, nan ya gayama iyayensa zai wuce da Ameena dan an bashi gida, nan sukaje Argungu sukayi musu sallama, nan ma Yusuf saida ya tada maganar son abasu Abdool, hak'uri Abba ya basu yace kada su katse mai karatu, hakan suka wuce badan ransu yaso ba, irin kulawarda Yusuf ke bama Abdool shiyasa Ameena k'ara sonsa da ganin girmansa, haka sukayi bankwana da yan uwa da abokan arziki suka lula garin gwamna...
_safe trip_ 🚗
~~~~~~~~~~~~
Lokacin da labarin Auren Abdulrahim ya bazu a k'auye Kilgore mutane sai tururuwa sukeyi gidan dan ganin amarya da 'yan gulma da 'yan ganin kwam, da masu yabawa da masu tsinewa, su Lanti anzo sai yatsine take dan Uwar ta kitsa mata tana yad'a bak'ak'en maganganu, Abdulrahim ko dayaji tass yayi Mata sannan yace karta k'ara zuwa gidan muddin ba abin kirki zai kawo ba, aiko iya Hari ina wuta in fad'a inda take shiga banan take fita ba, cin mutunci gaske tayi masa, wai karya kuskura ya takurawa 'yarta akan wannan korarriyar wanda iyayenta suka sallama, cin fuska dai sai Wanda ta manta, ranar Asma'u tasha kuka tare da kewar gidansu lallai kowa yabar gida ya barshi, gata ana mata gori ba yadda zatayi, hakan ya k'ara ba Lanti kwarin gwiwar yi Mata iskanci son ranta, saidai batayi in Abdulrahim nanan dan tana shakkarsa, Saude kam haukane kawai batayi ba, da taji Auren Abdulrahim haka tazo har gida tayima iya Hari rashin kunya, wai ai ita tayi mata alk'awari amma tsabar munafurci ta bari ya auri wata ba ita ba, itako Sam bataga laifinta ba saima hak'uri ta bata akan lallai zai aureta ta shigo ta biyo, tace Allah ya kiyaye ta zama ta biyu ta d'auki sauran wata, ta yafe, dama ba sonsa take ba sha'awa ce kawai.
Kamar yadda Ard'o yace haka kuwa akayi an Gina mata ciki da falo hadda bayan gida. Lol
Shanu biyu Ard'o ya Ware yayi Mata kayan d'aki a matsayin sa na uba gareta, an gyara d'aki ba laifi, nan kuma wani gorin ya tashi habaici kam tasha harta gode Allah, zuwa yanzu ta fara sabawa da cin mutuncin Iya Hari da Lanti, amma kullum abin na kona ranta bata dai yadda zatayi ne, ga uban aiki gidan da yanzu ya dawo Kanta, komai ita danma Shatu na kamata inba idon Iya Hari, dan tuni tayi Mata iyaka da Asma'u, in kaga Asma'u saika tausaya mata duk tayi baki ta rame danma ta Saba da aiki a gida da sai tafi wahala, Abdulrahim baida halin magana a balbaleshi da bala'i itama Asma'u tace ya dena magana kada ya had'u da fushin mahaifiyarsa tunda ita ta haifeshi ya zama wajibi yayi mata biyayya, Ard'o ma yayi fad'a harya gajia amma a banza da maganan sa da babu duk d'aya suka ha Hari, saidai in ya samu tanayi yace ta aje inya fita ace tazo tayi dan ubanta (oh Asma'u kina ganin rayuwa).