← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 53

Sashe 21

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sauk'inta Mijinta na tausasa mata da nuna mata k'auna, inta zauna sai taita tunani "wato mu haka tamu k'addarar take an jarabcemu da uwar miji, haka aunty Ameena tayi fama, ashe nata nafila ne, gwanda ita ina kusa kuma zata kira gida taji dad'i to nifa ba ko d'aya, yanzu ko sakina akayi INA zan nufa, ya Allah ka sassauto da zuciyar Baba yafemin ya mai domin da family i'm in need of them badly".

Ana hakane akayi posting nasu gurin service ita da Abdulrahim, ba state d'aya aka ajesu ba shi Katsina ita kuma Edo, hakan yasa yaje ya nemi alfarma aka maida ita Katsina, nan ma anyi rigima da Iya Hari wai ba inda zataje, k'aryane meyakai mace bautar k'asa, nan ma saida Ard'o yayi da gaske sannan ta Shafa musu lafia, zaman su Katsina zamane mai dimbin tarihi a cikin rayuwar Auren su dan sai a sannan ne suka samu nutsuwa, dama Dr gida ake bashi, so basuda matsala haka suka gudanar da service d'insu cikin kwanciyar hankali, ko marmarin dawowa basuyi,ranar da suka isa Abdulrahim ya sayomata waya nan ta kira numbobin gidansu amma ba wacce ke nan jikinta ya k'ara sanyi da d'auka kodan karta kirane yasa Baba sasu canja layuka(ba haka bane baraye suka kwase musu wayoyi dare d'aya) lokacin da suka gama zasu dawo kamar karsu dawo sukeji, haka sukayo tsaraba sosai suka dawo amma kam Asma'u ranta fal tsoro za'a koma 'yar gidan jiya.

Hakan ko takasance bayan dawowar su akaci gaba daga inda aka tsaya wannan karon hadda gorin rashin haihuwa ganin suna cikin shekara ta uku da Aure ba haihuwa, Abu dai kullum ba sauk'i sai abinda yayi gaba, gashi anyi Auren Shatu mai tausaya mata.

Cikin ikon Allah Abdulrahim ya samu aiki a uduth Sokoto hakan yasa Ard'o yace ya d'auki matarsa su koma can da zama, Iya Hari cewa tayi bak'in ciki ake mata tunda tana taya ta aiki, banza yayi da ita danya San Neman a tanka ne.

Haka suka tattara suka koma Sokoto, kuma Ard'o yayi Iya kashedin duk ta taka Sokoto bakin Aurenta, dole ta lahe dan tasan rabuwa da Ard'o babbar asarace gareta.

Suna shekara cikin ta 5 da Aure Asma'u ta samo ciki, fad'ar irin farinciki da sukayi ba'a ma magana, haka sukaci gaba da kula da cikinsu cikin so da k'auna har ya isa haihuwa inda Abdulrahim da Kansa ya anshi haihuwar zankad'ed'iyar 'yarsa me kama dashi, baki kamar gonar auduga, su Modibbo anyi 'ya, Ard'o yaje yazo dasu da sunan ayi mata wankan jego tunda haihuwar fari CE batasan makari ba, Amma abin takaici ko kallo basu ishi Iya Hari ba, anyi ba'ayi ba dai kenan dan komai Asma'u ce kema Kanta, da bata iya ba saidai ta rub'e anan, tayi kukan rashin 'yan uwanta harta gode Allah, lallai naka sai naka, da sunanan da bata wulak'anta ba, Abdulrahim ne ke kama Mata aiki sai kuwa Shatu idan tazo shima idon uwarta kamar ya tsiyaye gurin harara, Abdulrahim ko saidai tace shanyayye Mara tayi.

Haka sati ya zagayo ranar suna yarinya taci suna *Ramlah* rago biyu da sa aka yanka, Abdulrahim yayi k'ok'ari dan yayi musu komai na goyo tsadaddi Hari ko sai yad'a magana anyi Aure ba dangi haka suna ma, Abu sai kace mayya, ita Kanta Asma'u abun na matuk'ar damunta, dan Abdulrahim yasha cewa ta bari suje Argungu suba Baba hak'uri, sanin halin mahaifinta na kaifi yasa tace cewa Aa su jira dai(tab aiya canja duniya ta horashi) lol.

Tun kan suyi arba'in ganin wahala tayi ma Asma'u yawa, balle Abdulrahim ya kawo sai k'arshen sati yake zuwa yasa, ga dawainiyar kula da kai da jaririya gana gida yasa Ard'o yace ya d'auketa su wuce kawai, duk k'arshen sati Abdulrahim na zuwa duba iyayensa, idan Asma'u bata zo ya zama abun zagi idan taho ma aci Mata mutunci.

Abdulrahim arziki sai bud'ewa yake tana ganin haske saboda biyayyar iyaye da yake, ga kulawa da iyalinsa da yakeyi, har Saudiya ya biyama Ard'o da Iya Hari, amma Iya cewa tayi ya bata kud'in kawai (hasararriya Mara rabo) Ard'o kam ya k'ara tsorata da lamarin Hari, haka ta kashe su a banza.

~~~~~~~~~~

B'angaren Ameena da Yusuf kuma zaman su lafia lau gwanin sha'awa, kowa na kaffa,-kaffa da d'an uwansa, tare suka kowa makaranta inda take karantar Botany (ilimin tsirrai) sam rashin haihuwar bai tab'a dagama Yusuf hankali ba, shine ma mai kwantar Mata da hankali, idan tana nuna damuwarta, yace "haihuwa ta Allah ce idan sunada rabo zasu samu idan babu Abdool ya ishesu".

Suna shekara 4 da aure ta samu ciki, murna sosai sukayi da kyautar da Allah yayi musu, wata tara cip ta sunbulo 'yarta mai kama da Yusuf sak, a Besse suka koma akayi suna inda yarinya taci sunan mamar Yusuf Aisha suna kiranta Nihal, mutane Argungu anzo an kwashi shoki!

Musamman Abdool daya zama dan samari sai murna yaks yayi k'anwa.........

*lol every body a kame kam sabuwar rawa 🕴🏾🕴🏾🕴🏾🕴🏾*

_kuyi hak'uri Dani friends abubuwan ne da yawa #one love# 😍_

💄Meryerm Abdool💄

👌🏻😉
[8/16, 8:27 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

```Manzon Allah (S.A.W) yace ma wani yaro:- kayi bismillah(idan zakaci abinci) kaci da hanun damanka, kaci daga abinda ke gabanka.```

_Ladubba ne nacin abinci mu kiyaye sannan mu koyar da yaranmu_ Allah yasa mudace🙏🏻

*Ina mai farinciki da wannan Auren da kikayi Aunty Kausar (kausar M Hasan) Allah ya sanyawa aurenki Albarka tare da zuria dayyiba Ameen #HML💏*

_Ina mik'a ta'aziyya ga Feedo Deedo (marubuciyar mamata gimbiyata) akan rashin mahaifiyarta da tayi, Allah yayi mata rahama yasa mutuwa hutuce ameen, Ku kuma Allah ya Baku hak'urin rashin da kukayi👏🏽_

📝 *Episode* 131-135

Bayan sunyi Arba'in sukaje Argungu ganin gida da kai musu jaririyar su gani, lokacin da Ameena ta shiga d'akin su, nan taga wasu kayan Asma'u wad'anda ba'a kyautar ba, batasan lokacin da hawaye ya wanke mata fuska cikin jimami take magana "Asma'u kina ina? Tsawon shekara biyar kenan, Asma'u kina lafia kuwa? Kina cikin farinciki ko sab'anin haka, Asma'u kizo gida mu ganki wlh Baba Neman ki yake ruwa a jallo, pls Husnatah sisto na friend dita ever kizo garemu muma buk'atar ki" cikin kuka tace maganar gwanin tausayi, kullum safiyar duniya kira gida maganarta kenan Asma'u tazo, Mama dake tsaye bakin k'ofa rik'e da Nihal dake motsi alaman yunwa dan tunda suka zo take sharar bacci abinta, Abdool na kusa da ita sai kallon ta yake ya tab'a nan ya tab'a can yana matuk'ar son k'anwar tasa, ko yanzun ma Baba ne ya kirashi suka fita.

Itama hawaye take daga nan tsaye, ita ta haifesu gaba d'aya, amma tasan akwai shakuwa mai girma a tsakaninsu sau da yawa idan matsala ta taso a tsakaninsu suke maganceta ba tare da ta sani, saidai idan tafi k'arfin su suka kawo mata, to ya zasuyi k'addara ta riga fata, saidai su bita Addu'a Allah ya k'are ta aduk inda take ya dawo musu da ita lafia, share hawaye tayi kada ta rauna nata.

K'arasawa tayi ciki tare da kamata zuwa bakin gado, cikin muryan rarrashi da tace "Ameena kuka bazai dawo da Asma'u ba, Addu'ar mu kawai take nema, kiyi hak'uri ki daure ki daina kuka kiyi mata Addu'a" haka tayi ta rarrashinta daga k'arshe ta bata 'yarta data fara kuka tare da ficewa cikin sanyi, dan ganin Ameenan kad'ai tuna mata da Asma'unta yake yi.

*****************

Satinsu d'aya a Argungu sun zaga dangi sosai har birnin lafia sunje, gidan Firdausi duk taje, Abdool kuwa kullum yana rik'e da Nihal har goyata yakeyi Mama tayita zolayarsa, da sunan mati sai cewa yake ai k'anwarsa CE, a satin Yusuf yazo nan ya dage da rokon Baba ya basu Abdool su wuce dashi tunda ya k'are primary, ganin sun dage kuma yaga shima yaron yana buk'atar uwarsa a kusa dashi duk da suma ba abinda basa yi masa amma d'a sai uwarsa, kuma ya yaba yadda Yusuf d'in ya nuna kulawarsa akansa, yanada tabbacin zai rik'e sa da Amana, amma duk da haka saida ya kira Alhaji Sada ya shaida masa abin da sukazo dashi.

Kai tsaye Alhaji ya amince dan yasan waye Ameena yasan zata bashi tarbiyar da ya dace, shi kanshi yaron zaifi jin dad'i gashi ga uwarsa, nan Baba ya basu Abdool sunyi murna Sosai bakin Yusuf ya kasa rufuwa danshi harga Allah yana son Abdool yana jinshi a ranshi kamar yadda yakejin Nihal.

Ban kwana sukayi ma Argungu garin nabame kowa sarki, sannan suka wuce Besse anan ma sam dangin Yusuf basu nunawa Abdool wata fuska k'ama ko wulak'anci ba, Wanda hakan yayima Ameena dad'i sosai, daganan suka shirya tsaf suka lula Kaduna.....

Zamansu kaduna zamane mai cike da k'auna da kulawa da yaran su sosai Yusuf ke kula da Abdool kaman ma yafi sonsa akan Nihal, dan Ameena cewa take Nihal ce babynta shi kuma yaron Dady, tare suka zuwa masjeed kullum muddin yana gida, haka zai baje a parlour yana mishi lesson don tuni suka sakashi secondary wata private, muddin Yusuf na gida to yana tare da Abdool hakan ba k'aramin dad'i yakewa Ameena ba, hakan ya k'ara wanzar da zaman lafia a familyn.

Sannu a hankali rayuwa taci gaba da shurawa kwanaki na tafiya, Nihal nada four years Ameena ta k'ara haihuwa wannan karon twins ta haifa mace da namiji, nan Ameena ta roki Akan a sakama macen sunan Asma'u hakan kuwa akayi inda ake kiranta da Husna namijin kuwa Abduljabbar, zuwa yanzu Yusuf ya gina musu gidan Kansu a unguwar K/mashi inda Ameena ta k'awata gidan da kalolin furanni masu dad'in k'amshi ga kuma garden had'adde Wanda ya k'unshi kayan more rayuwa, kai da ka taho gidan ba tambaya kasan ka taho gidan miss Botany tun farfajiyar gidan zaka fahimci haka.
Chapter 21 · 0% Book details