Sashe 50
Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Malam dan Allah tsaya" Kalmar da ta doki kunnensa kenan, dan tabbatar da dashi ake ya juyo.
Tozali da mutumin da yafi tsana a rayuwa wanda yayi silar tafiyar farincikinsa ya dasa masa bak'in ciki a rayuwa ne yasa ya tunkaro gurin sa gadan gadan fuskar nan kamar ta zaki, itama yarinyar ganin meke faruwa ne yasa ta saki jakar tare da bin bayan mutumin tana fad'in "Abi" dayin wani yare Wanda na fahimci larabcine.
Ko saurarenta baiyi ba ya isa ga mutumin tare da cafkar wuyar sa yana huci baiyi duba da halin nakasa da yake ciki ba.
Wawuyar matsa yayi ma mutumin a wuya tuni idanunsa suka firfito waje sunyi jajir sai kakari yake "saina kasheka azzalumi macuci mai raba sunnar manzo" shine Kalmar da ke fitowa daga bakinsa, shikam sai mutsu-mutsun kwantar kansa yake amma ina ko gezau bai ba.
Kuka yarinyar ta fashe dashi tana Jan hannun mahaifin nata "Aa Abi kada ka illatashi meyayi maka Abi ka barshi" tace fad'a Cikin kuka.
Sakinsa yayi da k'arfi tare da tura sa baya, Allah ya soshi badan kukan 'yarsa da yake matukar so ba da ba zai bar wannan azzalumin ba sai ya illatashi koya kasheshi, mugun kallo kawai yake binsa dashi.
Gurgun sai Sosa wuyar sa yake dayaji shaka ajali dak'yar ya daga keken ya sake hawa yace "na cancanci koma meye daga gareka amma dan Allah ka d'aure ka saurareni" yace, still da kallon yake binsa ba tare daya ce uffan ba.
"Nasan na zalince Ku kuma na dad'e ina Neman inda zan ganka na nemi gafararka kona samu sauk'in wannan bala'i da nike ciki, ba kai kad'ai na jefa a irin wannan halin ba hasalima Sana'a tace in bata aure a biyani, kaima ba haka kawai nayi maka haka sakani akayi inyi..."katsesa yayi da cewa "gayamin wane marar imani ne ya sakaka yimin wannan danyen aiki?"
Zaiyi magana sai wata mota ta tsaya a gabansu da mamaki na cikin motar ya fito baki bud'e ya nuna shi da yatsa baki na rawa yace "Auwal!"......
_gatan da zakuyimin d'aya ne masoyana ku nema min gafarar ubangiji dani daku gaba d'aya ya yafe mana kurakurai mu dan rahamarsa👏🏽_
💄Meryerm Abdool💄
[10/20, 5:27 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Real Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*#[email protected]*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*
```An karb'o daga ka'abi d'an Iyadi (R.D) yace" Manzon Allah (S.A.W) yace "kowace Al'umma tana da fitinar ta, fitinar al'umma shine dukiya```
Sahihuh(hakkun mubeen)
*ya Allah kada ka jarabcemu da dukiyar da zata zamo fitina a garemu* 👏🏽
😍 _kun nunan cewa ko bani media kunayi dani, kun nunan ni yar gata ce a gareku💕 Ku sani Meryerm Abdool ma tana sonku sosai iya wuya ana irin mugun taren nan har abada🤝 Hafsat mai Sharif, Raheenat Mahmoud, Maryam Y Zango #ILVYSM 4rm d higher rank of my ❤#_
📝 *Episode* 261--265
"Yaya Rabi'u" shima ya fad'a yana kallon sa, k'arasowa Rabi'u yayi "Auwal dama kana raye a duniyar nan ka gujemu? Haba Auwal wannan wane irin hukunci ne kayi mana akan laifin da bamu aikata ba, haba Auwal! Haba! Yanzu dai mu shiga ciki wad'annan fa?" Ya nuna gurgun da yarinyar.
"Mu shiga ciki Yaya zakuji bayanin komai" tura gurgun Rabi'u yayi suka shiga ciki, direct part d'in Alhaji suka nufa, yana zaune kamar kullum kan kujerarsa carbi a hannun sa yana ja, sallama Rabi'u yayi tare da shiga.
Kasa k'ara sa amsa sallamar Alhaji yayi tare da mik'ewa tsaye yana nuna Auwal da yatsa cikin inna inna yace "Au..Auwalu kaine ko dai gizau kakemin kamar yadda ka saba"
Gabansa Auwal ya isa tare da sakin kuka "nine dai Auwalun ka Baba, dan Allah Baba ka gafarceni nasan nayi ba dai2 ba dan Allah kayimin afuwa Baba" yace cikin kuka tare da kama k'afafunsa.
"Alamdulillahillazih bi ni'imatih tatimmus salihat" shine Kalmar da Alhaji Sada keta maimaita wa, d'ago shi yayi tare da rungume shi tsam wani sanyi da rahama ce ta ratsa su irin ta uba da d'a, Rabi'u dake gefe sai murmushi yake, shikam gurgun sai kwalla yake yana kaico da rayuwar sa duk shine silar nisantar su, yarinyar kuwa sai kallon tsohon take ba tambaya tasan shine kakanta.
"Rabi'u kaje kayi sanarwar metting na gaggawa yanzu" Alhaji Sada ya fad'a.
Hajia Kaltume ce ta fara isowa parlon suman tsaye tayi tare da zaro ido tana nuna Auwal ta k'asa magana, duk Wanda ya shigo indai yasan Auwal turus yakeyi dan sun dad'e da cire tsammanin sake ganinsa, Maryam ma suna gari sunzo hakan yasa itama ta halarci taron da nata iyalan, wad'anda basu sanshi ba sai a labari duk dai sun ganshi wasu sun ganesa wasu kan basu gane ba, Rafi'a ce ta shigo last dan bata gida tana gurin shashancinta saida Rabi'u ya matsa sannan tazo, ganin Auwal bai wani d'aga mata hankali ba, sai bayan ta zauna idonta suka sauka akan gurgun, ki tayi kamar ta saki fitsari a gurin tsabar tsoro zaro ido tayi tuni ta fara gumi duk da sanyin Ac dake parlon, Ji take kamar ta zura a guje saidai ba damar haka.
Bayan an nutsu kowa ya hallara Alhaji yasa aka bud'e taro da Addu'a, sannan ya fara jawabi kamar haka "kamar yadda muka sani munyi rashi na d'aya daga Cikin 'ya'yan gidan nan tsawon shekaru 29 da suka wuce, wasu daga cikinmu sun sanshi wasu kuma basu sanshi ba sai a labari Wanda har mun cire rai da ganinsa, to Alhamdulillah a yau Allah Cikin ikonsa da ganin damarsa ya dawo mana da Auwalu cikin mu, Alhamdulillah Allah mun gode maka da wannan ni'imar da kayi mana ba tare da k'arfi ko dabarar mu ba" nan hayaniya ta tashi kowa yana fad'in Kalmar nuna farincikinsa game da dawowar Auwal, saida aka gama aka sake nutsuwa Alhaji yaci gaba.
"Kuma kowa nada labarin abinda ya faru dalilin da yasa Auwal ya tafi ya barmu duk da agaremu bai isa dalili akan tafiyarsa ba to shima dai ya gane bai kyauta ba ya kuma nemi afuwa akan hakan munsan wannan bazai wuce sharrin zuciya da shed'an ba, to kuma duk a lokaci d'aya Allah ya kawo mana warwara a cikin wannan lamarin ga Wanda ya zamo silar sabani tsakanin Auwal da Ameena yana ikirari da bakinsa sharri yayi ma Ameena sannan yace saka shi akayi dan haka waka a bakin mai ita tafi dad'i sai a bashi dama yayi mana bayani"
Nan fa kallo ya koma ga wannan gurgun kowa na jiran jin mai zai fad'a.
"Nidai sunana Saminu amma anfi sanina da Shago kashe aure, na samo wannan suna ne a dalilin sana'ata ta kashe aure duk yanda Aure yake muddin akazo gurina akace ana buk'atar mutuwarsa to zan kashesa muddin zan samu kud'i wannan itace Sana'a ta, na kashe aure Wanda ni kaina bansan adadin auren da na kashe ba, a haka ne waccen ta sameni tace zanyi mata aiki" ya nuna Rafia tare da koro musu bayani yadda sukayi da ita da yadda suka tsara komai har zuwa abinda ta bashi.
"Kai munafuki yaushe na tab'a ganinka ni bamma tab'a saninka a rayuwa ba, ni zakayiwa sharri" tashi tayi tana bobbotai da borin kunya, ba Wanda yace uffan sai ido da aka zuba mata, murmushi yayi "dama nasan za'ayi haka shiyasa na tanaji irin wannan ga duk Wanda nayiwa aiki" nan take ya danna wata mp sai muryanta Radau da yadda suka shirya komai.
Tass...kakeji hajia Kaltume ta wanke mata fuska da mari masu kyau "amma dai ke anyi tsinanniya, munafuka yanzu duk yanda na d'auke ki Ashe ke kurace da fuskar akuya kika nasa aka saki 'yar mutane, kikayi silar tafiyar d'ana da nake matuk'ar so, er banza Allah ya isa tsakanina dake" hajia Kaltume tace cikin kuka.
"Aa Kaltume mi a laifin Rafia bayan ke kika bata k'ofa da baki nuna k'iyayyar ki ga Ameena ba ya za'ayi Rafia ta samu hanyar yi musu wannan ta'adi ba, duk da bamu San hujjarta nayin hakan ba" Alhaji Sada yace, sanyi jikin Hajia Kaltume yayi tabbas tayi kuskure a baya na nuna tsanarta a fili ga talaka, amma tuni ta gane gaskiya dan miyagun halayen da Rafia ta b'ullo dasu na rashin tarbiya da musgunawa kowa na gidan, saidai ta riga ta makaro dan Alhaji ya fita batunta akan maganar Abdool da mahaifiyar sa baya fad'a mata komai game dasu gashi ya hana Abdool zuwa gaba d'aya.
Rafia sai raba ido take tana kyarma nan Rabi'u ya daka mata tsawa "meye dalilinki na wannan badak'alar?"
Cikin inna-inna da tsananin tsoro ta shiga gaya musu akan tana son ya auri k'anwarta ne sannan ta tsani Ameena saboda yanda Auwal ke nuna mata k'auna.... Ai bata k'ara sa bayani ba sai saukar naushi taji a baki, tare da rufeta da duka duk jikinta, sai ihu take zundumawa "Auwallu me kakeyi haka ka dawo hankalinka fa tsaketa" Alhaji yace cikin daga murya, saketa Auwal yayi tare da kama gefe yana huci "Alhaji daka barshi ya illata annoba guba, kije na sakeki saki uku kuma Allah ya isa da cutar damu da kikayi" Rabi'u yace.
"Kayimin dai2 Rabi'u" hajia Kaltume tace, hannu Rafia ta aza a ka tare da fashewa da kuka hadda ihunta dan tasan karyar ta ta gama k'arewa "dalla Malama fice mana a gida ko yanzu in karyaki anan" Sani yace yana binta da mugun kallo, dakar taja kafarta dan ba k'aramin duka tasha a hannun Auwal ba ga bakin ta daya fasa mata sai jini yake, nan fa kowa ya hau murna sun rabu da wahala dan a gidan ta addabi kowa, kowa sai fad'ar albarkacin bakinsa yakeyi, shidai Alhaji sai kallon su yakeyi, shiru ya biyo baya "Rabi'u me yasa ka yanke irin wannan hukuncin da Allah bayaso kai tsaye?"
Tozali da mutumin da yafi tsana a rayuwa wanda yayi silar tafiyar farincikinsa ya dasa masa bak'in ciki a rayuwa ne yasa ya tunkaro gurin sa gadan gadan fuskar nan kamar ta zaki, itama yarinyar ganin meke faruwa ne yasa ta saki jakar tare da bin bayan mutumin tana fad'in "Abi" dayin wani yare Wanda na fahimci larabcine.
Ko saurarenta baiyi ba ya isa ga mutumin tare da cafkar wuyar sa yana huci baiyi duba da halin nakasa da yake ciki ba.
Wawuyar matsa yayi ma mutumin a wuya tuni idanunsa suka firfito waje sunyi jajir sai kakari yake "saina kasheka azzalumi macuci mai raba sunnar manzo" shine Kalmar da ke fitowa daga bakinsa, shikam sai mutsu-mutsun kwantar kansa yake amma ina ko gezau bai ba.
Kuka yarinyar ta fashe dashi tana Jan hannun mahaifin nata "Aa Abi kada ka illatashi meyayi maka Abi ka barshi" tace fad'a Cikin kuka.
Sakinsa yayi da k'arfi tare da tura sa baya, Allah ya soshi badan kukan 'yarsa da yake matukar so ba da ba zai bar wannan azzalumin ba sai ya illatashi koya kasheshi, mugun kallo kawai yake binsa dashi.
Gurgun sai Sosa wuyar sa yake dayaji shaka ajali dak'yar ya daga keken ya sake hawa yace "na cancanci koma meye daga gareka amma dan Allah ka d'aure ka saurareni" yace, still da kallon yake binsa ba tare daya ce uffan ba.
"Nasan na zalince Ku kuma na dad'e ina Neman inda zan ganka na nemi gafararka kona samu sauk'in wannan bala'i da nike ciki, ba kai kad'ai na jefa a irin wannan halin ba hasalima Sana'a tace in bata aure a biyani, kaima ba haka kawai nayi maka haka sakani akayi inyi..."katsesa yayi da cewa "gayamin wane marar imani ne ya sakaka yimin wannan danyen aiki?"
Zaiyi magana sai wata mota ta tsaya a gabansu da mamaki na cikin motar ya fito baki bud'e ya nuna shi da yatsa baki na rawa yace "Auwal!"......
_gatan da zakuyimin d'aya ne masoyana ku nema min gafarar ubangiji dani daku gaba d'aya ya yafe mana kurakurai mu dan rahamarsa👏🏽_
💄Meryerm Abdool💄
[10/20, 5:27 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Real Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
*#[email protected]*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*
```An karb'o daga ka'abi d'an Iyadi (R.D) yace" Manzon Allah (S.A.W) yace "kowace Al'umma tana da fitinar ta, fitinar al'umma shine dukiya```
Sahihuh(hakkun mubeen)
*ya Allah kada ka jarabcemu da dukiyar da zata zamo fitina a garemu* 👏🏽
😍 _kun nunan cewa ko bani media kunayi dani, kun nunan ni yar gata ce a gareku💕 Ku sani Meryerm Abdool ma tana sonku sosai iya wuya ana irin mugun taren nan har abada🤝 Hafsat mai Sharif, Raheenat Mahmoud, Maryam Y Zango #ILVYSM 4rm d higher rank of my ❤#_
📝 *Episode* 261--265
"Yaya Rabi'u" shima ya fad'a yana kallon sa, k'arasowa Rabi'u yayi "Auwal dama kana raye a duniyar nan ka gujemu? Haba Auwal wannan wane irin hukunci ne kayi mana akan laifin da bamu aikata ba, haba Auwal! Haba! Yanzu dai mu shiga ciki wad'annan fa?" Ya nuna gurgun da yarinyar.
"Mu shiga ciki Yaya zakuji bayanin komai" tura gurgun Rabi'u yayi suka shiga ciki, direct part d'in Alhaji suka nufa, yana zaune kamar kullum kan kujerarsa carbi a hannun sa yana ja, sallama Rabi'u yayi tare da shiga.
Kasa k'ara sa amsa sallamar Alhaji yayi tare da mik'ewa tsaye yana nuna Auwal da yatsa cikin inna inna yace "Au..Auwalu kaine ko dai gizau kakemin kamar yadda ka saba"
Gabansa Auwal ya isa tare da sakin kuka "nine dai Auwalun ka Baba, dan Allah Baba ka gafarceni nasan nayi ba dai2 ba dan Allah kayimin afuwa Baba" yace cikin kuka tare da kama k'afafunsa.
"Alamdulillahillazih bi ni'imatih tatimmus salihat" shine Kalmar da Alhaji Sada keta maimaita wa, d'ago shi yayi tare da rungume shi tsam wani sanyi da rahama ce ta ratsa su irin ta uba da d'a, Rabi'u dake gefe sai murmushi yake, shikam gurgun sai kwalla yake yana kaico da rayuwar sa duk shine silar nisantar su, yarinyar kuwa sai kallon tsohon take ba tambaya tasan shine kakanta.
"Rabi'u kaje kayi sanarwar metting na gaggawa yanzu" Alhaji Sada ya fad'a.
Hajia Kaltume ce ta fara isowa parlon suman tsaye tayi tare da zaro ido tana nuna Auwal ta k'asa magana, duk Wanda ya shigo indai yasan Auwal turus yakeyi dan sun dad'e da cire tsammanin sake ganinsa, Maryam ma suna gari sunzo hakan yasa itama ta halarci taron da nata iyalan, wad'anda basu sanshi ba sai a labari duk dai sun ganshi wasu sun ganesa wasu kan basu gane ba, Rafi'a ce ta shigo last dan bata gida tana gurin shashancinta saida Rabi'u ya matsa sannan tazo, ganin Auwal bai wani d'aga mata hankali ba, sai bayan ta zauna idonta suka sauka akan gurgun, ki tayi kamar ta saki fitsari a gurin tsabar tsoro zaro ido tayi tuni ta fara gumi duk da sanyin Ac dake parlon, Ji take kamar ta zura a guje saidai ba damar haka.
Bayan an nutsu kowa ya hallara Alhaji yasa aka bud'e taro da Addu'a, sannan ya fara jawabi kamar haka "kamar yadda muka sani munyi rashi na d'aya daga Cikin 'ya'yan gidan nan tsawon shekaru 29 da suka wuce, wasu daga cikinmu sun sanshi wasu kuma basu sanshi ba sai a labari Wanda har mun cire rai da ganinsa, to Alhamdulillah a yau Allah Cikin ikonsa da ganin damarsa ya dawo mana da Auwalu cikin mu, Alhamdulillah Allah mun gode maka da wannan ni'imar da kayi mana ba tare da k'arfi ko dabarar mu ba" nan hayaniya ta tashi kowa yana fad'in Kalmar nuna farincikinsa game da dawowar Auwal, saida aka gama aka sake nutsuwa Alhaji yaci gaba.
"Kuma kowa nada labarin abinda ya faru dalilin da yasa Auwal ya tafi ya barmu duk da agaremu bai isa dalili akan tafiyarsa ba to shima dai ya gane bai kyauta ba ya kuma nemi afuwa akan hakan munsan wannan bazai wuce sharrin zuciya da shed'an ba, to kuma duk a lokaci d'aya Allah ya kawo mana warwara a cikin wannan lamarin ga Wanda ya zamo silar sabani tsakanin Auwal da Ameena yana ikirari da bakinsa sharri yayi ma Ameena sannan yace saka shi akayi dan haka waka a bakin mai ita tafi dad'i sai a bashi dama yayi mana bayani"
Nan fa kallo ya koma ga wannan gurgun kowa na jiran jin mai zai fad'a.
"Nidai sunana Saminu amma anfi sanina da Shago kashe aure, na samo wannan suna ne a dalilin sana'ata ta kashe aure duk yanda Aure yake muddin akazo gurina akace ana buk'atar mutuwarsa to zan kashesa muddin zan samu kud'i wannan itace Sana'a ta, na kashe aure Wanda ni kaina bansan adadin auren da na kashe ba, a haka ne waccen ta sameni tace zanyi mata aiki" ya nuna Rafia tare da koro musu bayani yadda sukayi da ita da yadda suka tsara komai har zuwa abinda ta bashi.
"Kai munafuki yaushe na tab'a ganinka ni bamma tab'a saninka a rayuwa ba, ni zakayiwa sharri" tashi tayi tana bobbotai da borin kunya, ba Wanda yace uffan sai ido da aka zuba mata, murmushi yayi "dama nasan za'ayi haka shiyasa na tanaji irin wannan ga duk Wanda nayiwa aiki" nan take ya danna wata mp sai muryanta Radau da yadda suka shirya komai.
Tass...kakeji hajia Kaltume ta wanke mata fuska da mari masu kyau "amma dai ke anyi tsinanniya, munafuka yanzu duk yanda na d'auke ki Ashe ke kurace da fuskar akuya kika nasa aka saki 'yar mutane, kikayi silar tafiyar d'ana da nake matuk'ar so, er banza Allah ya isa tsakanina dake" hajia Kaltume tace cikin kuka.
"Aa Kaltume mi a laifin Rafia bayan ke kika bata k'ofa da baki nuna k'iyayyar ki ga Ameena ba ya za'ayi Rafia ta samu hanyar yi musu wannan ta'adi ba, duk da bamu San hujjarta nayin hakan ba" Alhaji Sada yace, sanyi jikin Hajia Kaltume yayi tabbas tayi kuskure a baya na nuna tsanarta a fili ga talaka, amma tuni ta gane gaskiya dan miyagun halayen da Rafia ta b'ullo dasu na rashin tarbiya da musgunawa kowa na gidan, saidai ta riga ta makaro dan Alhaji ya fita batunta akan maganar Abdool da mahaifiyar sa baya fad'a mata komai game dasu gashi ya hana Abdool zuwa gaba d'aya.
Rafia sai raba ido take tana kyarma nan Rabi'u ya daka mata tsawa "meye dalilinki na wannan badak'alar?"
Cikin inna-inna da tsananin tsoro ta shiga gaya musu akan tana son ya auri k'anwarta ne sannan ta tsani Ameena saboda yanda Auwal ke nuna mata k'auna.... Ai bata k'ara sa bayani ba sai saukar naushi taji a baki, tare da rufeta da duka duk jikinta, sai ihu take zundumawa "Auwallu me kakeyi haka ka dawo hankalinka fa tsaketa" Alhaji yace cikin daga murya, saketa Auwal yayi tare da kama gefe yana huci "Alhaji daka barshi ya illata annoba guba, kije na sakeki saki uku kuma Allah ya isa da cutar damu da kikayi" Rabi'u yace.
"Kayimin dai2 Rabi'u" hajia Kaltume tace, hannu Rafia ta aza a ka tare da fashewa da kuka hadda ihunta dan tasan karyar ta ta gama k'arewa "dalla Malama fice mana a gida ko yanzu in karyaki anan" Sani yace yana binta da mugun kallo, dakar taja kafarta dan ba k'aramin duka tasha a hannun Auwal ba ga bakin ta daya fasa mata sai jini yake, nan fa kowa ya hau murna sun rabu da wahala dan a gidan ta addabi kowa, kowa sai fad'ar albarkacin bakinsa yakeyi, shidai Alhaji sai kallon su yakeyi, shiru ya biyo baya "Rabi'u me yasa ka yanke irin wannan hukuncin da Allah bayaso kai tsaye?"