← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 53

Sashe 43

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saida yayi tsawon 30mnt yana addu'a, mik'ar da ita yayi sannan ya nad'e darduma tare da cire mata hijab da zanin ya ninke, gefen bed ya zaunar da ita sannan ya zauna shima, kama hannun ta yayi yace "nagode wa Allah daya nuna min wannan ranar da muka samu fahimta juna, zanyi marking nata cikin rana mai girma bayan first night namu, sannan nayi alk'awarin zan kula dake zan tarairayeka zan zamo hango abin jinginawarki zan kare mutuncinki zan rik'e amanar ki har abada, fatar zakiyi hak'uri dani da kuskurena idan nayi miki, ina mana fatar zaman lafia mai d'orewa".

Matse hannunsa tayi cikin nata " inshaa Allah zaka sameni mai biyayya a gareka, ta kowanne fanni zanyi iya k'ok'arina, Allah ya bamu Alkhairi mai dorewa a zamanmu"

Lumshe ido yayi wani dad'i na ratsashi yana feeling special, sannan yace "ameen uwargidana, one mnt" yace tare da mik'e wa yabar d'akin, plate ya dawo dashi a hannunsa, kayan cikine masu kyau a ciki da zafinsu sunji albasa, da tumatur da yaji sai k'amshi ke tashi, aiko d'iyar baffa tuni yawu ya tsinke, table ya janyo ya girke a gabanta tare da bud'e fridge d'inta ya d'auko fresh milk, stool din mirror ya janyo ya zaune yana fuskanta "bismilla" yace tare da d'aukar yanka d'aya zuwa bakinta, itama d'auka tayi ta bashi, a haka suka ciyar da juna cike da salon k'auna.

D'auke plate d'in yayi yakai kitchen ita kuma toilet ta shiga tayi brush, tare da hayewa kan bed, d'akin sa ya wuce yayi brush shima sannan ya dawo d'akin ta, kashe wutar yayi yabar deep one, sannan ya bita kan bed d'in, kusa da ita ya kwanta tare da leka fuskarta, likimo tayi yasani, murmushi yayi mai sauti tare da janyota zuwa jikinsa, anan suka shige wata duniya mai wuyar fassarawa romancing juna suke ba sassautawa duk da ranta fal tsoro, kasa daurewa tayi "pls yaya i'm scared kamin a sannu" Cikin kasalalliyar murya yace "feel free baby, ba zakiji zafi ba wannan Karon and zan biki a sannu ki saki jikinki kawai"....

***************

Tun daga ranar zaman lafia ya wanzu tsakaninsu, soyayya suke kamar su cinye juna, ga kulawa da tarairaya da take samu wurinsa kamar wata sarauniya, lallai a yanzu ta k'ara yadda da ba kowa a zuciyar Abdool sai ita natane ita kad'ai, komai tare sukeyi tun daga, kullum suna manne da juna suna soyewa, datayi d'an motsi kad'an " mene ne, meya faru, unborn ne ko" duk ya rikice yana tambayan ta, haka idan hospital yake yana mak'ale da waya suna hira har dawo gida, baya jin shakkar nuna mata soyayya a gaban kowa, ko gidan Mami sukaje bayajin kunyar nuna mata k'auna da tarairayar ta, sai ita yake bari da kunya.

Tuni suka dawo da junior gurin su Inda suke nan nan dashi, Ramlah kuwa ta had'a kiba abinta ta k'ara haske, Abdool sai tsokanarta yake wai ta zama Auntynsa yanzu tunda ta fishi kiba, had'e fuska take kamar yarinya inya tsokaneta, junior kuwa saidai yayi ta dariya yace Maa ta dawo yayinya.

*****************

Sanda Iya Hari ta farfad'o ba abinda take fad'i sai "kai mini rai Jauro karka kasheni" sai tambayan ta ake meya had'a ta da Jauro, meya kaita jeji amma ba amsa sai kuka take tana rokon Jauro yayi mata rai.

Tsawon watansu uku a asibiti sannan Ard'o yace a dawo gida tun da raunukan sunyi sauki ayi maganin kariyar na gargajia, abun tausayi iya Hari duk ta jeme ta lalace dama can ya muke muna 'yan sarki, kullum cikin kuka take tana fad'in a kira mata Ramlah, idan aka tambayeta me zata mata saidai tai ta kuka tana ita dai a kawo mata Laure, Hinde kuwa likkafa taci gaba dan yanzu tabar k'auyen gaba d'aya tabi wani saurayinta birni, wai iya Hari ta dameta da doyi a gida, da yake ba'ayi mata wanka saidai a goge mata jiki kawai Wanda shima Shatu CE keyi kullum tana gidan tun safe sai dare take komawa gidanta, da yake mijinta bai da matsala, Lanti kam sai tayi sati bata zo ba kuma ko zuwan tayi saidai ta kame gefe tana mata sannu ko Inda take bata zuwa wai d'oyi takeyi, kuma a dalilin ta tasa 'yarta ta gudu saboda azabar d'oyi.

Ard'o ma zuwa yanzu tausaya mata yake sosai ganin yadda duniya ta juye da ita (hmm duniya kenan tafi bagaruwa iya jima).

Gashi har yanzu tak'i fad'ar meya kaita jeji amma yafi kyautata zaton ba Alkhairi bane, ga shanunta ya Nema ya rasa anyi juyin duniya tak'i fad'in in da ta kaisu, kullum saidai kuka daga an tambayeta, yanaso yaje Kaduna yaga Ramlah saidai ciwon Hari ya hanashi tafiya gashi sai kashin kud'i ake amma kamar ana k'ara ma ciwon tak'i ne (to dama duniya imma shakiran ce ko imma kafura 🤷🏽‍♀) Allah yasa mudace......

Manage pls

_ina cikin damuwa ina Neman Addu'arku Friends😣_

💄Meryerm Abdool💄
[10/3, 10:53 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

*#[email protected]*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*

*_zuwa garemu writers, ban cire kaina ba, tambayace dani shin meyasa muke rubutu? Saboda samun fans masu zugamu suna cewa muci gaba da fire zasu bimu da fetur ko kuwa munayi ne saboda gyara? Bansan abinda ke ranku ba, amma abin da na sani shine kowace kalma da muka rubuta wallahi zamuyi bayani akanta a gaban ubangijinmu gobe k'iyama, shin muna tunanin idan muka doge da yadda muke rubutu a yanzu all about romancing sex, zamu tsira kuwa? Zamu iya hujja da rubutun mu gaban mahaliccin mu? As an advice we ar not too late even now, muyi k'ok'ari mu gyara mu, nidake dasu ana sabawa ubangiji dare da rana shi kuma mai gafara ne dare da rana muddin bawa yayi tuba mai kyau, so mu taimaki kanmu muyi amfani da basirar mu ta hanyar ceton al'umma daga wata musiba ba tsunduma su a ciki ba, idan har nayi/kikayi rubutu mai amfani koda mutum daya ya karanta ya amfana dake yafi mu rubuta barna mutum dubu su yaba mana, Wanda yabon iya Inda mukayi ne shikenan, ita kuwa azabar Allah tana can tana jiranmu a madakata, Allah yasa mu gane🤦🏽‍♀banyi dan cin zarafi ga kowa ba, duka nace so wacce ta tsargu ita taso ba ruwana.🙅🏿_*

*_oh!🤦🏽‍♀ Readers kuma ga naku....meyesa kuke son halaka kanku Ku halaka wasu gaba d'aya, without u impossible, saboda Ku ake rubutun nan, amma abin haushi yanzu idan novel ba bad'ala ba wacce zata cigiyesa amma idan ana batsa to yanzu kunyi chaa akansa kuna nema ko meye amfanin haka? Bansan meke ranku ba, amma abinda na sani shine kuna da babban kamisho a halakar writer, a duk lokacin da kuka an rubuta barna kuya kamata kuyi zanga-zanga ku kauracewa littafin Ku nuna anyi ba dai2 ba, amma ina bakwayi saidai ma Ku k'ara zuga writer d'in kuna fashemata kai kuna nuna mata masu gayamata gaskiya hasada suke mata, ko meye abin hasada a cikin rubutu na online Wanda ba riba a ciki, ribar d'aya idan ka rubuta abinda wani ya amfana ka samu lada that all fa🙅🏿 wanda muke zuwa neman lada mu tashi da zunubi, wallahi Readers kuji tsoron Allah Ku sani yana kallon mu, mu duka damu daku, kuma akwai ranar had'uwarmu dashi, so better mu tuba mu gyara, Allah yasa mudace ameen👏🏽_*

📝 *Episode* 231--235

Three months da tarewarsu lokacin cikinta na four months, aka fara bikin Nihal su Ramlah an dage sai hidima ake kullum gidan Mami take wuni sai dare Abdool ke d'aukar su, da sassafe kuma zai saukesu, kallo d'aya zakayi mata ka gane tana da ciki dan duk alamomin sun bayyana duk da bai fito ba ya boye a k'irji da hips, aiko tanashan tsiya gasu sadee wacce itama saura 2 months bikinta, Amal ma an saka mata rana ita da Ismail cousin d'in Abdool, "hmmm kuyi abinku ai dad'in ta dai duk kuna hanya kuma" sannan ta kalli Nihal "hehehe ke sisto kima daina biyesu dan saura k'iris ki jona ni" ta fad'a tana dariya harara Nihal ta aika mata ba tare datace komai ba, dan tunda satin bikin ya kama tasha jinin jikinta ganin rawan kan ya Hakeem ya sai k'aruwa yake.

Mutanen Besse dana Argungu duk sun iso, gida Mashaa Allah ya cika sai hidima akeyi.

Abdool ya taho d'ukarsu a parlour ya had'u dasu Inna "oh ni Habiba! Kaidai ka zama bita zai-zai to wuce yau ba inda zata" wani malalacin smiling yayi.

"Imma da abin yafi haka ki fad'a na yadda, amma ba abinda zai hanata tafiya yanzu" yace yana dialing no nata ganin bata gurin.

Turo baki tayi ganin kiran nasa, dariya Sadee tayi " 'yan matan gidan Dr majeed yadai" harara ta jefa mata tare da kai mata duka, dariya ta k'arayi harda kashe mata ido d'aya, Amal kuwa dafa tayi "manta su sisi jeki gani ko zai barki d'in" mayafinta ta Zara kawai tana fatar Allah yasa ya barta, dan tanaso sukai k'arshen shirye-shiryen Friends day da zasuyi gobe, gashi suna tsaka da tad'i ya k'atse su.

Bata bi takan Inna dake mata tsiya ba wucewa tayi abinta harabar gidan, saman motar ta hango shi shida Junior, suna firansu, tana isowa ya diro yana mata Murmushin nan nashi mai sanyi, mayar masa martani tayi tare da tambayansa office, ansawa yayi yana tambayan ta gajian hidima da unborn.

Bud'e mata murfin yayi kamar yadda ya saba saidai a maimakon ta shiga sai rik'e murfin tayi tana kallonsa da pity face "pls Yaya one favour?"

Ido ya zuba mata "oya said it all ears?"

"Um... dan Allah ka barmu mu kwana anan yau kaga bamu gama tsara event d'in gobe ba ka taho" junior jin me ta fad'a yasa yayi tsalle "Yawwa Maa nima inaso mu kwana gidan Mami"

Harara ya watsa ma Junior tuni yayi tsit sannan ya lafe a jikinta, ido kawai ya zuba mata baice komai ba,

"Pls Yaya yau d'aya, kafa junior ma naso"
Chapter 43 · 0% Book details