← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 53

Sashe 41

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Abdool ma daga bakin k'ofa ya dakatar da abokansa yace ba wani sayen baki da za'ayi kuma nasihar sun gode, nan suka kansa da zolaya da tsiya yace yadai ji.

D'akin sa ya fara shiga ya watsa ruwa tare da saka farar jalabiya, sannan ya nufi d'akin ta da ledoji a hannun sa, jin ba'a amsa sallamarsa ba, yasa ya shiga kawai dan yasan ko taji tana iya kin amsawa saboda haukanta.

Kwance take sai sauke numfashi take Cikin nutsuwa alaman tana enjoying baccin nata.

Tsaye yayi kanta tare da hard'e hannayensa a k'irji, kallon yake kamar yau ya fara ganinta, tayi masa wani irin kyau ji yake kamar ya shige jikin jikinta yai ta romance nata, lips d'inta ya kalla da suka kara jajar dasu ganin sha'awa, har ya sunkuya sai kai mata kiss sai kuma ya fasa kada ya tasheta ya katse mata jin dad'i.

Ledojin ya aje kan d'an table dake gefen gadon tare da wuce wa, har ya kai k'ofa, ya tuna kila fa bataci komai ba, kitchen ya wuce ya d'auko plate da cup ya dawo, naman ya juye Wanda yasha kayan vegetable sai tururi yake, sannan ya tsiya ya mata juice d'in ya ije.

Gefen gadon ya zauna tare shafo fuskarta a hankali, motsi ta faraji jin ana Shafa ta ne yasa ta ware idonta tare da sauke su a kansa, tsuke fuskarta tayi, shima fuskarsa ba yabo ba fallasa yace.

"Tashi ga abinci nan ciki nasan da wuya idan kinci wani Abu, and banaso ana barmin baby na da junwa" yana gama fad'i ya tashi ya fice.

Da harara ta rakasa, tare da jan tsaki, nan idanunta sukayi tozali da plate d'in, wani yawu ta had'iye, Cikin yayi k'ugi jikinta har b'ari yake, abunka ga mai yaron ciki, da sauri ta sauko ta d'auki plate d'in ta baje k'asa ta shiga d'ibarsa........

_kowa yace shine tofa ba shine ba_ 🙄

💄Meryerm Abdool💄
[9/27, 8:01 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

*#[email protected]*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*

*_Annabi Muhammad S.A.W yana cewa "Ku kasance masu yawan tunawa da mai yanke jin dad'in rayuwa, mai rabaka da masoyinka da mahaifanka, kai dama duniya gaba d'aya wato MUTUWA. Yar uwa nidake dasu anya muna tunawa da ita a kowace rana? Muna sane da tana nan tana bibiyarmu ba makawa ba gudu ba tsira? To idan hakane mai muka tanadar ma wannan doguwar tafiya? Wane guzuri muke dashi a wannan tafiyar? Mu dage don lahira anan duniya ake nemanta, kuma mutuwa bata bada alert zuwa take bagatatan koka shirya ko baka shirya ba!🤷🏽‍♀ Allah ya bamu kyakkyawan k'arshe dan alfarmar rasulillah S.A.W_* 👏🏽👏🏽

Kud'in na daban ne a gareni

```Maryam Y Zango(Wanda yayi nisa)
Raheenat Mahmoud(meye hujjarki)
Fareedat sweery (yar sarki) muna zuba👀
Fashuna
Salma Queen(momma)

Daduk sauran member of pure moment, Ku sani kuna wuta fa, kufa unique ne, just keep d fire burning #ana tare iya wuya#💋💋❤```

📝 *Episode* 221--225

Kiran farko na Asuba akan kunnenta, dama bata da nauyin bacci, ga kuma training d'in Iya Hari, a daddafe tayi alwala, dan da muguwar yunwa ta tashi jikinta har rawa yake kamar wacce tayi sati bata ci ba, har mamakin mugun cin nata take daya sameta a 2days d'in nan.

Koda Abdool ya shigo dan tayar da ita a dadduma ya sameta tana raka'atanil fajr, gaggauta fita yayi jin ana shirin tada sallah.

Tana kammala wa ko addu'ar kirki batayi ba, ta kwab'e hijab d'in tare da janyo sauran kazar data rage, ba maganan d'umamawa haka tahau ci, saida ta cinye tas, ta kora da juice d'in, ta dad'a da hollandia sannan taji dai2, ajiyar zuciya tayi kana ta d'auki Qur'an ta shiga karantawa.

K'arfe 6:00am ta gama karatun da azkar nata, mik'ewa tayi tare da d'aukar plate takai kitchen, wankesu tayi sannan ta share ko'ina tare da mopping, turare tayi nan take gidan ya d'au seti da k'amshi, to renon Iya Hari ce ba kyuya tana ganin ta cutar da ita, batasan taimakon ta tayi ba.

Saidai jin tayi turaren na haye mata kai, Allah yasa iya parlour ta saka bada bedrooms ba, d'akin ta ta shige tana toshe hanci ga zuciyarta sai tashi take kamar zatayi amai, aiko saida tayi sannan ta samu sassauci, saida ta dad'e zaune kafin ta iya gyara jikinta da wanka gaba d'aya.

Bayan ta gama shafe-shafenta, sip ta bud'e Tun k'asa har sama duk English wears tsaki taja tare da rufewa "nice zan K'ara saka wad'annan? God forbid" (d'iyar Baffa an tuba) lol.

D'ayan gefen ta bud'e nan taga su atampha, less, shadda da materials, wata super ta ciro blue and yellow, riga da siket ne ya zauna daram, tasan gun telansu akayi dama shike kai musu dinkin, bata d'aura d'an kwali ba, sarka ta saka 'yar simple me kyau, perfume ta d'auko dan fesawa tun kan ta fesa taji ya fara hau mata kai, dafe kai tayi tare aje turaren, hollandia ta k'ara sha sannan tasha maganin ta, da Mami tayi mata gargadi kula da shansa, bed ta koma tana game daga nan bacci yayi gaba da ita.

Saida gari yayi haske sannan ya dawo daga masjeed, direct d'akin sa ya wuce saboda a gajiye yake, duk kwanakin sunata hada-hada bai samun issheshen bacci, kwanciyar sa keda wuya bacci yayi gaba dashi shima mai cike da mafarkin 'yar rigimar tasa suna soyewa.....

**************

10:00am

Knocking ne ya tayar dashi, jiki a mace ya isa tare da tambayan waye, Nihal data shaka Dan sun dad'e wurin suna Knocking, jin muryan yayanta yasa ta waye tare da fad'in "mune" bud'e musu yayi sannan ya basu hanya, junior kuwa sai mak'ale sa yayi shi kuma ya daga shi sama suna dariya, gaidashi sukayi sannan suka aje basket d'in abincin akan dinning suna tambayan Ramlah.

"Tana ciki, and ki zubo min abincin nan, ki kawomin a d'aki" yace ma Nihal yana wucewa tare da junior.

"Kai waya gayamiki Amarya na baccin safe" Nihal tace tana Kai mata dun du a baya.

Bud'e ido tayi cike da masifa, sai taga ba Wanda take tunani bane, dariya suka sa mata Nihal da Amal, dan zaro ido tayi " yaushe kuka zo?"

"Ina zaki sani kuwa kina nan kina bacci, keda ya kamata ace kina parlour kina jiran isowar mu" Amal ta fad'a tana harara ta.

Dariya tayi "um kinga fa daga game ne, baccin ya sureni" tace tana sauke k'afafun ta k'asa, parlour suka wuce tana fad'in "me kuka zo mana dashi ni break fa ban had'a ba nayi baccin" d'an yunwa takeji sosai, dinning Nihal ta nuna mata tana mik'ewa zuwa kitchen dan d'auko plate dan zuba abincin da Abdool yace takai masa kada ta manta.

Gyara zama sukayi a parlon tare da jona kayan kallo, ganin Nihal ta d'auki hanya d'akin Abdool yasa tace "wai bani kika zubawa ba?" Harara ta balla mata "OK jirani nazo" tace tare da wucewa, dariya Amal tayi tace "um aunty barin zubo maki" ta mik'e zuwa kitchen...

Junior ne kad'ai kan sofa yana game da tab d'in Dadyn sa "son ina Dady?" Iya toilet " yace yana cikin bagwarar hausarsa, aje abincin tayi kan coffee table nashi, tana fad'in "wato ba zakaje Inda Maa dinka ba ko?" Tana k'ok'arin ficewa.

"Maa tana iya" ya fad'a yana aje tab d'in tare da biyota baya da gudu...

"Maa!" Ya fad'a da k'arfi, Ramlah dake zaune tana d'uri Amal sai dariya take mata, aje abincin tayi tana tare da ware hannu tana mishi murmushi.

"Son d'ina ni d'aya" ta fad'a bayan ya shige jikinta ta rungume sa "iyye yaron Maa ya kake"

Nan suka zauna sunata mata tsiya wai ba'asan Amarya da sakin ciki tana d'uri, jinsu kawai take, nan Sadee ta iso tare da wasu k'awayenta suka had'u sai tsiya suke mata, wai ta fad'a musu EDD dan kada ayi musu ba zata tunda anyi basu sani ba, banza tayi musu kamar bataji su ba, nan suka wuni har 6 sannan suka wuce bayan ta cikasu da kayan make up da English wears tare tace suje suyi ta sakawa itakam tayi retired sannan tace Sadee CE ta cuceta koma mai ya faru, dariya kawai suke mata, tace suyi dakyau yana zuwa Kansu, nan sukayi sallama da Amal dan gobe zasu koma, ba yadda batayi dasu su bar mata junior ba, sukace Aa sokoto za'aje dashi gobe tare dasu Amal, kuma ma Mami tace bata gama warwarewa ba balle ta iya d'aukar rigimarsa tadaiji da kanta..

Abdool kuma yana gama Karin ya shirya, ta k'ofar parlonsa ya wuce abinsa, bashi ya dawo ba sai after magrib, yau ma kazar ya k'ara kawo mata, saidai kowa jin k'amshi yake bamai kula wani.

Washe gari su Inna sukazo tare sukayi mata sallama, ta cikasu da tsaraba suma, sati Mami ta d'auka tana aiko musu abinci saida Ramlah ta tace ta daina kawo wa ta samu sauki zata iya yi sannan ta daina, komai tanayi a gidan kama da gyaran gidan, girki da sauran su, hadda maid Mami tace ta kawo mata tace aa, saidai ita da mai house d'inne kowa a sama magana ma sai a dole sukeyi, kowa d'akin sa yake kwana saidai hakan bai hanashi kula da duk wani motsinta ba,duk da zaman ba dad'i yake mishi ba dan gaskiya yayi missing nata d most, kusan kullum saita kira Amal ta had'a ta da junior sunyi waya, Inda hakan ba k'aramin dad'i yakewa iyayen Zee ba.

Ard'o ma suna waya akai akai, kullum maganar sa suna lafia dai ko to ta k'ara hak'uri yana nan zuwa....

****************

Wasa-wasa har sunyi month da tarewa ba wani ci gaba a zamansu shi yanaso yaga iya gudun ruwanta ne, itama zaman nasu na damunta dan kad'aici ba dad'i damar ta ma bata irin laulayin nan ci daine kamar gara, wayarta da kayan kallo ne abokan hirarta, anata ganin wulak'antata ne Abdool yayi saboda ya samu abinda yakeso daga gareta, bayan itace ta d'au zafi data ganshi zata wani d'aure fuska kamar taga abin k'i, amma kuma shi ta d'aura wa laifi.
Chapter 41 · 0% Book details