← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 53

Sashe 35

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Itace yau a tayi kara2 har ta kammala secondary, gashi ta samu ilimin da bata taba tunani ba, ware ido take ba Wanda takeson gani sama Ya Abdool tasan kome ta zama shine sila, aiko can ta hangosu zaune sai tafi suke musu idonsu ne ya had'u murmushi ya sarkar mata tare dayi mata jinjina da hannu, share hawaye tayi tare da sakar masa tattausan murmushi, ta matsu a sallamesu taje garesu ganin hadda Baffanta anzo dashi.

Haka akaci gaba da gudanar da program d'in akayi drama da wak'ok'i na bankwana sannan aka gabatar musu da gift d'insu, kusan sune suka an she gift d'in musamman ma ita, ana sallarmu da gudu ta isa runfar da suke zaune, haka ta shiga rungumesu suna tayata murna, Nihal haka, ita Sadee Inda Familyn ta ta dosa, jikin baffa tayi masauki, sai hawaye sharrrr.

Murmushi yayi "haba Ramlatuna yaufa ranar farinciki ne a gareki ba ranar kika ba, ko ke manta yaune burinki ya cika ne Ramlatuna"

Murmushi take cikin hawayen "baffa kukan farinciki ne wallahi, baffa Mami da ya Abdool sunyi komai a rayuwa, baffa suna matuk'ar k'auna ta".

" na sani Ramlatuna karamci a cikin jinin zuri'ar Asma'u yake, Allah ya saka musu da Alkhairi, ya biya musu buk'atunsa na Alkhairi "

"Ameen baffana"

Junior ta ansa a hannun Husna dake ta jillewa yana mik'a mata hannu yana kiran "Maa" dan haka yake ce mata.

"Oyoyo mai Son yaudai mun samu freedom zan rayu dakai ba kara tafia kaji Son" ta fad'a kamar mai magana da wani babba, shikam sai dariya yake mata yana jin dad'in ganinta da yayi, dan ya Santa kamar me.

Hakeem kam an kame gefe sai kallon k'asa -k'asa yakewa Nihal Wanda ita kad'ai ta gane yaren.............

_Thanks so much my sweet dota(Ramlah Abdallah mazoji) for d care, ur momma really appreciate_ 😍😘

*Nagode da addu'o'inku sisters am feeling better now thanks one again* 👌🏻👌🏻

💄Meryerm Abdool💄
[9/23, 8:51 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

Ga shafukan mu nan da zaku ringa samun k'ayatattun novel namu👇🏻

*#[email protected]*
*#IG PML WRITERS*
*#https://www.facebook.com/PML_-Writers-FANS-459256761123035*
*#http://maryamsbello.blogspot.com*

```🎂🎂🍰🍧🍬🍾may Allah Blessing and protect be wit u here and after, may ur birthday b d key 2 ur success in each and every step u go, may Allah bless ur remaining year wit his Rahma and barakat Ameen ```😍👌🏻

*happy birthday day*

*Namecy*

Maryam y Zango.💝💐

📝 *Episode* 196--200

Tun tana k'aramarta abokin yayan nata ke burgeta, bayan girmanta ne ta fahimci sonsa takeyi, amma a matsayin ta na 'yar bahaushe da kunya tace tana sonsa shiyasa tabar abin a ranta kowa bata fad'awa ba duk kuwa da surutu irin nata, Ubangiji kawai take gayama kukanta.

Shima Hakeem hakance a gurin sa ya dad'e yana k'aunar Nihal a ransa, duba da k'arancin shekarunta yasa ya b'oye a ransa kawai, a tunanin sa batasan meye soyayya ba, hakan yaci gaba da rainon sonta a ransa, koda Dr Majeed bai tab'a gayamasa ita yakeso ba, yace zai masa surprise.

Saidai tun can yana bata kulawa as a sister, saidai kulawar da yake bata daga baya is like more than a sister, har take tunanin kodai shima yanajin abinda take jine game dashi, Abdool baiyi noticing komai ba cos normally yasan Hakeem na kula da komai daya shafesa, kamar yadda shima yake kula da nasa, ita kam Ramlah tana shakkar wannan kulawar shiyasa da zancen saurayi ya tashi idan Nihal tace ita bata soyayya Ramlah ke cewa indai tayi wari saji, ita kanta Mami ta fara zargin wani abu a shakuwarsu inda take fatan hasashenta ya zama gaske, dan tasan Hakeem yaron kirki ne, iyayensa haka, zatayi farinciki idan ya zamo daga cikin zuriyarta.

Duk da bai furta kalmar so ga Nihal ba, amma yayi amfani da hikima ya koyar da ita k'aunarsa, baisan dama akwai k'aunar ba....

Kallon ta yake mai kice da ma'anoni Wanda ni kaina Meryerm bansan ma'anar ba, ita kuma sai sunne kai take tana murmushi.

Anan aka gabatar da jawabin bankwana, students sukayi bankwana da teachers nasu da juniors, nan aka rufe taro da addu'a, pics students suka shiga yi da k'awayensu da iyayensu, nan suka rabu kowa ta kama cike da kewar juna hadda koke-koke tare da ansan numbobin juna had'e da alk'awarin ziyartar juna.......

_School days kenan is d best days_

***************

A gida ma da aka dawo saida suka gabatar da kwarya-kwayar walima, Kyautar latest phones Abdool ya basu as his give, Samsung galaxy new version, had'e da sim tare da full credit na 5k, tare da Hakeem aka sayi phones d'in shine ya siya sims tare da credit yace tashi gudummuwar, hakan yayi ma Abdool dad'i sosai.

Tsabar dad'i tsalle Ramlah da daka tare da rungume yayan nata ita Nihal haka, tagal-tagal yayi zai fad'i da sauri Ramlah ta janyoshi tare da manna shi a k'irjinta, janye ta yayi daga jikinsa saboda yanayin da yaji mai wuyar fassarawa "Ramlah k'asa zaku Kaini kam?"

"Sorry sweet bro, duk murna ce fa"

Smiling yayi tare da wucewa yana fad'in "to ayi celebrate lafia, amma fa Ku kula sosai banda shiririta" Mami da Nany da Ard'o suka nunawa cikin farinciki, sunyi musu Ala sanya albarka Ard'o yace "to nima ga irin namu na k'auye".

Tsumi ne jarka d'aya, galon d'in zuma dana madara, da sauransu, shima rungumesa sukayi suna godiya, dama sun saba sha duk zuwan da zaiyi zaizo musu dashi, har Husna da Abduljabbar sha suke dan baida wata illa saima fa'ida, Mami kuwa tace su fad'i me sukeso ta basu as give, sukace is OK, ta barshi kawai but a duk da haka tace zatayi musu special gift.

Nan suka k'ure d'aki basu sha wahalar gane kan wayar ba tunda dama suna tab'a ta Mami da Abdool dama dai yace sai sun k'are school before su mallaki na Kansu, No d'insa data Mami ta baffa, data Hakeem ne a cikin sim d'in, Cikin zakuwa Nihal ta kira Hakeem don yi masa godiya.

Bayan sun gaisa " Yaya Nihal CE, munga abin Alkhairi mun gode sosai".

Smiling yayi "a murya na ganeki sweet sis, and meye na godiya 'yan matan Yaya Hakeem?"

Rufe ido tayi kamar tana gaban sa "uhm" kawai ta fad'a tare da saurin katse wayar, dariya ta bashi lumshe ido yayi tare da cewa "my shy girl".

" ke kuma keda waye hadda rufe ido" Ramlah ta fad'a idonta nakan phone d'inta da suke buga game ita da junior.

"Sa'idawa bansani ba" Nihal tace tana watsa mata harara.

"Hehehe A juri zuwa rafi dai...."

Harara ta watsa mata tare da shigewa toilet..

*************

Wasan rufe ido suke sai kuwwa suke kamar wasu yara duk sun hargitsa parlour, Ramlah ce aka daurewa ido wannan Karon, lalube take Wanda yayi dai2 da shigowar Abdool aiko kamar wacce aka tura ta fad'a a k'irjin sa, kamar da gayya ta k'ank'amesa tana fad'in "yarinya na kamaki" a tunanin ta Nihal ta kama, saukar masa kasala tayi gaba d'aya jikinsa, dama a gajiye ya dawo, ga azumi da yake faman yi yanzu kusan kullum, k'asa koda kwakwaran motsi yayi yana binta da kallo sanye da half gown peach anyi mata love shape da black, iya guiwa ta tsaya sai legging black data saka, ta kama Kanta da ribbon sannan ta saka bandana tayi masa kyau Kamar wata India, zameta daga jikinsa yayi karta karya masa azumi, jin shiru yasa ta janye d'aurin idon da niyyan yin masifa idonne ya sauka a nasa.

"Oyoyo Yaya, ina su Nihal d'in?" Tace tana raba idon ta gansu, tunda suka ga shigowarsa suka silale suka gudu dan ya hanasu kuwwace-kuwwace da mugun wasa.

Itama data ganshi ta razana amma da yake 'yar duniya ce saita maze, kallon ta kawai yayi ba tare da yace uffan ba ya wuce abinsa.

Ji tayi bata kyauta ba, hakan yasa ta bishi dan bashi hak'uri, kwance ta samesa rigingine yana kallon silin, bakin gadon taje tare da duk'awa "pls Yaya so sorry ba zamu k'ara ba" Sam baiji sallamarta da shigowarta ba dan yayi nisa a tunani muryanta ce ta dawo dashi.

Hannu yasa ba tare daya d'ago ba ya janyota zuwa jikinsa, gaba d'aya kan k'irjin sa ta zube kamar wata kayan wanki "meyasa kikeson azabtar dani Ramlah?" Taji ya jeho mata tambaya, sai raba ido take cikin tsoro jin yadda ya matseta a k'irjin sa dake harbawa da sauri-sauri, "Um..em..pls kayi hak'uri bazan k'ara ba" tace duk da batasan ainihin azabtarwar da take masa ba.

Ware ido yayi wad'anda sukayi jajir dasu, saida ta firgita da ganin yanayin sa, duk da idonsa ba farare amma wannan yafi karfin a kirasa kalarsu, duk ta tsure sai mutsu-mutsun kwace Kanta take, lumshe ido yayi tare dayin murmushi, ganin duk ta rikice a ransa yace "hmm sai tsoro amma ta iya jama mutum rigima, ashe ranar.... akwai rigima" sassauta rikon da yayi mata yayi aiko da sauri ta kwace kanta tare da sauka kan bed d'in sai sauke numfashi take tana raba ido.

Still idonsa a lumshe yace "meyasa kike irin wannan shigar?"

Shiru tayi masa, zaune ya mik'e tare dayin wani Smiling bayan ya ware idonsa a kanta, dariya ma ta basa ganin tayi tsuru kamar mara gaskiya "kinfison kiyita tayar min da hankali ko?"

Girgiza kai tayi alaman aa, "well jeki" yace aiko da gudu tabar d'akin kamar mai jiran kiris, dariya yayi "yauma na rasa azumin Kenan" yace tare dayin Mik'a rage kaya yayi sannan ya fad'a toilet dan yin fresh up.

"Ina Azabtar dashi.. To da meye?" Tace tana duba jikinta ita bataga laifin shigar ba, "yaya rigima yakeji, nidai gaskiya manyan kaya nauyin su nakeyi" ta fad'a tana tura baki gaba, kamar yana ganinta.

Jan k'afa tayi ta isa d'akin su Nihal ce kwance tana waya saidai baka iya jiyo abinda take fad'a saboda yanda tayi k'asa da voice nata, junior ne ke bacci gefenta, gadon ta haura tana fad'in "Juliet ta romeo ana baki aiki kenan, Yaya Hakeem yayi ya fito a shige ciki dake dan naga alamar a matse kuke" ta fad'a cike da zolaya.
Chapter 35 · 0% Book details