← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 53

Sashe 4

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Su Laure kam suna barin gurin sunyi nisa tace " Delu yau Allah ya cecemu da wanga d'an binni mai glass yakaimu inda 'yan sanda aida munci bone".

"Wallahi ko zuwan wannan mutumi ta cecemu".

"Hmmm amma kam dan binni nada kuddi har nonon jikka biyar"?

" Aida gani kilama shina kayinsu diba kigani sabuwa dal".

"Amma kam ban komawa ta hanyagga kar atai ya ganmu ya had'amu da 'yan sanda".

"E walla mubi ta waccen hanya".

Haka dai sukayita tattaunawa har suka isa kasuwa........

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^

Wasa-wasa tunanin yarinyar yayi tasiri a zuciyarsa shi yasa kullum daya gama aiki zai fito ya tsaya waje, amma ko mai kamarta bai tab'a bai gani, mamaki yakeyi meyasa ya damu da yaga yarinyar? Meyasa yake son sanin labarin yarinyar?

Ba Wanda zai ansa mishi amma tabbas zuciyarsa ta matsa mishi daya ganta yaji boyayyiyar damuwarta.......

*A garin kilgori...*

Kamar kullum Ardo tare da Amininsa Malam Garba ne zaune daf da magrib yana jiran Ramlah ta kawomusu ruwan Alwala, numfasashinsa ne yaji yana sassarfa kamar zai d'auke sai k'ok'arin janyosa yake.

Malam Garba da suke fira da Amininsa jin yayi shiru, yasa shi d'agowa ya kalleshi, ganin halin da yake ciki yasa ya tashi da sauri tare da kamashi yace.

" subhanallah Ardo ciwon ne ya tashi" duk ya rikice ana haka saiga Laure ta fito ganin halinda Baffanta ya yake, sakin buta tayi cikin kuka ta isa gareshi tana "wayyo Baffa, meya sameka Baffa" kan jikinsa ta kwanta tana kuka.

Jayeta Malam Garba yayi "ba kuka zakiyi ba Laure, jeki kiro Hari muje asibiti".

Da gudu ta shiga gidan "ke tambad'add'ya minana kika shigoma mutane uwa kamun hauka".

" Iya Baffa ....." Ta kasa magana sai nuna mata k'ofar gidan take.

Ganin taki magana taja tsaki "ko minana babu ruwana can ta matsemuku ke dashi" ta bud'e baki zatayi magana.

"B'acemin da gani sauna" ta fad'a cikin tsawar da ya firgitata a guje ta fita, koda ta fita har Malam Garba ya kira mashin ana shirin d'ora Ardo.

"Ina Harin"?

" tana zuwa" kawai ta fad'a D'ora shi yayi shima ya hau tare da cewa su samesu a can.

Aiko suna wucewa ta bisu da gudu tana kuka, d'an clinic ne garesu a garin, ba kuma likita sai nurse kawai, ganin yanayinsa yasa sukace a wuce dashi Yabo kawai.

Koda ta iso har an samo mota, an sakashi, ai bata jira jin komai ba ta fad'a ciki driver yaja........

_manage pls friends_ 👏🏽

💄 Meryerm Abdool 💄
[7/11, 4:04 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

```WASIYYAR LUKMATUL HAKEEM GA D'ANSA ITACE :-```

*Ya kai d'ana kada kayi shirka ga Allah(kada ka had'ashi da wani a gurin bauta) domin shirka itace mafi munin zalunci, ka zamo mai biyayya ga iyaye, domin neman dacewa duniya da lahira.*

*Yakai d'ana ka tsaida sallah, kayi hak'uri da abinda ya sameka, kada ka nemi biyan buk'atarka ga mutane, kada kayi tafiya a cikin k'asa kana mai alfari da tak'ama, domin ubangiji bayason mutane masu alfari da tak'ama.*

*ka zamo mai tafiya cikin nutsuwa, kada ka zamo mai d'aga sautinka a gurin magana domin mafi munin sauti shine sautin jaki.*( _suratul Lukman_)

_Allah sarki, mutum mai mutum mai hikima kenan, ni dah keh dasu wance mun tab'a tunanin yima 'ya'yanmu wasiyya, tofa musani 'ya'ya amanace kuma abin tambayawa ne gaban ubangiji ranar gobe k'iyama._

Allah yasa mudace👏🏽

📝 *Episode* 31--36

Suna isa aka k'arbesu I&E aka wuce dashi, haka Laure da Malam Garba suka bi gadon da aka d'orasa, sai hawaye kebin fuskarta ganin yadda numfashin Ardo ke zuwa yana dawowa gani take rasashi zasuyi, idan Ardo ya tafi ya barta shikenan batada sauran gata (Allah ne gatanki Laure).

Suna isa bakin k'ofa aka dakatar da su daga waje, anan reception suka zauna kan bench, sai addu'a take duk Wanda tazo bakinta nah nemama Kakan nata lafeeya, Malam Garba safa da marwa kawai yakeyi yana jiran tsammani tare da tausayawa aminin nasa, dan ciwon bai tab'a taso masa irin hakaba zuwa d'aya, saidai fatan samun lafia yake masa.

Taimakon gaggawa suka fara bashi ta hanyar saka masa oxygen, nurse Zainab ce ta fito, sanye da uniform irin na nurse, domin kiran Dr, Abdool saboda baya nan yaje gida yanzun, gashi ta kira wayarsa yana busy, da sauri ta fita, ganin ta yasa suka taso suna tambayarta jikinsa "da sauki" kawai tace ta fita.

Knocking tayi "yes" aka bata Umurnin shigowa, flat ne gidan mai one sitting room and 2bed room sai kitchen, irin dai na quarters d'innan, kwance yake kan 3seat idon sa lumshe yana waya, kan 1seat ta zauna tana k'arema gidan kallo dan shine first time d'inta shiga, komai neat sai k'amshi ke tashi kamar gidan mace.

"Hmm haba Hakeem duk matan da na gani ABU basu dama min lissafi ba, sai wannan 'yar fillon? Never."

Banji me Hakeem yace ba, murmushi yayi "any way yanzu inada bak'uwa, amma zan shigo end of week inshaa Allah".

'Yar dariya yayi tare da cewa "shegen kaya" sannan ya katse wayar.

"Yadai Zainab" ya fad'a ba tare daya bud'e idon ba.

Zainab da tunda taji ya ambaci 'yar fillo, k'irjinta yai mummuman bugawa sai zafi yake Mata.

Zainab itama Attachment takeyi daga Sokoto tazo, tunda taga Dr Majeed haka suke kiransa, taji ba Wanda takeso duk duniya kamarsa, tun daga lokacin take shige masa muddin yana hospital to tana tare dashi tanada kyau sosai itama siririyace mai matsakaicin tsayi kalar fatar tah bak'a CE amma irin mai kyallin nan.

Tayi mamakin yadda ya kira sunanta bah tareda yaga waye ba, kodai shima yana sonta neh? Waye zai ansamata wannan tambayan? Abun ko ba haka bane normally idan Abdool yaji muryanka sau biyu to yana noticing idan ya k'ara jinta.

Jin shiru nad'an mintuna ya sakashi mik'ewa zaune tare da ware manyan idonsa a Kanta.

Karaf ya idonta cikin nasa, cikin rawan murya tace "Sir we have a patient right now, he is in a very critical condition".

" OK am coming " kawai ya fad'a.

Mik'ewa tayi ta fice, binta yai da kallon "ko miye damuwarta oho!" Ya d'aga kafad'ar sah tare da tab'e baki.....

Sosai ya tausayawa tsohon dan yana jin jiki sosai, kusan 30mnt yayi a kansa kafin yayi nasarar daidaituwar numfashinsa, allurar jijiya yayi masa sannan yasa aka maidashi d'akin Hutu.

Fitowa yayi yana cire hand glove tare da Handkerchief ya fito dashi yana share zufa, dai2 lokacin Malam Garba ya iso inda yake "dofto ya ake ciki ya mai jikin"?

Murmushi yayi masa " kwantar da hankalinka Baba, ya samu sauki yanzu yana d'akin hutu muje muyi sallah koh"....

Laure data shige duniyar tunani bata masan Malam Garba ya tashi ba sai dubawa tayi bata ganshi ba d'agowa tayi ganin shi da Dr suna magana saidai bayansa kawai take gani, tashi tayi zuwa inda Suke.

Kaman ance ya juyo sukayi four eye cikin mamaki yace "you again"? Itakam tsoracewa tayi ganinsa, ita tama manta dashi.

Sunkuye kai tayi ba tare datace komai ba don batasan meyace ba, ganin idonta jajir alaman tasha kuka " me kikeyi anan."

Malam Garba ne yace "kasantane dofta"?

" eh to na tab'a ganinta anan garin tazo saida nono harma nasiya toh shine nake mamaki."

"Ayyo! Ai kakanta neh baida lahiya."

K'ara kallonta yayi cikin ransa yace "dalilin kukan kenan"? A fili yace "OK, amma meyasa kuka taho da ita Baba"?

" wallahi d'anga an rud'e ne, ni bammasan ta shigo ba."

Wayarsa ya d'auko yayi kira " Zainab d'anzo reception zakiyimin wani aiki" ya fad'a tare da tsinke wayar.

Minti kad'an sai gata tazo "kije da yarinyar nan gidanku pls" kallonta tayi sannan tace "muje ko" tana mata murmushi.

Binta tayi sannan ta shima Abdool suka fita jin an fara kiran isha'i, bayan sun fito gida yaje ya d'akko bargo da filo ya kawoma Malam Garba sannan yaje yayi round ya wuce gida, har yanzu Ardo bai farka ba, saboda hadda alluran bacci a ciki.

Tana zaune k'asa sai raba ido take, Zainab ce ta fito daga kitchen abinci ta aje mata tare da ruwa da drink, "ya sunanki ta tambayeta"?

" Ramlah " ta fad'a a takaice.

"Wow nice name."

Itakam name kawai ta gane, da yake tadanyi makaranta zuwa primary four Iya Hari ta fidda ita.

Murmushi yake tayi mata, "ciki abinci sai kizo kiyi sallah" Zainab ta fad'a tare da shiga bedroom d'in ta, da yake gidan su 2 ne dashi tare da wata Christan.

Aiko tana shigewa Laure ta kama cin abinci hannu baka, sai dadi ke ratsa mata k'wak'walwa tana jinjina ma 'yan birni akan cin dad'i.

Cikin minti biyar ta gama dashi tsaf, cikin kayan gida Zainab ta fito ganin plate kawai tayi, smiling tayi sannan ta d'auke takai kitchen, kunyace ta kama Laure, amma saita share kada ta Renata(hoho su Laure aja girma) lol.

"Muje kiyi sallah" dakin tsaf2 ba wani tarkace gado ne sai wardrobe, toilet ta nuna mata "ruwa nanan a bocket kiyi wanka akwai ruwa a bota na alwala" nagode " ta fad'a tare da shigewa.

Girgiza kai Zainab tayi tare da cewa "kodai itace 'yar fillon"? Tab'e baki tayi tare da fitar mata da kaya, sannan ta shimfida mata dadduma.

^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^^

*A k'auye...*

Iya Hari jin shiru har bayan isha ba Malam ba Laure yasa hankalinta yad'an d'aga, fita tayi ganin ba kowa yasa ta koma gida rikice ta d'auki mayafi, a waje taga wani yaro ta tambayesa nan yake shaida mata yagansu bakin asibiti an sakashi mota a mace.

K'ara rudewa tayi ta rasa inda zata saka Kanta, 'ya'yanta ta aikawa Lanti da Shatu, suma tuni suka iso a firgice.........

_love u friends_ ❤.

💄Meryerm Abdool 💄
[7/13, 10:01 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

```Manzon Allah (S.A.W) yana cewa:-```

_Baya shiga aljannah, maiyin annamimanci._

*Annamimanci yana nufin munafurci, munafurci yana nufin kayi maganan mutum koda abinda ka fada gaske ne abayan idonsa, Wanda ya kasance tozarci ne garesa.*
Chapter 4 · 0% Book details