Sashe 14
Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Auwal kuwa duk sati yana Argungu gurin d'ansa mai kama dashi fatar CE kawai baiyi hasken Baban ba, kuma yafi uwar haske yana nan dai tsakiya, Mama kuwa sai aikin gyaran 'yarta ta ciki da waje aiko tuni ta d'auki sheki tun balle bata kusa ga Hajia.
Abdool kuwa kullum yana hannun Asma'u, shan nono kad'ai ke had'ashi da uwarsa, tsabar sonda Asma'u ke mishi ko cikin barci taji kukansa saita farka, Mama tace lallai kuwa ranar da suka koma zai barki da kewa.
Auwal da kanshi ya roki Baba su basu Asma'u, ganin yadda ta shaku da Abdool, kuma tunda tace karatu zatayi, dan tunda taji abinda ya faru da yayarta(ta gayamata abinda ya faru, dan itace abokiyar shawarar ta)tace Aure ba yanzu ba, duk Wanda yazo hak'uri kawai take bashi.
Dak'ar suka shawo kan Baba ya amince, Auwal ya samo musu admission a *Usmanu danfodiyo* ita da Maryam k'anwarsa, Hajia nan habaici ya tashi hadda fad'in saboda an samu banza shine hadda kwaso k'anwa, anga dukiya shine akazo a dangwala, cin fuska dai zalla abinda Ameena ta guda kenan.
[8/6, 8:09 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
_💘💘 where r u my berries😘 Fatima Bello(momy shatima), Shamsiya Isma'il(fresh daughter) Aisha wanzams (my kanwa) I heart u guys 😘 *#1love#*_
📝 *Episode* 101--105
Saida tayi mai isarta ta godewa Allah, dak'yar ta mik'e idonta sunyi jajir tare da kumbura, sai Kanta dake matsanancin sarawa tsabar kukan da tasha, Abdool ta d'auka wanda shima sai kuka yakeyi ganin mamarsa nayi, dabin bango ta shiga part d'inta, saboda jirinda ke d'ibarta, a parlour ta zube zuciyarta kamar an d'ora mata dutsi dak'yar ta jawo wayarta ta kira Asma'u akan tazo gida, rud'ewa Asma'u tayi jin murya yayarta wata iri tasan ba lafia, kafin tace komai harta tsinke wayar, aiko kota kan Maryam bata bi ba tayi bakin titi tare da taron taxi.
Auwal kuwa yana shiga part d'insa ji yayi duniyar gaba daya tayi mishi zafi, ga rad'ad'in da zuciyarsa ke masa, ga kukan Ameena da Abdool da yake jiyowa yana tab'a masa zuciya, duk da cewa ita mai laifi ce a gareshi amma zuciyarsa ta k'asa yadda da bak'on al'amarin da ya same shi na rabuwa da Ameena, key kawai ya d'auka yabi ta k'ofar baya, normally kowa nada k'ofar baya wacce zai fita ba tare da sanin wani, motar shi ya d'auka ya fita gidan a tsiyace, tafiya kawai yake shi kanshi baisan inda ya dosa ba.
Ganin yanayin da ta isko yayarta ciki ga Abdool sai ihu yake amma uwar ko kallonsa ta k'asa yi balle tayi tunanin shayar da shi, Abdool ta d'auka, abinci ta had'a mishi saida ta tabbatar ya k'oshi sannan ta goyashi ba dad'ewa bacci yayi gaba dashi sai ajiyar zuciya yace, gurin yayarta ta matsa wanda itama jikinta a sanyaye yake, dafata tayi, nan ta d'ago ta kalleta da rinannun idanunta, "Aunty komai yayi tsanani maganin shi Allah, ki d'aure ki gayamin meke faruwa?"
Kama hannayenta duka biyu tayi, bakinta na rawa, sai a lokacin wasu zafafan hawaye suka zubo mata, sharewa tayi, nan ta labartawa k'anwarta duk abinda ya faru bayan wucewar ta makaranta.
"Inalillahi wa'inna ilaihirraji'un" shine kalmar da Asma'u tace maimata tawa iya tashin hankali kenan, yanzu ta fita tabar mata da mijinta lafia, amma kuma cikin k'ank'anin lokaci komai ya canja, farinciki ya koma bak'in ciki, batasan lokacin da hawaye suga zubo mata ba, nanta rungume yayarta sukaci gaba da kuka bamai lallashin wani.
Bankad'o k'ofa akayi da k'arfi, a tare suka d'ago dan ganin wanene, da kallon k'ask'anci ta bisu, ba kowa bace face Hajia "to matsiyata 'yan gadon lalata(sadnaf), me kuke jira yanzu kuma?, ina auren ya k'are ko kuma da sauran zance ne iyye" duk cikin masifa tace maganar.
Saida ta saka full stop sannan Asma'u tace "yi hak'uri Hajia yanzu zamu tafi" tsaki tayi tare da cewa "aikin banza sannan ta fice.
B'angaren Rafia kuwa suna isa part d'in Hajia bayan tayi Jim na mintuna tace "Hajia Bari in tafi zanyi wani aiki" part d'inta ta shiga, wannan gardin ne zaune a kureja amma ya maida kayanshi, wata shu'umar dariya tayi sannan ta d'aga mai babban farcenta "weldone Wizzy aikin ka ya tafi yadda akeso" murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba, bedroom ta shiga sai gata ta fito da rafar 'yan duba, bashi tayi tare da bud'emai k'ofar baya ya ware.
Asma'u ce ta d'ibo musu kayan sawarsu trolley biyu, drop suka d'auka sai k'ofar gida.
************************
Lokacin suka isa dak'ar suka shiga ciki, Mama na tsakar gida tana aiki, Mansur kuma na gyara mata alayyahu, ganin da kaya nik'i-nik'i sannan fuskacinsu a jeme duk sun wani yamutse, yasa tasan ba lafia ba, gaisa sukayi sannan suka shiga ciki, itama wanke hannu tayi tabi bayansu, ba wani boye-boye Asma'u ta gayamata abinda ya faru.
Ba k'aramin tashin hankali ta shiga ba, amma saita daure tace "Allah yasan hakan shi yafi zama mafi Alkhairi" dama tunda k'anwarta ta gayamata halin Hajia da irin wulak'anci da tayi musu, yasa ko sha'awa zuwa gidan bata tab'a yi ba, amma wannan sharrin dame yayi Kama, idan so take a saketa basai ta had'a da sharri ba, dan ta yarda da tarbiyar 'yarta ba zata taba aikata hakan ba koda bada Aure ba balle da Aurenta, Allah ya saka Mata, shine kawai ta fad'a a ranta.
Baba ma daya dawo yaji ba ransa ne yayi mummunan b'aci, musamman sharrin da akayi mata, dama Baba akwai zafi, abin ya bala'in k'ona ransa, fad'a yayi tayi da cewa zaije Sokoto gobe, saida Mama ta tausheshi sannan ya hak'ura, dan tasan idan yaje da wuya ayi mai kyau, amma yace gobe su Hafsat da Usman(k'anwar Mama da d'an kanin babansa) suje su kwaso kaya sannan su anso masa
takardar 'yarsa.
Auwal kuwa bayan gari yaje bakin ruwa, a can yayi zamansa dan gari ya riga yayi mishi zafi, nan yayi ta sak'awa da warwarewa har dare bai samo mafita, ganin duhu ya shigo, yasa shi hak'ura ya koma gida.
Hajia kuma ganin har dare ba Auwal ba labarin sa gashi ta kira wayoyinsa a kashe yasa hankalinta tashi, bakin k'ofar part d'insa ta tsaya zaman jiran dawowar sa.
Dai2 part d'insa yaga Hajia, jiki sukwana ya k'arasa gurinta tare da gaida ita, bata ansa sai fad'a data haushi dashi "wai kai Auwalu wane iri yaro kake, kabi ka tada hankalinka akan yarinyar da ta gama cutar da kai, gara ka fiddata a ranka dan kun rigada kun rabu kenan ehe, to garama tun wuri ka yakiceta a ranka ka rungume Ummita dan har nayi magana da hajiyarta nan ba dad'ewa za'ayi bikinku, sannan ka rubuta takardar waccen matsiyaciyar ka kawo min, zan aika mata har gida" Auwal da zuciyarsa ta gama k'ek'ashewa "tau Momy" kawai yace, sannan ya shiga ciki, itama ficewa tayi tana fad'in "daga Allah ya tona mana 'yar iska" tana shiga part d'inta nan ma Maryam ta isko ta had'a kai da guiwa, dan tunda ta dawo Hajia ta fad'a mata abinda ya faru, ta shiga damuwa hadda kukanta dan ta saba da Aunty da Asma'u ga Abdool Son d'inta, ita sam bata yadda aunty zata aikata abinda akace tayi ba, dan tasan ta farin Sani kullum cikin yi musu nasiha take itada akan su tsare mutuncinsu sannan ace ta aikata wannan barnar.
Tsaki Hajia tayi "kwayi kwa gama" sannan ta shige ciki tana mitar halin irin na 'ya'yanta Sam basu biyota ba(ai sun huta basuyi bak'in gado ba) waya ta kira hajia Umma mamarsu Rafia danso take ayi komai cikin lokaci, saboda ta k'ara cusawa Ameena bak'in ciki.
Auwal na shiga ciki jin ba motsin wata halitta ko'ina shiru, sabanin da, koda zai shigo a parlour zai samesu suna kallon sunnah TV wata ran kuwa su kalli zee TV ko kuma su zauna suna hirarsu gwanin sha'awa, Murmushin takaici yayi tare da shigewa ciki, takardar ya rubuta kamar yadda ta buk'ata yakai mata.
Washe gari kamar yadda Abba ya buk'ata haka su Hafsat da Usman Suka taho da babbar motar kwasar kaya, amma me Hajia tace ba wani kaya da zasu kwasa ai danta ne ya saya, haka aka shiga rigima sun nace sai kwasa itama tace basu isa ba, hayaniyar ce ta kawo hankalin mutanen gidan wad'anda duk abinda ya faru basuma San anyi ba sai lokacin.
Ganin rigimar tak'i k'are wa yasa Sani kiran Auwal ya tambayesa nan ya tabbatar kayanta ne ko tsinke bai siya mata ba, da yake a hand's free ya saka kowa yanaji yasa ta basu suka kwasa, tana biyarsu da habaici da bak'ak'en maganganu, ba Wanda ya kulata har suka k'are tun kafin su tambayi takardar 'yarsu ta kawo musu, tare cin mutunci.
Auwal da tun safe ya fita zuwa yayi ya tattara duk wata k'addara tasa ya sayar, banki yaje ya bud'e kid account ya zuba kudin, iya wad'anda zai rike a hannun sa ya rage, bashi ya dawo ba sai goman dare, d'akin sa ya shiga yayi wanka ya kimtsa sannan ya d'auka diary sabo kal, rubuta sosai yayi sannan ya sake rubuta wasik'u har uku, part d'in Hajia yaje yace Maryam ta d'auko mishi key din part d'in Alhaji dan duk wannan ruguntsumin da ake Alhaji bayanan ya tafi umrah, d'auko mishi tayi bud'ewa yayi sannan ya shiga bedroom, wardrobe d'insa ya bud'e wata leda ya saka daga can sama sannan ya rufe ya fito, Maryam ya kira ya bata keys d'in da wasik'a tare da tabbatar mata da ta bawa Hajia zuwa gobe da tau ta ansa masa sannan ta shige ciki.
Washe gari bayan sun gama breakfast ta d'auko wasik'ar ta bama Hajia.
"Lahaula walah k'uwwati illah billah" shine Kalmar da Hajia ta fad'i tare da zubewa k'asa a sume........
_friends ina barar Addu'arku akan wata buk'ata tawa, ina da tabbacin zan samu. Love u all_ 😍
💄Meryerm Abdool💄
[8/6, 8:15 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
Abdool kuwa kullum yana hannun Asma'u, shan nono kad'ai ke had'ashi da uwarsa, tsabar sonda Asma'u ke mishi ko cikin barci taji kukansa saita farka, Mama tace lallai kuwa ranar da suka koma zai barki da kewa.
Auwal da kanshi ya roki Baba su basu Asma'u, ganin yadda ta shaku da Abdool, kuma tunda tace karatu zatayi, dan tunda taji abinda ya faru da yayarta(ta gayamata abinda ya faru, dan itace abokiyar shawarar ta)tace Aure ba yanzu ba, duk Wanda yazo hak'uri kawai take bashi.
Dak'ar suka shawo kan Baba ya amince, Auwal ya samo musu admission a *Usmanu danfodiyo* ita da Maryam k'anwarsa, Hajia nan habaici ya tashi hadda fad'in saboda an samu banza shine hadda kwaso k'anwa, anga dukiya shine akazo a dangwala, cin fuska dai zalla abinda Ameena ta guda kenan.
[8/6, 8:09 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽
(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)
_💘💘 where r u my berries😘 Fatima Bello(momy shatima), Shamsiya Isma'il(fresh daughter) Aisha wanzams (my kanwa) I heart u guys 😘 *#1love#*_
📝 *Episode* 101--105
Saida tayi mai isarta ta godewa Allah, dak'yar ta mik'e idonta sunyi jajir tare da kumbura, sai Kanta dake matsanancin sarawa tsabar kukan da tasha, Abdool ta d'auka wanda shima sai kuka yakeyi ganin mamarsa nayi, dabin bango ta shiga part d'inta, saboda jirinda ke d'ibarta, a parlour ta zube zuciyarta kamar an d'ora mata dutsi dak'yar ta jawo wayarta ta kira Asma'u akan tazo gida, rud'ewa Asma'u tayi jin murya yayarta wata iri tasan ba lafia, kafin tace komai harta tsinke wayar, aiko kota kan Maryam bata bi ba tayi bakin titi tare da taron taxi.
Auwal kuwa yana shiga part d'insa ji yayi duniyar gaba daya tayi mishi zafi, ga rad'ad'in da zuciyarsa ke masa, ga kukan Ameena da Abdool da yake jiyowa yana tab'a masa zuciya, duk da cewa ita mai laifi ce a gareshi amma zuciyarsa ta k'asa yadda da bak'on al'amarin da ya same shi na rabuwa da Ameena, key kawai ya d'auka yabi ta k'ofar baya, normally kowa nada k'ofar baya wacce zai fita ba tare da sanin wani, motar shi ya d'auka ya fita gidan a tsiyace, tafiya kawai yake shi kanshi baisan inda ya dosa ba.
Ganin yanayin da ta isko yayarta ciki ga Abdool sai ihu yake amma uwar ko kallonsa ta k'asa yi balle tayi tunanin shayar da shi, Abdool ta d'auka, abinci ta had'a mishi saida ta tabbatar ya k'oshi sannan ta goyashi ba dad'ewa bacci yayi gaba dashi sai ajiyar zuciya yace, gurin yayarta ta matsa wanda itama jikinta a sanyaye yake, dafata tayi, nan ta d'ago ta kalleta da rinannun idanunta, "Aunty komai yayi tsanani maganin shi Allah, ki d'aure ki gayamin meke faruwa?"
Kama hannayenta duka biyu tayi, bakinta na rawa, sai a lokacin wasu zafafan hawaye suka zubo mata, sharewa tayi, nan ta labartawa k'anwarta duk abinda ya faru bayan wucewar ta makaranta.
"Inalillahi wa'inna ilaihirraji'un" shine kalmar da Asma'u tace maimata tawa iya tashin hankali kenan, yanzu ta fita tabar mata da mijinta lafia, amma kuma cikin k'ank'anin lokaci komai ya canja, farinciki ya koma bak'in ciki, batasan lokacin da hawaye suga zubo mata ba, nanta rungume yayarta sukaci gaba da kuka bamai lallashin wani.
Bankad'o k'ofa akayi da k'arfi, a tare suka d'ago dan ganin wanene, da kallon k'ask'anci ta bisu, ba kowa bace face Hajia "to matsiyata 'yan gadon lalata(sadnaf), me kuke jira yanzu kuma?, ina auren ya k'are ko kuma da sauran zance ne iyye" duk cikin masifa tace maganar.
Saida ta saka full stop sannan Asma'u tace "yi hak'uri Hajia yanzu zamu tafi" tsaki tayi tare da cewa "aikin banza sannan ta fice.
B'angaren Rafia kuwa suna isa part d'in Hajia bayan tayi Jim na mintuna tace "Hajia Bari in tafi zanyi wani aiki" part d'inta ta shiga, wannan gardin ne zaune a kureja amma ya maida kayanshi, wata shu'umar dariya tayi sannan ta d'aga mai babban farcenta "weldone Wizzy aikin ka ya tafi yadda akeso" murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba, bedroom ta shiga sai gata ta fito da rafar 'yan duba, bashi tayi tare da bud'emai k'ofar baya ya ware.
Asma'u ce ta d'ibo musu kayan sawarsu trolley biyu, drop suka d'auka sai k'ofar gida.
************************
Lokacin suka isa dak'ar suka shiga ciki, Mama na tsakar gida tana aiki, Mansur kuma na gyara mata alayyahu, ganin da kaya nik'i-nik'i sannan fuskacinsu a jeme duk sun wani yamutse, yasa tasan ba lafia ba, gaisa sukayi sannan suka shiga ciki, itama wanke hannu tayi tabi bayansu, ba wani boye-boye Asma'u ta gayamata abinda ya faru.
Ba k'aramin tashin hankali ta shiga ba, amma saita daure tace "Allah yasan hakan shi yafi zama mafi Alkhairi" dama tunda k'anwarta ta gayamata halin Hajia da irin wulak'anci da tayi musu, yasa ko sha'awa zuwa gidan bata tab'a yi ba, amma wannan sharrin dame yayi Kama, idan so take a saketa basai ta had'a da sharri ba, dan ta yarda da tarbiyar 'yarta ba zata taba aikata hakan ba koda bada Aure ba balle da Aurenta, Allah ya saka Mata, shine kawai ta fad'a a ranta.
Baba ma daya dawo yaji ba ransa ne yayi mummunan b'aci, musamman sharrin da akayi mata, dama Baba akwai zafi, abin ya bala'in k'ona ransa, fad'a yayi tayi da cewa zaije Sokoto gobe, saida Mama ta tausheshi sannan ya hak'ura, dan tasan idan yaje da wuya ayi mai kyau, amma yace gobe su Hafsat da Usman(k'anwar Mama da d'an kanin babansa) suje su kwaso kaya sannan su anso masa
takardar 'yarsa.
Auwal kuwa bayan gari yaje bakin ruwa, a can yayi zamansa dan gari ya riga yayi mishi zafi, nan yayi ta sak'awa da warwarewa har dare bai samo mafita, ganin duhu ya shigo, yasa shi hak'ura ya koma gida.
Hajia kuma ganin har dare ba Auwal ba labarin sa gashi ta kira wayoyinsa a kashe yasa hankalinta tashi, bakin k'ofar part d'insa ta tsaya zaman jiran dawowar sa.
Dai2 part d'insa yaga Hajia, jiki sukwana ya k'arasa gurinta tare da gaida ita, bata ansa sai fad'a data haushi dashi "wai kai Auwalu wane iri yaro kake, kabi ka tada hankalinka akan yarinyar da ta gama cutar da kai, gara ka fiddata a ranka dan kun rigada kun rabu kenan ehe, to garama tun wuri ka yakiceta a ranka ka rungume Ummita dan har nayi magana da hajiyarta nan ba dad'ewa za'ayi bikinku, sannan ka rubuta takardar waccen matsiyaciyar ka kawo min, zan aika mata har gida" Auwal da zuciyarsa ta gama k'ek'ashewa "tau Momy" kawai yace, sannan ya shiga ciki, itama ficewa tayi tana fad'in "daga Allah ya tona mana 'yar iska" tana shiga part d'inta nan ma Maryam ta isko ta had'a kai da guiwa, dan tunda ta dawo Hajia ta fad'a mata abinda ya faru, ta shiga damuwa hadda kukanta dan ta saba da Aunty da Asma'u ga Abdool Son d'inta, ita sam bata yadda aunty zata aikata abinda akace tayi ba, dan tasan ta farin Sani kullum cikin yi musu nasiha take itada akan su tsare mutuncinsu sannan ace ta aikata wannan barnar.
Tsaki Hajia tayi "kwayi kwa gama" sannan ta shige ciki tana mitar halin irin na 'ya'yanta Sam basu biyota ba(ai sun huta basuyi bak'in gado ba) waya ta kira hajia Umma mamarsu Rafia danso take ayi komai cikin lokaci, saboda ta k'ara cusawa Ameena bak'in ciki.
Auwal na shiga ciki jin ba motsin wata halitta ko'ina shiru, sabanin da, koda zai shigo a parlour zai samesu suna kallon sunnah TV wata ran kuwa su kalli zee TV ko kuma su zauna suna hirarsu gwanin sha'awa, Murmushin takaici yayi tare da shigewa ciki, takardar ya rubuta kamar yadda ta buk'ata yakai mata.
Washe gari kamar yadda Abba ya buk'ata haka su Hafsat da Usman Suka taho da babbar motar kwasar kaya, amma me Hajia tace ba wani kaya da zasu kwasa ai danta ne ya saya, haka aka shiga rigima sun nace sai kwasa itama tace basu isa ba, hayaniyar ce ta kawo hankalin mutanen gidan wad'anda duk abinda ya faru basuma San anyi ba sai lokacin.
Ganin rigimar tak'i k'are wa yasa Sani kiran Auwal ya tambayesa nan ya tabbatar kayanta ne ko tsinke bai siya mata ba, da yake a hand's free ya saka kowa yanaji yasa ta basu suka kwasa, tana biyarsu da habaici da bak'ak'en maganganu, ba Wanda ya kulata har suka k'are tun kafin su tambayi takardar 'yarsu ta kawo musu, tare cin mutunci.
Auwal da tun safe ya fita zuwa yayi ya tattara duk wata k'addara tasa ya sayar, banki yaje ya bud'e kid account ya zuba kudin, iya wad'anda zai rike a hannun sa ya rage, bashi ya dawo ba sai goman dare, d'akin sa ya shiga yayi wanka ya kimtsa sannan ya d'auka diary sabo kal, rubuta sosai yayi sannan ya sake rubuta wasik'u har uku, part d'in Hajia yaje yace Maryam ta d'auko mishi key din part d'in Alhaji dan duk wannan ruguntsumin da ake Alhaji bayanan ya tafi umrah, d'auko mishi tayi bud'ewa yayi sannan ya shiga bedroom, wardrobe d'insa ya bud'e wata leda ya saka daga can sama sannan ya rufe ya fito, Maryam ya kira ya bata keys d'in da wasik'a tare da tabbatar mata da ta bawa Hajia zuwa gobe da tau ta ansa masa sannan ta shige ciki.
Washe gari bayan sun gama breakfast ta d'auko wasik'ar ta bama Hajia.
"Lahaula walah k'uwwati illah billah" shine Kalmar da Hajia ta fad'i tare da zubewa k'asa a sume........
_friends ina barar Addu'arku akan wata buk'ata tawa, ina da tabbacin zan samu. Love u all_ 😍
💄Meryerm Abdool💄
[8/6, 8:15 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
✨ *Servant of Majesty* ✨
Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄
© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽