Sashe 22
Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abdool yana SS1 Nihal na nursery, tuni ya saba da saka medical d'insa inda a school d'insu wasu ke ganin jin kai ne da tsabar raini dan yaga yanada Brain yasa yake saka glass dan sauka haka kawai yake sakawa ganin yadda ya zauna mishi tsaf, Abdool ya taso yaro mai kuzari da sanin ciwon kai ga k'auna da yake nunawa kanninsa haka sai saka Nihal gaba yayi mata lesson in Dadynsu bayanan shi kuma inya dawo yayi mishi, shi har mamakin k'ok'arin Abdool yake yaro sai kace dan Jamia komai kana ana bud'e kwakwalwarsa ana zuba masa, ita ma dai Nihal Kanta naja ba laifi sai yake danganta hakan da ilimin Ameena, haka sukaci gaba da gudanar da Rayuwarsu cikin farinciki, sukanje Hutu lokaci zuwa lokaci haka Alhaji Sada na zuwa har Kaduna ya dubasu, yanajin dad'in yadda suke kula da Abdool, tuni Alhaji ya saba da Yusuf haka zasu zauna suyi ta hira in yazo dama ga Yusuf da barkwanci wuni guda kukayi a tare zaku Saba.
*****************
Ranar rabuwa ranar da zukata suka nisanta da juna ranar ruhi da gangar jiki suka shiga maraici ranar da mai rabawa ta raba, ranar da Yusuf yayi accident a hanyarsa ta dawowa Kaduna ya fito daga Besse anan on d sport wuyansa ya kare nan take ya ansa kiran maliccinsa, sai gawa su Ameena suka gani fad'in kalan tashin hankalinda suka shiga anan dan page d'in ga bazai ishemu ba, kowacce ta kwatanta da mijinta ne da babanta ne da d'anta ne da k'annin ta ko yayanta ne ya zataji haka suma Familyn Yusuf sukaji da rashin da ya sameso, a Besse aka wuce da gawar akan kayi komai daya dace da shari'ar sunnar Manzo S.A.W, ba'ayi wani zaman makoki ba, duba da yadda zaman ya koma zaman hira da tsegumi da cin shinkafa, Wanda ya mutu shiya mutu kawai sai kuwa na kusa dashi, da suke cikin jimami rashin sa, duk wannan abun Abdool baida labari dan lokacin yana ABU zariya inda yake matriculation, Wanda Yusuf ne da kanshi ya kaishi ya kuma zaba mishi medicine, ganin yanata kiran Dadyn nashi wayanshi bata zuwa yasa ya kira Maminsa, nan ta sheda mishi suna Besse ba charge a wayansa, sannan tace idan da chance ya samesu Bessen k'arshen sati, nan ya tambayeta lafia dai tace qlau ba komai, amma jikin na bashi ba lafia.
Lokacin da yazo ya samu abinda ya faru, yayi kukan rashin Dady dan sosai ya maye masa gurbin Auwal yanzu gashi ya tafi ya barsu.
(Duniya labari)
Anan ta zauna harta kammala takabanta, akayi rabon gado kamar addini ya tanadar daga an kammala hada komai, tayi sa'a gidansu na Kaduna ya shigo cikin rabonsu hakan yasa tace zata koma Kaduna, sun so tayi zaman ta nan tare dasu dan Ameena mutum ce wacce kowa ke sha'awar zama da ita, saboda iya zamanta da mutane da kyautata,tafi so koda zata cutu ne wani yaji dad'i amma batason wani ya cutu akanta, hak'uri ta basu saboda ta riga ta saba da Kaduna ga kuma karantun yara (weather ma akwai banbanci sosai tsakanin Kebbi da Kaduna) haka taje Argungu tayi musu sallama nasiha sosai Baba da Inna sukayi mata duk da susan Ameena zata tsare mutuncinta aduk inda ta riski Kanta, sannan ta wuce da Mansur d'an yad'an rage mata kewa, da yake Abdool ya koma Zariya saboda karatu, shima Mansur ya kammala NCE inda zaiyi degree a can.
Bayan komarsu ta shiga neman aiki tuk'uru, shine amfanin ayi karatun koba mutuwa akwai sayin yanayi Wanda miji zai nemi agajin matarsa musamman ma inga nauyin iyali, cikin sa'a ta samu aiki ministry of Agriculture inda zata ringa basu shawarwari akan dashen itatuwa da fulawowi da dai duk wani dangin tsirrai, haka kuma gefe d'aya ta bod'e nata gidan koma inda ita kula da abinda sai Mansur da wasu matasa data d'auka take biyansu, in fact dai ita keda mallakinsa nata ne, ga business tana yi da tana bada odar kaya daga Dubai, Alhamdulillah, tafi k'arfin buk'atunta dana yaranta, yayin su kuma ta saya musu shares da gadon su ana jujjuyawa a Ja'iz bank inda suka halattacen kasuwanci da kud'in.
Wata rana in ta zaune sai tayi ta tuna maganganun Yusuf da yake cewa "Ameena ko a yanzu nabar duniya bana shayin Wanda zai kulamin da yara na da tarbiyar su, saboda nasan zaki iya ke namijin duniya ce, wacce kowane namiji ya sameki zaiyi alfahari da ita, ina k'aunarki Ameena har numfashi na, na k'arshe" ita kuma idan yana fad'ar haka saita rufe masa baki tace.
"Ba zaka mutu ba mijina kai kad'ai inshaa Allah saidai mutuwa ta doke mu tare bana fatan ka barni a duniya ni kad'ai, pls ka dena fad'ar haka" murmushi kawai yakeyi ya canja zance, gashi yanzu tana tunawa shikenan ya tafi ya barta, nema masa gafarar ubangiji take dan shine kadai ya rage a tsakaninsu yanzu, ga zawarawa sunyo mata caa abokan Yusuf da abokan aikinta itakam hak'uri kawai take basu, yanzu kam renon marayun yaranta ne a gabanta bata sake jajibo wani Auren ba, ko iyayenta da sukaji sun goyi bayanta dan yanzu tasan meye mai amfaninta da Wanda baya amfaninta...
Ciwo ne ya tasowa Alhaji Sada da gaske har anyi admitting nashi hospital, hakan yasa Abdool zuwa kiran Maminsa akan zaije ya dubasa, sosai ta tausaya masa itama taso taje ta dubasa dan Alhaji kamar ubane gunta ga kirki, har Besse yaje mata gaisuwar Yusuf, amma kuma tana tsoron yadda familyn zasu karb'eta, tsoron abinda zaije ya dawo yasa ta fasa zuwa tace Abdool ya gaishesa sosai.
Alhaji yayi murna sosai da zuwan Abdool Wanda shine na farko tun bayan rabuwar iyayensa haka 'yan uwa da iyayensa maza ga su Isma'il sa'anninsa ga kuma k'anninsu gida ya cika sosai sa zuria, Hajia tunda ta ansa gaisuwarsa a dak'ile bata koda kalli inda yake ba, dan ita har yau haushinsu takeji shida uwarsa, Rafia kowa sai wani son munafurci take nuna masa amma shi Sam bata kwanta masa a rai ba tunda ya ganta(INA kuwa kaga shedan mai raba aure).
A tare dashi akayi jinyar Alhaji har murmure, aka sallamesu a part d'in Alhaji ya tare wadda hakan yasa ta daina shigowa, satin sa 1 yace zai koma saboda makaranta, nan Alhaji ya d'auko wasiyyar mahaifinsa ya danka masa, d'akin da ya zama NASA a part d'in Alhaji ya shiga ya, direct da diary ya fara.
_"zuwa gareka d'ana abin Alfahari sanyin idaniyata, kayi hak'uri d'ana nasan koda wasik'a ta zata sameka, zakace banyi maka adalci ba dana barka tun bakasan waye kai ba, nasan zaka zargeni da tauye maka hakk'inka, saidai ina da tabbacin Ameena zatayi dutyn ta ta kuma had'a da nawa tayi, saboda na yadda da ita"_
Hawayen da suka zubu masa ya share tare da cewa "wannan hakane Abba Mami mace tamkar dubu" sannan yaci gaba, duk wani labari tun daga had'uwarsu da Ameena auren da k'uncin da ta shiga da soyayyar da Asma'u ta nuna masa har zuwa rabuwarsu saida ya rubuta masa, zuwa yanzu kuma yake harda majina yana tausaya iyayen nasa, tare dajin k'ara son aunty Asma'u dayi mata Addu'a akan Allah ya bayyana ta, sannan yace "Abba banga laifinka akan komai ba sai akan tafiyar ka meyasa Abba? Meyasa zaka tafi ka barni, shin kayi tunanin rayuwar da zanyi? Meyasa ka guji mahaifarka kabar iyayenka da begenka, kana ina Abba!? Where r u Abba??" Ya fad'a da k'arfi cikin sheshekar kuka.
Alhaji Sada ne ya shigo jin k'aran sa, yasan za'ayi haka duk baisan mai wasik'ar ta k'unsa ba, dagoshi yayi tare da rungume shi yana dan bubbuga masa baya, alaman rarrashi "yi Hak'uri Abdulmajeed ka d'auke shi a matsayin k'addarar ka, ka yafewa mahaifinka tare da masa fatan Alkhairi kaji" rarrashinsa yayi da kalamai masu kwantar da zuciya....
A ranar yaje banking, ya girgiza da ganin tsabar kud'in da mahaifinsa ya aje, masa kud'i bana wasa ba, tun lokacin bare kuma yanzu da komai ya canja, (Allah ya zuba Alkhairi a harkar kasuwanci, don abinda annabawansa sukayi Kenan, muddin bawa zai tsarkake sana'arsa tabbas zaiga akhairai a ciki).
Transfer kud'in yayi zuwa account d'insa, nan ya nemi shawarar Alhaji akan yadda zaiyi da kud'in dan kud'in da yawa kuma shi baya da buk'atar kud'i dan Alhaji ne ke d'auke da karatunsa yanzu tun bayan rasuwar Yusuf, kuma shima yana dan business dan Abdul yarone da yasan ciwon kansa, ko lokacin da yake Argungu shik kula shagon kawu Mansur in ya shiga school kuma tsab zai dawo ya isko kayansa, haka Mami na turo mishi sosai duk da yana cewa ta barshi.
Alhaji shawarar a fara Gina mishi hospital ya bashi tun da medicine yake karantawa, hakan kuwa akayi dan itama Mami hakan tace nan suka sayi fili mai kyau aka fara tsara hospital ta gani a maganta inda kawu Mansur ke kula da ganin da yake yana gari.
*****************
B'angaren Asma'u kuwa yanzu bata da wata matsala dan ba'ayi mata sai in taje Wanda zuwa yanzu ta Saba da jarabar Iya Hari, Abdulrahim kuwa ya rik'e ta da Amana kamar yadda yayi alk'awari suna zaune lafia abinsu bakajin Kansu ko sabani suka samu suke shirya Kansu ba tare da wani yaji ba, Ramlah kuwa sai girma take abinta ga kulawar iyaye tana samu suna matuk'ar kula da ita da bata tarbiyar islama, tuni ta iya haruffa k'ananan surori tana 4 year, er lukuta da ita yanayin jikin irin na Asma'u ne, nan kad'ai suke kama.
A 'yan kwanakin nan mafarkin su Baba da Inna da Aunty Ameena, Abdool ya matsawa Asma'u har yakai ko kwanciyar rana tayi sai tayi, hakan yasa hankalinta ya koma gida baki d'aya, yanzu kam ta shirya runkarar Baba duk da tsawon lokaci bai nemata ba, amma tana fatan idan taje ya yafeta ya maida mata iyalanta, hakan yasa ta tunkari Abdulrahim da maganar son zuwa gida, hakan yayi mishi dad'i sosai dama ya dad'e yana bibiyarta suje tana cewa ba yanzu ba, suka tsara zasuje k'arshen sati.
*****************
Ranar rabuwa ranar da zukata suka nisanta da juna ranar ruhi da gangar jiki suka shiga maraici ranar da mai rabawa ta raba, ranar da Yusuf yayi accident a hanyarsa ta dawowa Kaduna ya fito daga Besse anan on d sport wuyansa ya kare nan take ya ansa kiran maliccinsa, sai gawa su Ameena suka gani fad'in kalan tashin hankalinda suka shiga anan dan page d'in ga bazai ishemu ba, kowacce ta kwatanta da mijinta ne da babanta ne da d'anta ne da k'annin ta ko yayanta ne ya zataji haka suma Familyn Yusuf sukaji da rashin da ya sameso, a Besse aka wuce da gawar akan kayi komai daya dace da shari'ar sunnar Manzo S.A.W, ba'ayi wani zaman makoki ba, duba da yadda zaman ya koma zaman hira da tsegumi da cin shinkafa, Wanda ya mutu shiya mutu kawai sai kuwa na kusa dashi, da suke cikin jimami rashin sa, duk wannan abun Abdool baida labari dan lokacin yana ABU zariya inda yake matriculation, Wanda Yusuf ne da kanshi ya kaishi ya kuma zaba mishi medicine, ganin yanata kiran Dadyn nashi wayanshi bata zuwa yasa ya kira Maminsa, nan ta sheda mishi suna Besse ba charge a wayansa, sannan tace idan da chance ya samesu Bessen k'arshen sati, nan ya tambayeta lafia dai tace qlau ba komai, amma jikin na bashi ba lafia.
Lokacin da yazo ya samu abinda ya faru, yayi kukan rashin Dady dan sosai ya maye masa gurbin Auwal yanzu gashi ya tafi ya barsu.
(Duniya labari)
Anan ta zauna harta kammala takabanta, akayi rabon gado kamar addini ya tanadar daga an kammala hada komai, tayi sa'a gidansu na Kaduna ya shigo cikin rabonsu hakan yasa tace zata koma Kaduna, sun so tayi zaman ta nan tare dasu dan Ameena mutum ce wacce kowa ke sha'awar zama da ita, saboda iya zamanta da mutane da kyautata,tafi so koda zata cutu ne wani yaji dad'i amma batason wani ya cutu akanta, hak'uri ta basu saboda ta riga ta saba da Kaduna ga kuma karantun yara (weather ma akwai banbanci sosai tsakanin Kebbi da Kaduna) haka taje Argungu tayi musu sallama nasiha sosai Baba da Inna sukayi mata duk da susan Ameena zata tsare mutuncinta aduk inda ta riski Kanta, sannan ta wuce da Mansur d'an yad'an rage mata kewa, da yake Abdool ya koma Zariya saboda karatu, shima Mansur ya kammala NCE inda zaiyi degree a can.
Bayan komarsu ta shiga neman aiki tuk'uru, shine amfanin ayi karatun koba mutuwa akwai sayin yanayi Wanda miji zai nemi agajin matarsa musamman ma inga nauyin iyali, cikin sa'a ta samu aiki ministry of Agriculture inda zata ringa basu shawarwari akan dashen itatuwa da fulawowi da dai duk wani dangin tsirrai, haka kuma gefe d'aya ta bod'e nata gidan koma inda ita kula da abinda sai Mansur da wasu matasa data d'auka take biyansu, in fact dai ita keda mallakinsa nata ne, ga business tana yi da tana bada odar kaya daga Dubai, Alhamdulillah, tafi k'arfin buk'atunta dana yaranta, yayin su kuma ta saya musu shares da gadon su ana jujjuyawa a Ja'iz bank inda suka halattacen kasuwanci da kud'in.
Wata rana in ta zaune sai tayi ta tuna maganganun Yusuf da yake cewa "Ameena ko a yanzu nabar duniya bana shayin Wanda zai kulamin da yara na da tarbiyar su, saboda nasan zaki iya ke namijin duniya ce, wacce kowane namiji ya sameki zaiyi alfahari da ita, ina k'aunarki Ameena har numfashi na, na k'arshe" ita kuma idan yana fad'ar haka saita rufe masa baki tace.
"Ba zaka mutu ba mijina kai kad'ai inshaa Allah saidai mutuwa ta doke mu tare bana fatan ka barni a duniya ni kad'ai, pls ka dena fad'ar haka" murmushi kawai yakeyi ya canja zance, gashi yanzu tana tunawa shikenan ya tafi ya barta, nema masa gafarar ubangiji take dan shine kadai ya rage a tsakaninsu yanzu, ga zawarawa sunyo mata caa abokan Yusuf da abokan aikinta itakam hak'uri kawai take basu, yanzu kam renon marayun yaranta ne a gabanta bata sake jajibo wani Auren ba, ko iyayenta da sukaji sun goyi bayanta dan yanzu tasan meye mai amfaninta da Wanda baya amfaninta...
Ciwo ne ya tasowa Alhaji Sada da gaske har anyi admitting nashi hospital, hakan yasa Abdool zuwa kiran Maminsa akan zaije ya dubasa, sosai ta tausaya masa itama taso taje ta dubasa dan Alhaji kamar ubane gunta ga kirki, har Besse yaje mata gaisuwar Yusuf, amma kuma tana tsoron yadda familyn zasu karb'eta, tsoron abinda zaije ya dawo yasa ta fasa zuwa tace Abdool ya gaishesa sosai.
Alhaji yayi murna sosai da zuwan Abdool Wanda shine na farko tun bayan rabuwar iyayensa haka 'yan uwa da iyayensa maza ga su Isma'il sa'anninsa ga kuma k'anninsu gida ya cika sosai sa zuria, Hajia tunda ta ansa gaisuwarsa a dak'ile bata koda kalli inda yake ba, dan ita har yau haushinsu takeji shida uwarsa, Rafia kowa sai wani son munafurci take nuna masa amma shi Sam bata kwanta masa a rai ba tunda ya ganta(INA kuwa kaga shedan mai raba aure).
A tare dashi akayi jinyar Alhaji har murmure, aka sallamesu a part d'in Alhaji ya tare wadda hakan yasa ta daina shigowa, satin sa 1 yace zai koma saboda makaranta, nan Alhaji ya d'auko wasiyyar mahaifinsa ya danka masa, d'akin da ya zama NASA a part d'in Alhaji ya shiga ya, direct da diary ya fara.
_"zuwa gareka d'ana abin Alfahari sanyin idaniyata, kayi hak'uri d'ana nasan koda wasik'a ta zata sameka, zakace banyi maka adalci ba dana barka tun bakasan waye kai ba, nasan zaka zargeni da tauye maka hakk'inka, saidai ina da tabbacin Ameena zatayi dutyn ta ta kuma had'a da nawa tayi, saboda na yadda da ita"_
Hawayen da suka zubu masa ya share tare da cewa "wannan hakane Abba Mami mace tamkar dubu" sannan yaci gaba, duk wani labari tun daga had'uwarsu da Ameena auren da k'uncin da ta shiga da soyayyar da Asma'u ta nuna masa har zuwa rabuwarsu saida ya rubuta masa, zuwa yanzu kuma yake harda majina yana tausaya iyayen nasa, tare dajin k'ara son aunty Asma'u dayi mata Addu'a akan Allah ya bayyana ta, sannan yace "Abba banga laifinka akan komai ba sai akan tafiyar ka meyasa Abba? Meyasa zaka tafi ka barni, shin kayi tunanin rayuwar da zanyi? Meyasa ka guji mahaifarka kabar iyayenka da begenka, kana ina Abba!? Where r u Abba??" Ya fad'a da k'arfi cikin sheshekar kuka.
Alhaji Sada ne ya shigo jin k'aran sa, yasan za'ayi haka duk baisan mai wasik'ar ta k'unsa ba, dagoshi yayi tare da rungume shi yana dan bubbuga masa baya, alaman rarrashi "yi Hak'uri Abdulmajeed ka d'auke shi a matsayin k'addarar ka, ka yafewa mahaifinka tare da masa fatan Alkhairi kaji" rarrashinsa yayi da kalamai masu kwantar da zuciya....
A ranar yaje banking, ya girgiza da ganin tsabar kud'in da mahaifinsa ya aje, masa kud'i bana wasa ba, tun lokacin bare kuma yanzu da komai ya canja, (Allah ya zuba Alkhairi a harkar kasuwanci, don abinda annabawansa sukayi Kenan, muddin bawa zai tsarkake sana'arsa tabbas zaiga akhairai a ciki).
Transfer kud'in yayi zuwa account d'insa, nan ya nemi shawarar Alhaji akan yadda zaiyi da kud'in dan kud'in da yawa kuma shi baya da buk'atar kud'i dan Alhaji ne ke d'auke da karatunsa yanzu tun bayan rasuwar Yusuf, kuma shima yana dan business dan Abdul yarone da yasan ciwon kansa, ko lokacin da yake Argungu shik kula shagon kawu Mansur in ya shiga school kuma tsab zai dawo ya isko kayansa, haka Mami na turo mishi sosai duk da yana cewa ta barshi.
Alhaji shawarar a fara Gina mishi hospital ya bashi tun da medicine yake karantawa, hakan kuwa akayi dan itama Mami hakan tace nan suka sayi fili mai kyau aka fara tsara hospital ta gani a maganta inda kawu Mansur ke kula da ganin da yake yana gari.
*****************
B'angaren Asma'u kuwa yanzu bata da wata matsala dan ba'ayi mata sai in taje Wanda zuwa yanzu ta Saba da jarabar Iya Hari, Abdulrahim kuwa ya rik'e ta da Amana kamar yadda yayi alk'awari suna zaune lafia abinsu bakajin Kansu ko sabani suka samu suke shirya Kansu ba tare da wani yaji ba, Ramlah kuwa sai girma take abinta ga kulawar iyaye tana samu suna matuk'ar kula da ita da bata tarbiyar islama, tuni ta iya haruffa k'ananan surori tana 4 year, er lukuta da ita yanayin jikin irin na Asma'u ne, nan kad'ai suke kama.
A 'yan kwanakin nan mafarkin su Baba da Inna da Aunty Ameena, Abdool ya matsawa Asma'u har yakai ko kwanciyar rana tayi sai tayi, hakan yasa hankalinta ya koma gida baki d'aya, yanzu kam ta shirya runkarar Baba duk da tsawon lokaci bai nemata ba, amma tana fatan idan taje ya yafeta ya maida mata iyalanta, hakan yasa ta tunkari Abdulrahim da maganar son zuwa gida, hakan yayi mishi dad'i sosai dama ya dad'e yana bibiyarta suje tana cewa ba yanzu ba, suka tsara zasuje k'arshen sati.