← Book details Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 53

Sashe 29

Abdulmajid Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Taci gaba cikin murtuk'e fuska har iya yau "to ba zamu lamunci wannan sakarcin ba ya zama wajibi ayiwa tukkar hanci gudun abinda zaije ya dawo, kuma ya zama darasi ga duk mai niyyan aikata irin abinda sukayi" nan ta kira sunayensu jiki a sanyaye suka hau gaban Assembly duk jiki a Mace, nan aka umurci sajen yayi musu 30 lashes and then labour master ya yanka musu field mai girma gashi schools tayi haki ko'ina, tare da anshe musu prefect ship nasu da tabbacin duk wacce ta k'ara kwantanta hakan to za'ayi withdrew nata ne kawai kuma ba dawowa ko waye ubanta ko, sannan taja kunnen junior akan hakan bazai zama dalilin su raina senior nasu ba, su basu respect a matsayinsu na na gaba dasu, duk wacce aka kawo da laifin raina senior tofa zata fuskanci hukunci.

Da haka taro ya watse junior sai murna suke sun samu freedom, yayin da Senior suka shanye jinin jikinsu.

K'ara kiran Ramlah ta bata hak'uri akan abinda ya faru tare da bata tabbacin hakan bazai sake faruwa ba, a mtsayinta na new comer kada ta tsorata tace ba zata dawo ba, daganan suka wuce class don gudanar da pref, tun daga ranar komai ya dawo normal ba wani seniority a school d'in tuni su Safara'u suka shiga taitayinsu suka kama Kansu.

Sannu a hankali Ramlah ta fahimci boarding da rayuwar boarding, ta saba da ita a yadda take, bata wani sha wahala dan duk k'uncin rayuwar boarding tafi ta gidan iya Hari saidai tana kewar baffa da mami da uwa uba d'an binni mai gilashi, kullum suna tare da Nihal ita kad'aice k'awarta, ba Momy ba Darling duk da dinbin masu son k'ulla alaka da ita da takeda.

***************

B'angaren Zainab kuwa ta Dage gurin Neman fili a zuciyar Dr kuma da alama tayi nasara, don Zee mutum CE mai kulawa da nuna damuwarta akan Abu, tun Abdool bayajin komai game da ita har yanzu yakai yana jinta a ranshi soyayya tsabtatacciya suke gudanarwa kowanne na kaf kafa da d'an uwansa.

Lokacin da ta gayama Waleed ya shiga tashin hankali dan harga Allah yana k'aunar Zainab, saidai dole ya hak'ura don yanason farincikinta, fatan Alkhairi yayi mata, itama tayi masa fatan dacewa da mafi alkhairi.

****************

*End of month*

Tsaf su Mami suka shirya zuwa visiting d'insu Ramlah cike da provision kaman ba'a zo musu last month da irinsa ba (ni kuma nace koya zasuyi dashi oho) Abdool ne ke driving cike da nishad'i zaije yaga Ramlatunsa, su Husna sai zumud'i suke zasuga Aunty's.

Tun gate Ramlah ta tsinkayo aiko da gudu ta kwasa taje garesu, Nihal sai k'urarta ta hanga itama nan ta bita da nata gudun.

Tasa isa jikin Abdool ta fad'a tare da sakin...........

_Fatan Alkhairi masoya barkanmu da Sallah, barka sake saduwa_🙋🏾

💄 Meryerm Abdool💄
[9/5, 11:49 PM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

```😱 Wallahi i'm so speechless, bansan da wane word zanyi amfani na gode maku ba friends, kun nunan k'auna sosai, kunyi min k'ara nagode da birthday wishes naku, Allah yabar zumunci da k'auna Ameen👏🏽💋```

📝 *Episode* 166--170

Tare da sakin kuka "subhanallah Ramlah kuka again menene kuma ko an k'ara dukanki ne?" shiru tayi tare da lafewa, yayi dai2 da isowar Nihal da murnan ta, ta rungume Mami "uhm ba'a mata komai bafa kawai dai tana murnan ganinku ne, kunsan munyi missing naku".

Dungure mata kai Mami tayi "tau parrot munji, aifa yanzu zaki fara surutun naki" sannan ta Shafa kan Ramlah "dota haka zaki dinga mana ko, aiko saimu daina zuwa tunda tayar maki da hankali muke, sai a ringa aiko maku Sale driver kawai".

" Aa Mami na daina baran k'ara ba, kinji Mamina?" Ta rungumeta, su Husna sai dariya suke mata, Abdool kuwa kallonta kawai yake yana murmushi, a haka suka k'arasa Filin visiting d'in.

Wani babban carpet suka shimfid'a aka zazzauna, abinci aka gabatar nan sukayi lunch gaba d'aya, sai nishad'i su Ramlah keyi, ji suke kaman a gida ake, daga nan aka shiga fira, sunata basu labarin School wahalarta da dad'inta, nan suka gangaro firar gida Mami ke gayamusu Auren da Abdool zaiyi.

Duk da k'aranci shekaru irin na Ramlah saida Abinda ya daketa a zuciya, amma dake tanada wayo saita waske, murmushi tayi tare da d'an tsalle.

"Allah Mami, waye matar?" Nihal kam kwab'e fuska tayi tare da turo baki, Abdool kam ji yayi ba dad'i duk sai yaji wani iri.

"Auntynki ce fa Zainab".

"Lah! Aunty Zainab? Wlh nayi murna sosai Yaya, pls d'an kira mana ita mu gaisa Yaya"

Shidai baice komai ba sai kallonta yake, Nihal sai jifanta da harara take irin ta bata Haushin nan (oh su Nihal akwai aiki kenan) Mami kam sai murmushi take ba kad'an ba Ramlah ta burgeta, saidai dama tasa hakane zai kasance dan tasan ai yarinya ce da wuya ta damu tunda ko ma'anar auren bata sani ba.

"Kaji Yaya" ta k'ara fad'a hakan yasa dole ya kira mata ita, aiko da murna suka gaisa, hadda su Nihal duk sun gaisa ta tare da tambayansu karatu.

Zainab ta yadda da Ramlah yarinyace sosai kamar yadda Abdool ke fad'a, ko a jikinta bata nuna ta damu ba hadda kiranta da Aunty, nan take ta sak'a a ranta zatayi zama mai kyau da Ramlah zata rik'eta kamar su Amal k'anninta, zata roki Allah ya yaye mata azabar kishi da takeda.

Anan suka wunin musu tun safe sai marece suka wuce, suka barsu da kewa, haka suka kwashi kayansu nik'i-nik'i sai hostel, Nihal kam tun tana mata fushi ganin bata kulata yasa ta ware sukaci gaba da sha'anin gabansu...

********************

Kwanaki sunja wata ya wuce tuni su Ramlah sun zana jarabawarsu anyi Hutu, an dawo gida cike da farinciki, sai kuma hada hadar biki da aka shiga basu can basu nan Nihal ma tuni anyi giving up, dan ta fahimci Aunty Zainab akwai kirki tuni suka saba da ita kullum suna mak'ale a waya, tuni sukayi sabo har ma da Amal kanwarta kusan sa'arsu ce, Baffa kamar yadda ya alkawaranta yazo ganin Ramlah ranar kuwa kamar ta koma cikinsa tana nanik'e dashi har dare bacci ne kawai ya rabasu, kashe gari ya koma da kukanta da komai na kar ya tafi, haka Mami ta cikasa da tsaraba, itama Ramlah ta bada tata akaiwa iya Hari da gwagwaninta da Aminiyarta Deluwa.

Komai aka saka masa lokaci to za'a yazo kamar wucewar iska, a yau dubban jama'a suka shedi d'aurin Auren Abdulmajid Auwal Sada da Zainab Salis Madaki, taro yayi taro can na hango Ango da abokansa su Hakeem k'irjin biki, su Ismael da sauran su, gefe d'aya su Alhaji Sada na hango su Baba, Ard'o ma ansha rawani, su kawu Mansur, su Dady Ayuba, Sani, salis, Rabi'u, Dadyn Hakeem, duk ba'a barsu a baya uban amarya ma baki har kunne tsabar farinciki taro dai mashaa Allah sai fatan Alkhairi.

Cikin gida na garzaya, ya cika ya batse dak'ar na zak'ulo Amarya subhanallah zanso Ku hasko Zee tayi kyau like take away, ni kaina sai daga baya na ganeta sanye take cikin wani Arnen code lace Red and golden, head, shoes, purse duk golden ne, anyi mata d'auri irin na Amare fuskar tasha make-up sosai irin na amare, sai k'amshi take zubawa kamar anyi barin perfume a jikinta.

Ido ta k'ara warewa dan ganin 'yan biki dakyau can na hango su Ramlah ansha ankon wani material black and silver su uku da Nihal da Amal, ware ido nayi nace su kuma wad'annan yaushe gari? Harara ta balla min "naki wasane ai tun ranar da aka fara even muka bayyana" ah lallai kunsha gari na fad'a tare da k'ara wa kafata iska, Uwar Amarya sai nan da nan ake da bak'i zuciyarta fal farincki ayau sun sauke wani nauyi d'aya rataya a kansu, sosai ta yaba da Ramlah don tun zuwansu yarinyar ta kwanta mata arai duk Wanda aka nunama ita a matsayin abokiyar zaman Zainab saiya yaba don dagani yariyar batada matsala ita kam batamaso ana nunata, sai sunne kai take tanajin kunya dan harga Allah mantawa take da auren.

Zuwa karshe 4:00p suka nufi giginya hotel inda aka gudanar da mother's day, last even nasu sai dare aka tashi inda su Ramlah suka rak'ashe kamar ba gobe, su Abdool kam basusan ma anyi ba, dan ana gama d'aurin aure suka d'auki hanya don gudanar da tasu walimar da Hakeem ya shirya musu.

Washe gari da saffafe motocin d'aukar Amarya suka sola hanya, bayan tasha nasiha sosai daga iyayenta, sai kukan rabuwa take da gida duk soyayyarta da Abdool.

2:00pm a Kd tayi musu gidan Mami suka sauka bayan sunci susha an dank'a amanarta ga surukar tata, daganan Mimi da k'awayenta sukayi musu jagora zuwa gidanta dake unguwar malali Wanda Abdool ya kama dan yace gidan sa na cikin asibitinsa ba yanzu zasu tare ba sai ya an tashi bude hospital din gaba d'aya.

Gidane matsakaici mai kyau dashi, sosai danginta suka yaba, har kuryar d'aki kan gadonta sannan suka barta da k'awayenta suka koma gidan Mami inda sukayi masauki.

Haka k'awayenta suka sakata gaba da tsokana yaudai gata ga Dr tsami yakar, shiru tayi musu tanata murmushi Allah dai tasan farincikinta a yau, yau gata gidan Aure kuma da masoyin rayuwar ta Dr Majeed......

Manage

💄 Meryerm Abdool💄
[9/8, 12:01 AM] 💄Meryerm Abdool💄: 🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬
🖤 ```ABDULMAJEED``` 🖤
🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬🇳🇬

✨ *Servant of Majesty* ✨

Na
💄 _Meryerm Abdool_ 💄

© *Pure moment of life writers*
P.M.L💪🏽

(We don't just entertain and educate we touch the heart❤ of the readers📝)

```SAKI KOWA KAMA ALLAH, YI SOYAYYA DOMIN ALLAH, KAYI KIYAYYA DOMINSA, KA YARDA DOMINSA, YI FUSHI DOMINSA, KA JUYA BAYA DOMINSA, KAI KOMAI MA YA ZAMO DOMINSA ZAKACI RIBAR RAYUWA```

Small quote👌🏻

📝 *Episode* 171--175
Chapter 29 · 0% Book details