← Book details Zurfin Ciki Part 1 - 4 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 63

Sashe 63

Zurfin Ciki Part 1 - 4 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Sai da suka yi
tsiya da qyar bishira ta lallasheta ta yarda ta
bada fitsarin.

Rungume likitan yaya lokacin da
yake fada masa ciki ne in dai har fitsarinta ne.

Afalo gaban bishira da yara abba ya rungume
ummi yana murna, ji tayi tamkar tsokana amma
ganin ya zauna yana ta buga waya yanata
yadawa ta amince cewa gske ne.

Don haka ta
tashi ta shiga dakinta tayi alwala tazo tayi nafila
raka'a 2 cikin kuku take godewa Allah tare da
addu'ar ya raba lpy.

Ya bata mai albarka.

Tsohuwa ma kuka ta saka lokacin da labarin ya
riske su.

Ummi taga gata musamman daya
kasance cikin yazo da kumburi tayi sumtum.

Duk
kowa ya tsorata sbd tunanin ko hawan jininta ne
ya tashi.

ALLAH cikin Ikonshi data tashi haihuwa
saita santalo danta cikin gajeriyar nakuda, sak da
abba kwabo da kwabo.

Rungume ummi abba yayi
don murna, sunan alhaji babba ya sake maida wa
kuma walid din dai suke kiranshi.

Watan yaron
bakwai ummi ta sake rasa kanta, kuka wiwi ta
dinga yi shiko abba murna kamar yayi rawa.

Tasake samun da namiji inda yaci sunan alhaji
karami suka sa masa hibban.

Haka suka ci gaba
da rayuwa cikin haquri da juna, tsakanin bishira
da ummi, bama irin bishira saboda abba baya iya
boye son ummi.

Kan 'ya'yansu ahade ba kya
gane bambanci, bishira ta gane umma uwa ce
guda har da rabi, don haka hatta shawara saitaje
gurin umma kuma ko sabani suka samu da abba
gurin umma take zuwa.

Ita kuma umma ta dauke
ta babu bambanci da ummi, don bata taba fada
ma ummi sirrin bishira ba.

Sahura yanzun ta
yarda umma da alhaji sune rufin asirinsu, kuma
gatan Abba, bashi ma da yayi aure gidan dasu
ummi suka tashi nan ya zauna.

Dangin bishira
yanzun sunga bishira ta samu natsuwa sun
sulhunta.

Abba agurin aikinshi yana ta samun ci
gaba, lamuran sai godiya.

Ummi tashafa addu'ar
da takeyi sannan tamiqe tana linke dardumar tace
kallon me ka ishe ni dashi ne ya Abba, yace ina
kallo ne na kusan samun da na uku wannan
karon takwara zan ma kaina.

Ummi ta jefa masa
dardumar hannunta, daina min fata ni, yace ban
karanci likitanci ba amma ni likitanki ne.

Ta fada
kanshi, ya rike fuskarta yana kallonta cikin ido,
ummi lokuta da yawa ina zama inta tuna da,
musamman in na kalli 'yan yaranmu wadanda
suke matuqar kama dani, tace me kafi tunawa a
baya?

Yace, yanda kikayi ta kirana awaya kina
tsara ni suhaylan kaduna.

Suka sa dariya.

Ni kam
nafi tuna yanda ni da kai muka yi ta 'ZURFIN
CIKI' dason juna.

Yace Allah yabarni da ke har
abada matata.

Ta kwantar da kanta
amakwancinta ''Amin mijina''.

Muma Allah ya bar
mu da masoyanmu har gidan aljanna, ya bamu
lafiya dazama lafiya.

Ya zaunar mana da 'yan
uwanmu lafiya, Amin ya rabbi. ** ** ** ** Bayan
shekara goma naje nasamu yaya Abba nace
inason muhibba yace badamuwa yabani kyautar
gida da mota.

Ummi kuma ta hada mun kayan
lefe saboda namijin kokarin danayi na rubuto
maku wannan littafin aka daura mana aure da
muhibbata muka tare muka cigaba da soyayya
fiye dasu ummi ma.
* ,
Times New Roman
Times New Ro
Calibri
Calibri
!%),.:;>?]}
$([{
SummaryInformation
DocumentSummaryInformation
WpsCustomData
TECNO LD7
WPS Office
dcdd1e012b26437ea5236115941f8b17
Chapter 63 · 0% Book details