Sashe 12
Zurfin Ciki Part 1 - 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"sleeping beauty" tayi mika sannan ta
bude ido,ya ce"a tashi ayi sallah ko?gashi sai
kinyi wanka ko?" ta ce,"eh." ya ce, "to tashi ki
gani gari ya soma haske." zani taja ta daura
daura ta nufi waje. da kallo tabi tsakar
gidan,sannan ta dawo dakin Abba.bazan iya jan
ruwa daga cikin rijiya ba. ya fito da sauri yaja
mata sannan yakai mata bandakin,ya dawo yayi
taja yana cika robobin ruwanta.sai da ya cika
mata komai,sannan ya koma dakin. lokacin ta
idar da sallah.ya dauko Alqur'ani mai girma ya
zauna gabanta,ya ce "madam zamuyi karatu." ta
dube shi tareda yatsina fuska,"wallahi bacci
nakeji."ya ce,"daure muyi ko aya biyar ce," ta ce
cikin shagwaba,"ni biyu." ya ce,"to bismillah,mu
fara ta sama ko ta kasa?" ta ce,"ni kam ko ta
ina, don haka sai ya soma mata daga bakara
yana yi tana maimaitawa,aya biyu kusan minti
ashirin ta ce, "zan kwanta." Ya aje kur'ani ya
kmama hannunta,zo muje kicin mu gani me zamu
nema.dan dole ta bishi zuwa kicin din.suka tsaya
suna kallm kayan, tukwane ne zuwa kuloli da
sauran tarkace,sai risho.ta dube shi cikin yanayin
tsausaya ma kanta. tace, sun qi sai min gas
cooker wai gidana ba flate ba ne bai dace da gas
cooker ba. ita ko anti aisha an sai mata, kayan
girkita ma duk yan chaina. tausayinta ya tsirga
ma abba, ya jawo ta jikinshi ya rungume, kada ki
damu bishira, duk abin da a ke sai ma yar gata
xan sai miki, matsawar Allah ya hore min. ya
janyo kwalin risho din ya ciro shi, ya hada yace
xan siyo lagwani da kalanxir kenan ko? tace eh.
ya miqe bari na dawo. tace to. ta nufi daki ta
fada kan gadanta taci gaba da baccinta, shi kam
gidansu ya nufa. tun daga nesa ya hango ahj
babba xai shiga dakin waje, in da aka sauki baqi
maxa, da alama ahjn ya hango shine shi yasa ya
tsaya a bakin qofar. abba yana cike da fara'a ya
rusuna xai gaida ahj shi kuma ya miqa masa
hannu, dan haka sai abban ya kama suka yi
musabaha. ahj yace Alhamdulillahi abbana, ka
xama mutun, sai ayi ta hakuri da rayuwa. abba
ya sunkuyar da kai yana tambayar kanshi ko
manya suna ganewa ne in kayi auratayya da
matanka? ahj ya katse shi da cewa, ya kwanan
iyalin taka? tare suka shiga gun baqin, yana
gaida su ya fito xuwa cikin gidan. yana leqawa
dakin umma bata ciki, sai baqi. wata uwani
dake
matsayin abokiyan wasansu tace ango amarya ta
koro ka ne? yace, keni karki dame ni, ina umma
na? umma daga kicin tace, gani nan dana, xo
qyale su uwani. gurinta ya nufa yana cewa,kina
kicin ashe? tace, eh ina hada ma baqi abin kari
ne. yace kalli yanda duk suka yi mana kaca kaca
da gidan,wannan in sun tafi sai kin sha aikin
tsaftace gidan.tace to yana iya?dole in gyara in
sun tafi,ai arxiki ne ma xuwan nasu.abba yayi
dan murmushi,sannanya canxa maganan da
cewa,umma galan din kananxir muke so.tace,ga
ma kananxir din can da ahj ya siyo jarka babba
wai saboda biki.nace yaushe girkin biki xai yiwu
da kananxir?shine na aje shi.sai kadau galan ka
cika.yayi murmushi.
Yace kai ahj akwai qoqari,
musamman lkcn bikin nan.umma tayi yar dariya
tare da cewa ko abinci fa baya iya tsayawa
yaci,in na masa magana sai yace bijin da guda
ina yaga ta cin abinci?abba ya girgixa kai,Allah
ya rama muku da mafificin alkairin da kuke
min,yasa ni ma in goya ku kamar yadda kuka
goya ni.tace amin abba ai muma kana yi mana
biyayya Allah yasa albarka a cikin auran, ya baka
yaya masu binka kaima.yace amin. ya isa gida da
kalanxir da lakwani ya samu ta koma bacci,dan
haka ya hada ya dora ruwan xafi ya juye cikin
plaks yaje ya ce ta shi mu karya. tayi juyi tare da
cewa sai an jima,dama tun jiya sun shigo da
biredi da kayan tea,shima sai ya sake
kwanciya.ya mannata jikinshi suka koma
bacci,goma da ishirin wayarsa ta tashe shi da
ruri. ya daga ahj ne ke san ganinsa qarfe sha
biyu.yace,ya sanme shi can kasuwa,ita ma ta
tashi.nan suka karya sannan yayo wanka ya tafi
kiran abba.kaya ne ya ba shi da kudin mota, yace
ya kawo ma baqi yan xamfara da xasu koma gida
yace ka tabbata ka dauki shatar mota har
Zamfara abba ya ce to.sai da ya samu motar
sannan yaje ya loda su suka daga,suna ta
godiya.yau satinsu daya cir umman shi ke kai
masu abinci,sannan ita kuma ya shigo da kayan
marmari,sai kaji ko tsire da balango.abba ya
shirya tsaf cikin qananan kaya xai tafi shago,yace
madam yau fa abinci xaki yi mana,kin san
abokaina su ahmad xasu xo muci abinci,in yaso
daga nan sai mu wuce gaisuwan surukai gidanku
a matsayin kina amarya wanda xaki soma girki
yau, me xaki dafa mana? ta tashi xaune duk abin
da ka ke so.dadi ya rufe shi,kowanne dai ki mana
fatana shine ki birge abokaina.tace an gama.
yace to bari inje xan turo yaran shago da abinci
da cefane tace to, har ya tafi kuma ya dawo
yace, xan biya in turo miki ummi,tace saidai in
fati.yace,ummi tafi fati hanxarin aiki fa.tace eh
nafi son fatin.kamar kullum sai da ya soma shiga
gun ummarshi suka gaisa ta tambaye bishira,
yace lafiyi lau.yaci gaba da cewa, yau nema xata
soma girki,nace na turo mata ummi tace wai
fati.umma tayi murmushi, sannantace kai ko
yaushe xata so a tura mata ummi umma tace ina
xata so a tura mata ummi? ita fa ba natsuwa
gareta ba.abba yace, duk da haka tafi fati
hanxarin aiki. umma tace,yanxu dai tura mata
fatin.ka ko sai kayan abinci?yace ina fa,yanxu dai
xan je bin wasu yan kudadena.tace ina xuwa
baqar leda ta ciro a cikin adakan suturunta,taxo
ta xauna sannan ta umurce shi da ya xauna.ta
miqa mashi ledan tace,kwance ka gani.abba ya
kwance ledan yana cewa menene a ciki ummana?
kudin da yayi arba da su su suka bashi amsa
yace,umma kudin nan fa?tace gudunmawa ce da
jama'a sukayi ta bani,ka gansu nan.yanxu ka je
ka siyi kayan abinci da su.abba yayi dariya,
sannan ya kullesu ya miqa mata tare da cewa.
Allah ya kyauta in amsan makh kudi, ki boye
abinki. tace bana son muyi ta jan magana
abba,kawai ka riqe kudin nan.muryan tsohuwa ne
ta katse su,inda take cewa yanxu ke suwaiba
hakan da ki ka yi adalci ne? yar gudunmuwar da
ki ka samu kiba mai sunan malam duka, ummin
fa? umma tace,to tsohuwa ummi me xatayi da
kudi yanxun?abba yace kai wannan matan sa
idan ki ya gota misali.
Tace kai tafi can,ni rufemin
baki,ke kuma suwaiba da kike cewan haka ba kya
siyan mata yan tukwane da kwanonin nan na yayi
maigida cika duba ne ku ke ce musu ko ci bari
kallo? umma da abba suka sa dariya,tsohuwa ta
sake jin haushi ta ce eh dole ku min dariya tunda
kema kin xama shi,ai sai kiyi ta bashi naki ne ba
nawa ba.umma tace yi haquri tsohuwa, gani nayi
nan gaba muna sa ran abba shi ne xai ma ummi
kayan dakin ma gaba daya tace,me kika ce?tab
mai sunan mlm ne xai yi wa takwara wani abin
axo a gani?shi da ya tsaneta.abba yace,in lkcn
yaxo ke kya yi ma.ta tafa hannu cikin jin
matuqan takaici ta ce,a gayawa mai xuciya ba
mai dukiya ba,dan ko xan mata.ta nufi dakinta
tana fada.umma tace,tashi abba,dauki kudin nan
kaje. yace,wallah umma bari dai in dauka tunda
kin matsa,amma ba xan amsa duka ba.ya qirga
dubu uku,tace ka qara dan kusan dubu tara ne
kudin,yace haka ma ya isa ki adana sauran.tace
shi kenan. daga nan kasuwa ya wuce,ya sai
kayan abinci.bayan ya amso wadansu kudaden
shi ya hada ya kai mata.
Sannan ya yi cefanen
kayan miyan rigijif da nama ya aika yaran
shago.dama kafin ya bar layin ya shiga gun
umman bashir ya gaisheta.da tana ta bace bacen
rai,sannan da yace umma ina fati? taje xata taya
bishira aiki ne.sai ta washe baki,tan bandaki.
yace to in ta fito ki tura mata ita.ya fice
abinshi.biyu saura ya iyo gidan,tun a tsakar gidan
yake jin qamshin shinkafa.ya isa kicin din tuni ta
sauke shinkafa sai miya.yace ki xubama yaran
shagona.ya dubi fati da ke yanka latas yace,in
kin gama jamin ruwan wanka a rijiya.tace to.yana
daki yana sa kaya yaji sallamar abokanshi.da
sauri ya fito, suna ta yi masa tsiya ango kasha
gyara, munxo dibar girki. abba ya bude musu
falo,falan yaji jeran samiru abin yayi na xamanin,
ga kujeru suka xauna suna yaba dukiyar da aka
xuba cikin falon.ya fito yace bishira ta saka hijabi
taje su gaisa.ya dauki abinci ya kai musu,sannan
yasa fati takai filet da ruwan sha,shi kuma ya
koma daki dan qarasa saka kaya.a xatam shi xai
samu sunyi nisa da cin abincin amma sai me?
dukkansu su shida kowanne filet din gabansa
shaqe da abinci da nama,ga cokali a
hannunsu,amma kowannansu juya abincin
yake,yace a,a kuci mana kai muke jira ka bude da
addua.tsaki yayi, yasan halin ahmad gun
xolaya,dan haka sai yace muktar kuci abincinku,in
kun bi ta ahmad xai ta bata mana lkc.cokali ya
dauka shima ya xauna kusa da sunusi ya ce mu
ci tare.take ya yatsina fuska tare da dawo da
abincin ya xube shi kan ledar yana tande
harshansa.dan danan gishirin da ya kama masa
harshe ya ragu,cike da kunya ya dubi abokanan
nasa suna ta dariyar da suke gimtse.da farko ya
dubi sunusi,wai gishiri ka qara ne?sunusi ya
ce,qila dai gishirin nan da bakin buhu ta
xufa.muktar yace dubi gaban rigata ni da shegen
kwandayi na tura nama a baki na tauna ya qwace
saboda tsananin qarfi ya dawo ya fado min
jiki.abba ya miqe cikin damuwa ya ce bari in
maku wata miyar. ahmad yace a,a duk yunwa
muka debo, inda yaji da mai a bamu muyi maneji.
abba ya fito xuwa kicin.fati ce xaune da nata
abincin tana ta juya cokalin.
bude ido,ya ce"a tashi ayi sallah ko?gashi sai
kinyi wanka ko?" ta ce,"eh." ya ce, "to tashi ki
gani gari ya soma haske." zani taja ta daura
daura ta nufi waje. da kallo tabi tsakar
gidan,sannan ta dawo dakin Abba.bazan iya jan
ruwa daga cikin rijiya ba. ya fito da sauri yaja
mata sannan yakai mata bandakin,ya dawo yayi
taja yana cika robobin ruwanta.sai da ya cika
mata komai,sannan ya koma dakin. lokacin ta
idar da sallah.ya dauko Alqur'ani mai girma ya
zauna gabanta,ya ce "madam zamuyi karatu." ta
dube shi tareda yatsina fuska,"wallahi bacci
nakeji."ya ce,"daure muyi ko aya biyar ce," ta ce
cikin shagwaba,"ni biyu." ya ce,"to bismillah,mu
fara ta sama ko ta kasa?" ta ce,"ni kam ko ta
ina, don haka sai ya soma mata daga bakara
yana yi tana maimaitawa,aya biyu kusan minti
ashirin ta ce, "zan kwanta." Ya aje kur'ani ya
kmama hannunta,zo muje kicin mu gani me zamu
nema.dan dole ta bishi zuwa kicin din.suka tsaya
suna kallm kayan, tukwane ne zuwa kuloli da
sauran tarkace,sai risho.ta dube shi cikin yanayin
tsausaya ma kanta. tace, sun qi sai min gas
cooker wai gidana ba flate ba ne bai dace da gas
cooker ba. ita ko anti aisha an sai mata, kayan
girkita ma duk yan chaina. tausayinta ya tsirga
ma abba, ya jawo ta jikinshi ya rungume, kada ki
damu bishira, duk abin da a ke sai ma yar gata
xan sai miki, matsawar Allah ya hore min. ya
janyo kwalin risho din ya ciro shi, ya hada yace
xan siyo lagwani da kalanxir kenan ko? tace eh.
ya miqe bari na dawo. tace to. ta nufi daki ta
fada kan gadanta taci gaba da baccinta, shi kam
gidansu ya nufa. tun daga nesa ya hango ahj
babba xai shiga dakin waje, in da aka sauki baqi
maxa, da alama ahjn ya hango shine shi yasa ya
tsaya a bakin qofar. abba yana cike da fara'a ya
rusuna xai gaida ahj shi kuma ya miqa masa
hannu, dan haka sai abban ya kama suka yi
musabaha. ahj yace Alhamdulillahi abbana, ka
xama mutun, sai ayi ta hakuri da rayuwa. abba
ya sunkuyar da kai yana tambayar kanshi ko
manya suna ganewa ne in kayi auratayya da
matanka? ahj ya katse shi da cewa, ya kwanan
iyalin taka? tare suka shiga gun baqin, yana
gaida su ya fito xuwa cikin gidan. yana leqawa
dakin umma bata ciki, sai baqi. wata uwani
dake
matsayin abokiyan wasansu tace ango amarya ta
koro ka ne? yace, keni karki dame ni, ina umma
na? umma daga kicin tace, gani nan dana, xo
qyale su uwani. gurinta ya nufa yana cewa,kina
kicin ashe? tace, eh ina hada ma baqi abin kari
ne. yace kalli yanda duk suka yi mana kaca kaca
da gidan,wannan in sun tafi sai kin sha aikin
tsaftace gidan.tace to yana iya?dole in gyara in
sun tafi,ai arxiki ne ma xuwan nasu.abba yayi
dan murmushi,sannanya canxa maganan da
cewa,umma galan din kananxir muke so.tace,ga
ma kananxir din can da ahj ya siyo jarka babba
wai saboda biki.nace yaushe girkin biki xai yiwu
da kananxir?shine na aje shi.sai kadau galan ka
cika.yayi murmushi.
Yace kai ahj akwai qoqari,
musamman lkcn bikin nan.umma tayi yar dariya
tare da cewa ko abinci fa baya iya tsayawa
yaci,in na masa magana sai yace bijin da guda
ina yaga ta cin abinci?abba ya girgixa kai,Allah
ya rama muku da mafificin alkairin da kuke
min,yasa ni ma in goya ku kamar yadda kuka
goya ni.tace amin abba ai muma kana yi mana
biyayya Allah yasa albarka a cikin auran, ya baka
yaya masu binka kaima.yace amin. ya isa gida da
kalanxir da lakwani ya samu ta koma bacci,dan
haka ya hada ya dora ruwan xafi ya juye cikin
plaks yaje ya ce ta shi mu karya. tayi juyi tare da
cewa sai an jima,dama tun jiya sun shigo da
biredi da kayan tea,shima sai ya sake
kwanciya.ya mannata jikinshi suka koma
bacci,goma da ishirin wayarsa ta tashe shi da
ruri. ya daga ahj ne ke san ganinsa qarfe sha
biyu.yace,ya sanme shi can kasuwa,ita ma ta
tashi.nan suka karya sannan yayo wanka ya tafi
kiran abba.kaya ne ya ba shi da kudin mota, yace
ya kawo ma baqi yan xamfara da xasu koma gida
yace ka tabbata ka dauki shatar mota har
Zamfara abba ya ce to.sai da ya samu motar
sannan yaje ya loda su suka daga,suna ta
godiya.yau satinsu daya cir umman shi ke kai
masu abinci,sannan ita kuma ya shigo da kayan
marmari,sai kaji ko tsire da balango.abba ya
shirya tsaf cikin qananan kaya xai tafi shago,yace
madam yau fa abinci xaki yi mana,kin san
abokaina su ahmad xasu xo muci abinci,in yaso
daga nan sai mu wuce gaisuwan surukai gidanku
a matsayin kina amarya wanda xaki soma girki
yau, me xaki dafa mana? ta tashi xaune duk abin
da ka ke so.dadi ya rufe shi,kowanne dai ki mana
fatana shine ki birge abokaina.tace an gama.
yace to bari inje xan turo yaran shago da abinci
da cefane tace to, har ya tafi kuma ya dawo
yace, xan biya in turo miki ummi,tace saidai in
fati.yace,ummi tafi fati hanxarin aiki fa.tace eh
nafi son fatin.kamar kullum sai da ya soma shiga
gun ummarshi suka gaisa ta tambaye bishira,
yace lafiyi lau.yaci gaba da cewa, yau nema xata
soma girki,nace na turo mata ummi tace wai
fati.umma tayi murmushi, sannantace kai ko
yaushe xata so a tura mata ummi umma tace ina
xata so a tura mata ummi? ita fa ba natsuwa
gareta ba.abba yace, duk da haka tafi fati
hanxarin aiki. umma tace,yanxu dai tura mata
fatin.ka ko sai kayan abinci?yace ina fa,yanxu dai
xan je bin wasu yan kudadena.tace ina xuwa
baqar leda ta ciro a cikin adakan suturunta,taxo
ta xauna sannan ta umurce shi da ya xauna.ta
miqa mashi ledan tace,kwance ka gani.abba ya
kwance ledan yana cewa menene a ciki ummana?
kudin da yayi arba da su su suka bashi amsa
yace,umma kudin nan fa?tace gudunmawa ce da
jama'a sukayi ta bani,ka gansu nan.yanxu ka je
ka siyi kayan abinci da su.abba yayi dariya,
sannan ya kullesu ya miqa mata tare da cewa.
Allah ya kyauta in amsan makh kudi, ki boye
abinki. tace bana son muyi ta jan magana
abba,kawai ka riqe kudin nan.muryan tsohuwa ne
ta katse su,inda take cewa yanxu ke suwaiba
hakan da ki ka yi adalci ne? yar gudunmuwar da
ki ka samu kiba mai sunan malam duka, ummin
fa? umma tace,to tsohuwa ummi me xatayi da
kudi yanxun?abba yace kai wannan matan sa
idan ki ya gota misali.
Tace kai tafi can,ni rufemin
baki,ke kuma suwaiba da kike cewan haka ba kya
siyan mata yan tukwane da kwanonin nan na yayi
maigida cika duba ne ku ke ce musu ko ci bari
kallo? umma da abba suka sa dariya,tsohuwa ta
sake jin haushi ta ce eh dole ku min dariya tunda
kema kin xama shi,ai sai kiyi ta bashi naki ne ba
nawa ba.umma tace yi haquri tsohuwa, gani nayi
nan gaba muna sa ran abba shi ne xai ma ummi
kayan dakin ma gaba daya tace,me kika ce?tab
mai sunan mlm ne xai yi wa takwara wani abin
axo a gani?shi da ya tsaneta.abba yace,in lkcn
yaxo ke kya yi ma.ta tafa hannu cikin jin
matuqan takaici ta ce,a gayawa mai xuciya ba
mai dukiya ba,dan ko xan mata.ta nufi dakinta
tana fada.umma tace,tashi abba,dauki kudin nan
kaje. yace,wallah umma bari dai in dauka tunda
kin matsa,amma ba xan amsa duka ba.ya qirga
dubu uku,tace ka qara dan kusan dubu tara ne
kudin,yace haka ma ya isa ki adana sauran.tace
shi kenan. daga nan kasuwa ya wuce,ya sai
kayan abinci.bayan ya amso wadansu kudaden
shi ya hada ya kai mata.
Sannan ya yi cefanen
kayan miyan rigijif da nama ya aika yaran
shago.dama kafin ya bar layin ya shiga gun
umman bashir ya gaisheta.da tana ta bace bacen
rai,sannan da yace umma ina fati? taje xata taya
bishira aiki ne.sai ta washe baki,tan bandaki.
yace to in ta fito ki tura mata ita.ya fice
abinshi.biyu saura ya iyo gidan,tun a tsakar gidan
yake jin qamshin shinkafa.ya isa kicin din tuni ta
sauke shinkafa sai miya.yace ki xubama yaran
shagona.ya dubi fati da ke yanka latas yace,in
kin gama jamin ruwan wanka a rijiya.tace to.yana
daki yana sa kaya yaji sallamar abokanshi.da
sauri ya fito, suna ta yi masa tsiya ango kasha
gyara, munxo dibar girki. abba ya bude musu
falo,falan yaji jeran samiru abin yayi na xamanin,
ga kujeru suka xauna suna yaba dukiyar da aka
xuba cikin falon.ya fito yace bishira ta saka hijabi
taje su gaisa.ya dauki abinci ya kai musu,sannan
yasa fati takai filet da ruwan sha,shi kuma ya
koma daki dan qarasa saka kaya.a xatam shi xai
samu sunyi nisa da cin abincin amma sai me?
dukkansu su shida kowanne filet din gabansa
shaqe da abinci da nama,ga cokali a
hannunsu,amma kowannansu juya abincin
yake,yace a,a kuci mana kai muke jira ka bude da
addua.tsaki yayi, yasan halin ahmad gun
xolaya,dan haka sai yace muktar kuci abincinku,in
kun bi ta ahmad xai ta bata mana lkc.cokali ya
dauka shima ya xauna kusa da sunusi ya ce mu
ci tare.take ya yatsina fuska tare da dawo da
abincin ya xube shi kan ledar yana tande
harshansa.dan danan gishirin da ya kama masa
harshe ya ragu,cike da kunya ya dubi abokanan
nasa suna ta dariyar da suke gimtse.da farko ya
dubi sunusi,wai gishiri ka qara ne?sunusi ya
ce,qila dai gishirin nan da bakin buhu ta
xufa.muktar yace dubi gaban rigata ni da shegen
kwandayi na tura nama a baki na tauna ya qwace
saboda tsananin qarfi ya dawo ya fado min
jiki.abba ya miqe cikin damuwa ya ce bari in
maku wata miyar. ahmad yace a,a duk yunwa
muka debo, inda yaji da mai a bamu muyi maneji.
abba ya fito xuwa kicin.fati ce xaune da nata
abincin tana ta juya cokalin.