Sashe 50
Zurfin Ciki Part 1 - 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Alhaji yace, tafi gidan kahadasu kayi masu nasiha, Abba yace ai baza ta tsaya ba, wannan yarinyar fa sai dai addu'a ni in nagaji kawai hakura za ayi, umma tace bana son jin wannan zancan, alhaji karami yace ai gskiyarshi ne, shi yasan irin zaman dayake da ita.
Alhaji babba yace, ai kuma darajar mahaifinta za aduba, da mutuncinsa, Abba yace ai dama alhaji ni banda mahaifinta da tuni nayar da kwallon mangwaro na huta da kuda.
Umman tace je ka gida Allah ya kyauta.
Nan dai ya musu sallama yanufi gida.
Ummi da gske tsoro ne da ita, da rana in ba kowa bta damuwa, amma da dare tfi son tdinga jiyo motsin bishira koda habaicin dta sabayi mata.
Soro taje ta tsaya tana yi tana leka waje, can ta hango bishira, don haka takoma daki ta kullo kofa aranta ta ce kada tazo tayi min duka.
Ummi tna jiyota lokacin data shigo tana cewa wllh kan yarinya zan rama marina, wannan dole ne koba dade saina ramashi.
Abba kan bai nufo gida ba, shagonsa ya wuce lokacin goma ta gota, yaran sunyi shirin tafiya, don haka ya amshi makullin ya shiga shagon saman teburin da suke yin yanka da guga ya hau ya zauna.
Tagumi ya zuba hummu biyu tare da sauke wata ajiyar zuciya mai karfi, me yasa ummi ta furta kalmar data tuna mishi cewa bata sonshi?
Sakankancewa dayanda ummin kenuna mishi yasa shi jin kamar sonsa take ashe dai shi yake shermenshi.
Ya tuno wani labari yaya tabaji na wani mutum da aka ara masa mata wadda bata sonsa, tazo tazauna dashi tsawon shekaru kuma tayi masa biyayya matuka.
Ga 'ya'ya sun haifa yaran sun yi girma sosai, suma sun zama magidanta, sai wata rana mutumin nan suna hira da matar, yace oh, wance dafa ba kya sona, yanzun gashi harmun tsufa kin manta dawata kiyayyah.
Tadubeshi, inji wa yace maka na manta?
Biyayya kurum nake maka amma har gobe bana sonka.
Abba yajinjina kai, lallai dole ne ya nutso, yadaina tunanin ummi tana sonshi kokuma zata soshi, shidai da kaddarar sonta tafada mishi sai yayi ta addu'a Allah ya bashi hakurin jure zama da ita ahaka.
Bai san adadin lokacin daya dauka awaje ba kuma baisan adadin tunanin dayayi ba.
Daga karshe yarufe shagon yanufi gida.
Ganin yanda garin yayi tsit shine yasa shi kallon agogon hannunshi, daya da minti shabakwai, lallai lokaci yatafi.
ZURFIN CIKI book 4 part 10
ZURFIN CIKI book 4 part 10
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:55
Yanufi dakin bishira aranshi yce da wanda yake
kinka gara mai sonka ko mahaukaci ne.
Gdon
yahau tagefe ya kwanta suka saka muhibba
atsakiya, ummi kuwa duk tsawon lokacin nan
tkasa bacci domin bata ga shigowarshi ba.
Idonta
biyu har sai daya shigo ta leka ta windo tana
kalloshi har yashiga dakin bishira ya rufo kofa,
sannan ta kwanta tare dayin ajiyar zuciya.
A fili
tace ina ga fa har dani alaifin nan, amma bari
gari yawaye inba shi hakuri durkusa ma wada ai
ba gajiyawa bane.
Bishira tafarka cikin dare taga
Abba kwance hannunsa na dama dore kan jikin
'yarsu, ta tsura mishi idanu tana son mijinta
sosai.
Ban dahaka data kaishi koto ya bata
takardarta koda mahaifinta xaimata baki
sanadiyar haka, amma shi yanzun yadaina sonta.
Takai hannu tadora a kumatunshi, ahankali
yabude idanu, suka kura majuna ido yace bishira
me yasa kike yin abinda zai samu mu samu
sabani bayan kinsan sone ya hadamu?
Idanuwanta suka kawo ruwa, Abba dane ka soni
kaji dani har alokacin ina ganin ba Wata mace
data kai ni dacen gwanin iya soyayya.
Amma
yanzun duk ka zuba ni a kwandon shara har kana
marina saboda ummi.
Ya ce, a'a ba sbd ummi na
mare kiba, saboda kin dukeni ne amma kiyi
hakuri.
Banason kina zubar da kanki a gurinta,
yawan fadanku zai sa raini ya shiga tsakaninku,
ni kuma ba zan so ta rainaki ba.
Kuma da kin
kwantar da hankalin ki ummi fa ba wai tana sona
bane, ita fa an matsa ma tane, kuma su umma da
kike zagi na rantse miki masoyan kine.
Ta ce
tokai kana son ummi ne ?
Ya dan yi jim, sannan
ya ce ai dai kin san yanda auran namu da ita
yakasance bagatatan bai dace ace kinma tsay
yin wannan tambayar ma.
Tadan yi shiru, zancen
nan ya shige ta bakamar yanda ta zata da farko
ba, ko dadin baki zaimata?
Sannan ta tuno da
ranar da fati tazo.
Ta labe taji koza suyi
zancenta sai taji suna ta hirarsu, acikin harar fati
ke cewa wai kuwa ya kuka kaya ne ummi?
Nasan
yanzun ai kin warke, kema kin goge.
Ta ce
damefa?
Fati tace, a'a ki gane mana, batun
kwanciya.
Ummi tace, kin san cewa yaya Abba ko
gadona bai taba kwana ba?
Fati tace kai haba?
Ummi tadinga yimata rantsuwa, tuno da wannan
sai bishira ta yarda mijinta ma baya son ummi,
don haka sai ta saki murmushi.
Yace, tunanin me
ki ke yi?
Tace da ina ga kamar dadin baki kake
min, amma dana tuno naji ummi tana fadama fati
wai baka taba ko kwanciya a gadonta ba, bare ka
hada jiki da ita sai na yarda.
Abba ya zaro ido, a
ina kika ji suna zancan?
Ta ce, a'a tazo mata
rakiyane naji suna maganar a soro.
Abba ya
girgiza kai.
Bishira tace, kuma da gske hakane,
yakai hannu yakama nata tafin hannun, wannan
wani sirri ne tsakanina da ummin.
Ynda ba zan
fada mata komai tsakanina dake ba, haka itama
zan sakaya nata sirrin, tadai fahimci hakane, don
haka sai ranta yayi mata dadi har ma ta baiwa
Abban kanta a daran.
Ynda taga yna rawar jiki ya
tabbatar ma ta ba wani angwanci da yayi, don
haka zuciyarta fes ta wayi gari.
Duk da cewa
abba ya tashe ta cewa taje tayi wanka harda
Allah yahadata amma tayi niyar baza tayi hakan
ba sai gari yayi haske.
Ummi ta fito don tanuna
mata cewa Abba ya kwana da ita.
Bishira an dafa
ruwan tea an kai falo sai wannan rawan kai ake
yi.
Sai data lura ummi ta dauko tsintsiya tasoma
sharar gidan kamar yanda tasaba, sannan tafito
da buta aka nufi bandaki, kai ko dankwali babu
aka yiwanka aka fito.
Gashi yna ta digar ruwa,
ummi ta fahimta kuma tagane cewa tayi hakan
don ta nuna mata ne.
Kuma taji zafi aranta
kamar ynda bishiran taso, ta amma azuciyar ta
sai tace na banza jiya nan yakora miki mari.
Lokacin da abba ya shigo gidan tagama shara
tana kwashewa, bai ko dubeta baya shige falon
bishira, kan ummi yasake daurewa, me yake
faruwane haka da zafi?
Ta tambayi kanta.
Data
koma daki tagumi ta zabga tana tunani ita da
suka yi kaca-kaca ma sun shirya bare ni?
Kamar
tabi shi har falon bishiran ta gaida shi, amma sai
tafasa.
Tazuba ido taga zai bar gidanne ba tare
daya leko dakinta ba?
Sun gama karin
kumallonsu tsaf yayo wanka don tafiya gurin aiki,
sai dai kayan dazai saka suna dakin ummi.
Ya
fito yanufi dakin.
Ciki- ciki yayi sallama ita kam
tsoro ne ya tsirga mata, tasake tambayar kanta
mekuma yafaru?
Ta amsa tare da gaida shi.
Nan
ma a ciki ya amsa, yadauki kayan sai dazai fita
sannan yace ba kya bukatar komai ko?
Tayi
karfin halin cewa sugata ceta kare.
Ya dube ta
furka tsuke me yasa baki fada minba?
Ta ce, na
manta ne, yace to sai kije gurin bishira da dibar
miki inzan dawo na siyo.
Ba kya neman komai da
rana ko?
Tace a'a sai nama kawai ya daga
murya, kullum ne ya zama dole a saka nama a
abinci?
Jikinta har bari yake don tsoro, ta ce a'a
yaja tsaki ya fita.
Ummi tasaka kanta cikin cinya
tana furta 'inna lillahi wa inna ilaihir raji'un.'
hawaye suka soma yi mata sintiri.KI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 11
ZURFIN CIKI book 4 part 11
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:57
Dadi tamkar yakashe bishira don tna labe tana
jinsu afalon ya saka kya yashirya tsaf, sannan ya
nufo dakinta don dauka jakar laptop dinshi.
Jin
sallamarshi tayi mza tashare hawaye sannan ta
amsa, yshigo ya dauko dari biyu ya aje mata
akan gdo, ga kudin maman nan kura, kada fati
tzo kifada mata baki kudin nama kullum tunda
har kin iya shaida mta cewa ban tba kwana
agadonkiba.
Kin kosa inkwanta dakene?
Yadauki
jakar yarataya sannan yayi mata wani kallo sama
dakasa, to banga gurin kwana agadon naki ba.
Hakanan banga abin kwanciya ajikinki ba, yafice
yabar ummi tsaye tazaro idanunta cikin matukar
al'ajabi da kunya.
Ina ya Abba yaji zancen nan?
Kodai fati ceta fada masa?
Wata zuciyar tace fati
baza ta iyayi masa zancan nanba saidai in
ummarsu tafada mawa ita kuma tafada masa.
Inko hakane fati batayi mata adalci ba, ai hira ce
irinta aminta tsakaninsu, gashi ta bata kunya har
tasa ya Abba naganin tazaku.
Tokuwa tasha
alwashin nuna mishi bahaka take nufi ba, afili
tace Allah yabamu rai da lpy.
Sai kuma tasoma
kuka.
Bishira tafadi kan dadi ashe gara data fada
masa zancen dataji suna yida fati, gashi yanzun
yayi mata rana.
Lallai labe yayi mata amfani sai
kawai tasabi 'yarta tazari mayafi tafice makota,
yau kan tana da labari mai dadi sai yawon raba
shi take bata manta ko kalma daya.
Sannan
darana tazo tahau kici-kicin dora girki, lokacin
ummi tafito don yin alwala, ita ko karyawa batayi
ba don tawuni da takaici ya Abba.
Tana kallon
yanda bishira tazubu kayan miya tana jajjagawa
batare data wanke ba hancin kawai ta cire.
Ummi
tayi alwala tashige daki, ranar har dare ummi
bataci komai ba, duk da tanajin yunwa.
Zantukan
abba kawai kemata yawo a kwanya.
Tayi kuka
harta gaji fuska ta kumbura.
Tun uku yadawo
baiga ummi ba, bishira tagabatar masa da abinci
dakyar yayi cokali uku.
Dama yazo dafura, yasha
sannan yanufi shago, yini yayi yana tunanin
kamar bai kyauta ma ummi ba, amma yana
mamakin yanda ummi ta iya cewa bai hau
gadonta ba.
Kenan inyahau din dakuma abinda
yabiyo bayan hawa gadon duk zata ringa fesarwa
ne?
Alhaji babba yace, ai kuma darajar mahaifinta za aduba, da mutuncinsa, Abba yace ai dama alhaji ni banda mahaifinta da tuni nayar da kwallon mangwaro na huta da kuda.
Umman tace je ka gida Allah ya kyauta.
Nan dai ya musu sallama yanufi gida.
Ummi da gske tsoro ne da ita, da rana in ba kowa bta damuwa, amma da dare tfi son tdinga jiyo motsin bishira koda habaicin dta sabayi mata.
Soro taje ta tsaya tana yi tana leka waje, can ta hango bishira, don haka takoma daki ta kullo kofa aranta ta ce kada tazo tayi min duka.
Ummi tna jiyota lokacin data shigo tana cewa wllh kan yarinya zan rama marina, wannan dole ne koba dade saina ramashi.
Abba kan bai nufo gida ba, shagonsa ya wuce lokacin goma ta gota, yaran sunyi shirin tafiya, don haka ya amshi makullin ya shiga shagon saman teburin da suke yin yanka da guga ya hau ya zauna.
Tagumi ya zuba hummu biyu tare da sauke wata ajiyar zuciya mai karfi, me yasa ummi ta furta kalmar data tuna mishi cewa bata sonshi?
Sakankancewa dayanda ummin kenuna mishi yasa shi jin kamar sonsa take ashe dai shi yake shermenshi.
Ya tuno wani labari yaya tabaji na wani mutum da aka ara masa mata wadda bata sonsa, tazo tazauna dashi tsawon shekaru kuma tayi masa biyayya matuka.
Ga 'ya'ya sun haifa yaran sun yi girma sosai, suma sun zama magidanta, sai wata rana mutumin nan suna hira da matar, yace oh, wance dafa ba kya sona, yanzun gashi harmun tsufa kin manta dawata kiyayyah.
Tadubeshi, inji wa yace maka na manta?
Biyayya kurum nake maka amma har gobe bana sonka.
Abba yajinjina kai, lallai dole ne ya nutso, yadaina tunanin ummi tana sonshi kokuma zata soshi, shidai da kaddarar sonta tafada mishi sai yayi ta addu'a Allah ya bashi hakurin jure zama da ita ahaka.
Bai san adadin lokacin daya dauka awaje ba kuma baisan adadin tunanin dayayi ba.
Daga karshe yarufe shagon yanufi gida.
Ganin yanda garin yayi tsit shine yasa shi kallon agogon hannunshi, daya da minti shabakwai, lallai lokaci yatafi.
ZURFIN CIKI book 4 part 10
ZURFIN CIKI book 4 part 10
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:55
Yanufi dakin bishira aranshi yce da wanda yake
kinka gara mai sonka ko mahaukaci ne.
Gdon
yahau tagefe ya kwanta suka saka muhibba
atsakiya, ummi kuwa duk tsawon lokacin nan
tkasa bacci domin bata ga shigowarshi ba.
Idonta
biyu har sai daya shigo ta leka ta windo tana
kalloshi har yashiga dakin bishira ya rufo kofa,
sannan ta kwanta tare dayin ajiyar zuciya.
A fili
tace ina ga fa har dani alaifin nan, amma bari
gari yawaye inba shi hakuri durkusa ma wada ai
ba gajiyawa bane.
Bishira tafarka cikin dare taga
Abba kwance hannunsa na dama dore kan jikin
'yarsu, ta tsura mishi idanu tana son mijinta
sosai.
Ban dahaka data kaishi koto ya bata
takardarta koda mahaifinta xaimata baki
sanadiyar haka, amma shi yanzun yadaina sonta.
Takai hannu tadora a kumatunshi, ahankali
yabude idanu, suka kura majuna ido yace bishira
me yasa kike yin abinda zai samu mu samu
sabani bayan kinsan sone ya hadamu?
Idanuwanta suka kawo ruwa, Abba dane ka soni
kaji dani har alokacin ina ganin ba Wata mace
data kai ni dacen gwanin iya soyayya.
Amma
yanzun duk ka zuba ni a kwandon shara har kana
marina saboda ummi.
Ya ce, a'a ba sbd ummi na
mare kiba, saboda kin dukeni ne amma kiyi
hakuri.
Banason kina zubar da kanki a gurinta,
yawan fadanku zai sa raini ya shiga tsakaninku,
ni kuma ba zan so ta rainaki ba.
Kuma da kin
kwantar da hankalin ki ummi fa ba wai tana sona
bane, ita fa an matsa ma tane, kuma su umma da
kike zagi na rantse miki masoyan kine.
Ta ce
tokai kana son ummi ne ?
Ya dan yi jim, sannan
ya ce ai dai kin san yanda auran namu da ita
yakasance bagatatan bai dace ace kinma tsay
yin wannan tambayar ma.
Tadan yi shiru, zancen
nan ya shige ta bakamar yanda ta zata da farko
ba, ko dadin baki zaimata?
Sannan ta tuno da
ranar da fati tazo.
Ta labe taji koza suyi
zancenta sai taji suna ta hirarsu, acikin harar fati
ke cewa wai kuwa ya kuka kaya ne ummi?
Nasan
yanzun ai kin warke, kema kin goge.
Ta ce
damefa?
Fati tace, a'a ki gane mana, batun
kwanciya.
Ummi tace, kin san cewa yaya Abba ko
gadona bai taba kwana ba?
Fati tace kai haba?
Ummi tadinga yimata rantsuwa, tuno da wannan
sai bishira ta yarda mijinta ma baya son ummi,
don haka sai ta saki murmushi.
Yace, tunanin me
ki ke yi?
Tace da ina ga kamar dadin baki kake
min, amma dana tuno naji ummi tana fadama fati
wai baka taba ko kwanciya a gadonta ba, bare ka
hada jiki da ita sai na yarda.
Abba ya zaro ido, a
ina kika ji suna zancan?
Ta ce, a'a tazo mata
rakiyane naji suna maganar a soro.
Abba ya
girgiza kai.
Bishira tace, kuma da gske hakane,
yakai hannu yakama nata tafin hannun, wannan
wani sirri ne tsakanina da ummin.
Ynda ba zan
fada mata komai tsakanina dake ba, haka itama
zan sakaya nata sirrin, tadai fahimci hakane, don
haka sai ranta yayi mata dadi har ma ta baiwa
Abban kanta a daran.
Ynda taga yna rawar jiki ya
tabbatar ma ta ba wani angwanci da yayi, don
haka zuciyarta fes ta wayi gari.
Duk da cewa
abba ya tashe ta cewa taje tayi wanka harda
Allah yahadata amma tayi niyar baza tayi hakan
ba sai gari yayi haske.
Ummi ta fito don tanuna
mata cewa Abba ya kwana da ita.
Bishira an dafa
ruwan tea an kai falo sai wannan rawan kai ake
yi.
Sai data lura ummi ta dauko tsintsiya tasoma
sharar gidan kamar yanda tasaba, sannan tafito
da buta aka nufi bandaki, kai ko dankwali babu
aka yiwanka aka fito.
Gashi yna ta digar ruwa,
ummi ta fahimta kuma tagane cewa tayi hakan
don ta nuna mata ne.
Kuma taji zafi aranta
kamar ynda bishiran taso, ta amma azuciyar ta
sai tace na banza jiya nan yakora miki mari.
Lokacin da abba ya shigo gidan tagama shara
tana kwashewa, bai ko dubeta baya shige falon
bishira, kan ummi yasake daurewa, me yake
faruwane haka da zafi?
Ta tambayi kanta.
Data
koma daki tagumi ta zabga tana tunani ita da
suka yi kaca-kaca ma sun shirya bare ni?
Kamar
tabi shi har falon bishiran ta gaida shi, amma sai
tafasa.
Tazuba ido taga zai bar gidanne ba tare
daya leko dakinta ba?
Sun gama karin
kumallonsu tsaf yayo wanka don tafiya gurin aiki,
sai dai kayan dazai saka suna dakin ummi.
Ya
fito yanufi dakin.
Ciki- ciki yayi sallama ita kam
tsoro ne ya tsirga mata, tasake tambayar kanta
mekuma yafaru?
Ta amsa tare da gaida shi.
Nan
ma a ciki ya amsa, yadauki kayan sai dazai fita
sannan yace ba kya bukatar komai ko?
Tayi
karfin halin cewa sugata ceta kare.
Ya dube ta
furka tsuke me yasa baki fada minba?
Ta ce, na
manta ne, yace to sai kije gurin bishira da dibar
miki inzan dawo na siyo.
Ba kya neman komai da
rana ko?
Tace a'a sai nama kawai ya daga
murya, kullum ne ya zama dole a saka nama a
abinci?
Jikinta har bari yake don tsoro, ta ce a'a
yaja tsaki ya fita.
Ummi tasaka kanta cikin cinya
tana furta 'inna lillahi wa inna ilaihir raji'un.'
hawaye suka soma yi mata sintiri.KI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 11
ZURFIN CIKI book 4 part 11
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:57
Dadi tamkar yakashe bishira don tna labe tana
jinsu afalon ya saka kya yashirya tsaf, sannan ya
nufo dakinta don dauka jakar laptop dinshi.
Jin
sallamarshi tayi mza tashare hawaye sannan ta
amsa, yshigo ya dauko dari biyu ya aje mata
akan gdo, ga kudin maman nan kura, kada fati
tzo kifada mata baki kudin nama kullum tunda
har kin iya shaida mta cewa ban tba kwana
agadonkiba.
Kin kosa inkwanta dakene?
Yadauki
jakar yarataya sannan yayi mata wani kallo sama
dakasa, to banga gurin kwana agadon naki ba.
Hakanan banga abin kwanciya ajikinki ba, yafice
yabar ummi tsaye tazaro idanunta cikin matukar
al'ajabi da kunya.
Ina ya Abba yaji zancen nan?
Kodai fati ceta fada masa?
Wata zuciyar tace fati
baza ta iyayi masa zancan nanba saidai in
ummarsu tafada mawa ita kuma tafada masa.
Inko hakane fati batayi mata adalci ba, ai hira ce
irinta aminta tsakaninsu, gashi ta bata kunya har
tasa ya Abba naganin tazaku.
Tokuwa tasha
alwashin nuna mishi bahaka take nufi ba, afili
tace Allah yabamu rai da lpy.
Sai kuma tasoma
kuka.
Bishira tafadi kan dadi ashe gara data fada
masa zancen dataji suna yida fati, gashi yanzun
yayi mata rana.
Lallai labe yayi mata amfani sai
kawai tasabi 'yarta tazari mayafi tafice makota,
yau kan tana da labari mai dadi sai yawon raba
shi take bata manta ko kalma daya.
Sannan
darana tazo tahau kici-kicin dora girki, lokacin
ummi tafito don yin alwala, ita ko karyawa batayi
ba don tawuni da takaici ya Abba.
Tana kallon
yanda bishira tazubu kayan miya tana jajjagawa
batare data wanke ba hancin kawai ta cire.
Ummi
tayi alwala tashige daki, ranar har dare ummi
bataci komai ba, duk da tanajin yunwa.
Zantukan
abba kawai kemata yawo a kwanya.
Tayi kuka
harta gaji fuska ta kumbura.
Tun uku yadawo
baiga ummi ba, bishira tagabatar masa da abinci
dakyar yayi cokali uku.
Dama yazo dafura, yasha
sannan yanufi shago, yini yayi yana tunanin
kamar bai kyauta ma ummi ba, amma yana
mamakin yanda ummi ta iya cewa bai hau
gadonta ba.
Kenan inyahau din dakuma abinda
yabiyo bayan hawa gadon duk zata ringa fesarwa
ne?