Sashe 56
Zurfin Ciki Part 1 - 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bishira tana dakin umma tana sallah yabi umma
kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya
Abba?
Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,
yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?
Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?
Tace, kyale ta muje dakin babanku.
Abba ya fada
ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar
bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.
Banda shashancin ta da ita kadai take son
azauna?
Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane
kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in
yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.
Shine ita zata qirqiro fitina?
Yace, umma ai ba da
bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane
kurenta da dare kuzo kai da ita.
Umma ce ta kira
ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu
don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar
isha'i taje gidan.
Can tasamu abba, nan ko umma
ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo
umma tafada mata komai sai ta shiga fada.
Wai
ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko
ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya.
Abba
yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun
in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma
ni abin ya qare akaina?
Nan fa umma tayi mata
tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka
kira shi awaya ya fita.
Umma ta samu dama
taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki
yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice
kinyi fushi da ita kin barwa kishiya?
To kada in
sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke
ganinki da ita.
Ta jima tana bata shawara kafin
Abba yadawo suka nufi gida.
Ya shiga gurin
Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai
kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,
tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa
s / ZURFIN CIKI book 4 part 21
ZURFIN CIKI book 4 part 21
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:19
Kwanci tashi asarar mai rai, shekara ta zagayo
lokacin bishira da tsohon ciki, Abba nason yara
don muhibba taqi dawowa tafi son umma dole
suka haqura suka bar mata.
Ta haifi 'yarta
budurwa tubarkalla ranar suna ta ci sunan sahura
inda suka sa mata walida.
Ummi nason yara, don
haka in tana gida to tana manne da walida, Abba
yana damuwa da rashin samun cikin ummi,
wanda ita ummin ta barma Allah komai.
Shekaru
uku sun sake biyo baya, lokacin Bishira ta sake
haihuwar habiba takwara Abba yayi wa ummi.
Tsohuwa an qara tsufa, 'yan rigingimu sun qaru
tace ita Abba yama takwara amma bata son ya
duke ta irin yanda yayi wa ummi.
Abba kullum
qara son ummi yake, umma ta matsa masa sai
da yayi qoqari ya sai fili rabin filoti tace kuma a
rage ciye ciyen dadin nan agina sh
.
Haka kuwa
ya gina flat mai daki hudu, daya ummi daya
bishira, sai nashi sannan na yara.
Yayi qoqari
gurin gyaran falon ita kuma ummi ya canza mata
kayan daki don bishira an canza mata daza su
tashi agidan su.
Yace tabishi bashi in ya samu
zai bata kudi amadadin kayan daya saima ummi,
tace ta yafe.
Ummi dake karantar (BUSSINESS)
har ta hada (H.N.D) dinta kuma tayi bautar qasa.
Abba dai yace baza'ayi aiki ba amma ya yarda
tayi kasuwanci, Alhaji babba ne ya bata jari inda
take saro kaya zannuwa, lesuna, takalma zuwa
jakunkuna.
Abin ya amsheta don har kayan aure
tana hadawa, tana yin saqo irin su kwatano da
chaina, india, pakistan ko dubai, ta hanyar wani
wan kawarta.
Haka kawai ummi ta samu kanta
da zaban abinci, yawan bacci kasala da dai
sauransu, sam bata san takamaiman lokacin
al'adarta ba.
Don bata wani lissafi in yazo shi
kenan in bai zo ba bata damu ba tama cire ranta
daga batun ciki.
Abba ya kalli nonuwanta, baby
kwanan nan kirjinki ya cika sosai, gashi kinyi
haske ko kin canza mai ne?
Tace yaya yaushe
kazama likita?
Yace, ummi kin fa canza shirya
muje asibiti, ta ce ya Abba don Allah ka bar ni
nagaji dazuwa asibiti.
Yace, to ni zan je inya
tambaya game da yanda ki ka canza.
Cikin jin
haushi tace sai ka dawo.
Ga yara atsakar gida
sun ishe mu, yace ni naki nake qawar in gani
nasan addu'ar da nike yi bazata fadi kara banza
ba, sannan ga qoqarin danake yi, shiru ta masa.
Dagaske yake yi yaje yayi wa likita bayani, yace
yadai kawo fitsarinta.
Sai da suka yi tsiya da qyar
bishira ta lallasheta ta yarda ta bada fitsarinURFIN CIKI book 4 part 23
ZURFIN CIKI book 4 part 23
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:22
Sam bishira bata damu da barin mijinta da zatayi
gurin ummi ba, tunda ta jima da sanin cewa
ummi bata da wani ammafni.
Wannan ne ma
yasa tasha alwashin in taje zatayi addu'a Allah
yakara toshe ummin kada ta warke sam, tunda
umma Bashir ta fada mata duk addu'ar da tayo
kafin ta dawo an karba mata.
Ta kuma kara bata
shawara ta roko musu rigima suyi tayi har su
rabu, Bishira tace duk zata roko.
Ko ranar da
zasu tafi sai da ta yi wa ummi habaici, kawyenta
sun shigo wato makotansu a tsakar gida take
fada musu cewa mijinta kurum take tunani.
Wai
zai sha wahala kafin ta dawo.
Wata cikin su tace,
wahalar me ga shi da amarya?
Ta ce amaryar da
ta ke a toshe, ai bata da ammfani.
Ummi duk
tana ji, takaicin duniya ya isheta sai dai ita zata
so ace bishiran take ta roko ma kanta shiriya ko
Allah zai sa ta dawo ta kama sallah.
Dayar tace,
to Bishira ki roko mata sauki mana, cikin zolaya
tayi zancen, Bishira tace ba abinda zai kaini
makka in roko ma kishiya abin arziki.
Ummi ta
fito ta ce Anty Bishira zai fi kyau ki roko ma
kanki shirya ko in kin dawo kya fara sallah da
tsafta.
To ban san ma yanda zaki kwashe da
ibadar ba ko za a karba tunda ba yin sallah ki ke
ba.
Ta taso fuuu, kawayen suka reketa suka ce
kyaleta bakin ciki ne.
Abba ya fito wanka yana
cewa, Ok, za kuyi na bankwana ko?
Yana da kyau
hakan.
Ummi ta koma dakinta.
Tun bayan tafiyar
Bishira Abba ya shiga takura musamman irin
wannan lkc na sanyi.
Ya dawo da yiwa ummi 'yan
wasanni da ya daina, sai hakan yakara sa shi
damuwa don haka ya shiga lallashin ummi ta
fadawa umma.......
Kuyi hkr da typing din banda
lafia sstr dita nake sawa tana maku.els / ZURFIN CIKI book 4 part 24
ZURFIN CIKI book 4 part 24
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:24
Tace ita kam ba zata iya ba ranar wata juma'a
suka tafi da nufun su fadama umma matsalarsu,
sai dai har zuwa bayan isha'i da abban yazo don
su tafi sun kssa sanar da umman komai, har
sunyi sallama abba yayi kunar bakin wake yace
umma ta fada maki matsalarta?
Umma tace wa?
Yace ummi tace a'a suka koma suka zauna.
Abba
kanshi na kasa Yace umma dama bata da lafiya
ne?
Umma tace mike damunta kuma?
Yace ummi
fada mata.
Ummi ta sunne kai cikin cinya tare da
cewa shiya fada.
Cikin sa'a aka kira wayarshi,
nan yayi waje ya barsu, umma tasa ummi saita
fada.
Ummi ta rasa ta inda zata dauki zancen,
umma ta soma yi mata fada har tsohuwa ta leko
tambaya take lafiya ba sunyi sallama dama basu
tafi bane?
Umma tace wai bata da lafiya ne,
kuma ita da abban sun kasa fadaman shi yayi
waje, ita kuma ta kunshe kai cikin cinya wai injira
ya dawo ya fadaman.
Tsohuwa taja hannun
ummi zuwa dakinta, suka zauna bakin gado ta
riko hannunta.
Takwara fadaman abunda ke
damunki.
Ummi ta sunkuyar da kai ta kasa
magana.
Tsohuwa tace inda baki fadaman ba
akwai wanda zai taimaka maki ne?
Tunda naga
duk yarda mijinki yake da umman ku ya kasa
fadamata to abun mai girma ne.
Ummi ta daure
tace "Gabana ne fa a toshe....." tsohuwa ta rafka
salati, sannan tace yannan badai angurya ba?
Cikin tsoro ummi Tace, ni ma ban sani ba ko
shine.
Salati tsohuwa ne ta jawo hankalin umma
tazo dakin da sauri.
Tsohuwa Tace ina ga
yarinyar nan angurya ne a gabanta.
Umma Tace
shine don wauta daga ke har abban kukayi shiru,
dubi tsawon watanin da kuka dauka, tsohuwa
Tace yanzun yaya za'ayi umma tace ni ina nasan
yanda za'ayi, ai ni na zata yanzun babu masu irin
wannan ciwon.
Rabon da inji labarinshi tun muna
yan mata.
Tsohuwa Tace kai nima na jima banji
ba, amman kinsan dama wanzamai ke aikin.
Alhaji ya dawo daga sallar isha'i yaga abba tsaye
a waje, Yace a'a babana dama baku tafi ba, Abba
yace eh yanzun zamu wuce, ya biyo bayan Alhaji
suka shigo suka riski zancen dasu dasu umma
keyi.
Alhaji Yace lafiya?
Umma Tace yaran nan
ashe zaune suka da lalura, tame inji Alhaji, umma
Tace angurya ce ashe ta fito ma Ummi wai suka
zaune.
Alhaji yace meye kuma angurya Tace wani
abu ne dake toshe mace.
Nan fa suka shiga
tattauna yanda za'a shawo kan abin, tsohuwa
Tace wanzami za a kira ya yanka mata.
Alhaji
yace to gobe zai kira wanzami.
ZURFIN CIKI book 4 part 25
ZURFIN CIKI book 4 part 25
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:26
Abba da jin haka sai ya fito, kishi fal da
zuciyarshi, ya ce umma wanzami kuma?
Ta ce
eh, aikin sune.
Yace gsky umma ba za a kai ta
gurin wani wanzami ba , bagara muje asibiti ba.
Tsohuwa ta ce, kaci gdanku da asibiti komai ku
ce asibiti to wannan ba aikinsu ba ne.
Abba ya
ce, Nifa gsky ba xa a kai min mata gurin wani
wanzami ba, umma asibiti zamu.
kicin, umma gurinki nazo, ta dube shi lafiya
Abba?
Ya turo baki, alamun ranshi bace baki,
yace umma ki sallami bishira, tace kamar yaya?
Yace taje can gidan ko muyi maganar agabanta?
Tace, kyale ta muje dakin babanku.
Abba ya fada
ma umma komai da ummi ke masa, tun dawowar
bishira ran umma ya baci tace ka barni da ita.
Banda shashancin ta da ita kadai take son
azauna?
Baga bishirar nan ba gidan nan ta gane
kuskurenta ko yau yarinyar nan sai da tace in
yafe ta nace ni dama ban riqe ta da wani abu ba.
Shine ita zata qirqiro fitina?
Yace, umma ai ba da
bishira take yi ba dani take yi, tace to zata gane
kurenta da dare kuzo kai da ita.
Umma ce ta kira
ta awaya tace tazo ita da abba, jikinta ya mutu
don tasan qararta aka kai, tana idar da sallar
isha'i taje gidan.
Can tasamu abba, nan ko umma
ta rufe tada fada, koda tsohuwa ta jiyo tazo
umma tafada mata komai sai ta shiga fada.
Wai
ai kishi halas ne, ke suwaiba tsakani ga Allah ko
ke bazaki so kishiya ba, bare ita yarinya.
Abba
yace to gata nan ita ce fata dame ne nida batun
in dawo da bishirar, yanzun na dawo da ita kuma
ni abin ya qare akaina?
Nan fa umma tayi mata
tatas, ta kuma sata anan ta ba Abba Haquri, aka
kira shi awaya ya fita.
Umma ta samu dama
taqara yi mata nasiha da cewa, in bnda shirmenki
yaushe zaki bar ladanki, hanyar aljannarki kice
kinyi fushi da ita kin barwa kishiya?
To kada in
sake jin haka, ki riqe darajarki da mijinki, ke
ganinki da ita.
Ta jima tana bata shawara kafin
Abba yadawo suka nufi gida.
Ya shiga gurin
Bishira ya fada mata cewa yau gurin ummi zai
kwana, nan ya bar ta da kewa yanufi gurin ummi,
tamkar yaune daren farkonsu hara sukai rayuwa
s / ZURFIN CIKI book 4 part 21
ZURFIN CIKI book 4 part 21
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:19
Kwanci tashi asarar mai rai, shekara ta zagayo
lokacin bishira da tsohon ciki, Abba nason yara
don muhibba taqi dawowa tafi son umma dole
suka haqura suka bar mata.
Ta haifi 'yarta
budurwa tubarkalla ranar suna ta ci sunan sahura
inda suka sa mata walida.
Ummi nason yara, don
haka in tana gida to tana manne da walida, Abba
yana damuwa da rashin samun cikin ummi,
wanda ita ummin ta barma Allah komai.
Shekaru
uku sun sake biyo baya, lokacin Bishira ta sake
haihuwar habiba takwara Abba yayi wa ummi.
Tsohuwa an qara tsufa, 'yan rigingimu sun qaru
tace ita Abba yama takwara amma bata son ya
duke ta irin yanda yayi wa ummi.
Abba kullum
qara son ummi yake, umma ta matsa masa sai
da yayi qoqari ya sai fili rabin filoti tace kuma a
rage ciye ciyen dadin nan agina sh
.
Haka kuwa
ya gina flat mai daki hudu, daya ummi daya
bishira, sai nashi sannan na yara.
Yayi qoqari
gurin gyaran falon ita kuma ummi ya canza mata
kayan daki don bishira an canza mata daza su
tashi agidan su.
Yace tabishi bashi in ya samu
zai bata kudi amadadin kayan daya saima ummi,
tace ta yafe.
Ummi dake karantar (BUSSINESS)
har ta hada (H.N.D) dinta kuma tayi bautar qasa.
Abba dai yace baza'ayi aiki ba amma ya yarda
tayi kasuwanci, Alhaji babba ne ya bata jari inda
take saro kaya zannuwa, lesuna, takalma zuwa
jakunkuna.
Abin ya amsheta don har kayan aure
tana hadawa, tana yin saqo irin su kwatano da
chaina, india, pakistan ko dubai, ta hanyar wani
wan kawarta.
Haka kawai ummi ta samu kanta
da zaban abinci, yawan bacci kasala da dai
sauransu, sam bata san takamaiman lokacin
al'adarta ba.
Don bata wani lissafi in yazo shi
kenan in bai zo ba bata damu ba tama cire ranta
daga batun ciki.
Abba ya kalli nonuwanta, baby
kwanan nan kirjinki ya cika sosai, gashi kinyi
haske ko kin canza mai ne?
Tace yaya yaushe
kazama likita?
Yace, ummi kin fa canza shirya
muje asibiti, ta ce ya Abba don Allah ka bar ni
nagaji dazuwa asibiti.
Yace, to ni zan je inya
tambaya game da yanda ki ka canza.
Cikin jin
haushi tace sai ka dawo.
Ga yara atsakar gida
sun ishe mu, yace ni naki nake qawar in gani
nasan addu'ar da nike yi bazata fadi kara banza
ba, sannan ga qoqarin danake yi, shiru ta masa.
Dagaske yake yi yaje yayi wa likita bayani, yace
yadai kawo fitsarinta.
Sai da suka yi tsiya da qyar
bishira ta lallasheta ta yarda ta bada fitsarinURFIN CIKI book 4 part 23
ZURFIN CIKI book 4 part 23
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:22
Sam bishira bata damu da barin mijinta da zatayi
gurin ummi ba, tunda ta jima da sanin cewa
ummi bata da wani ammafni.
Wannan ne ma
yasa tasha alwashin in taje zatayi addu'a Allah
yakara toshe ummin kada ta warke sam, tunda
umma Bashir ta fada mata duk addu'ar da tayo
kafin ta dawo an karba mata.
Ta kuma kara bata
shawara ta roko musu rigima suyi tayi har su
rabu, Bishira tace duk zata roko.
Ko ranar da
zasu tafi sai da ta yi wa ummi habaici, kawyenta
sun shigo wato makotansu a tsakar gida take
fada musu cewa mijinta kurum take tunani.
Wai
zai sha wahala kafin ta dawo.
Wata cikin su tace,
wahalar me ga shi da amarya?
Ta ce amaryar da
ta ke a toshe, ai bata da ammfani.
Ummi duk
tana ji, takaicin duniya ya isheta sai dai ita zata
so ace bishiran take ta roko ma kanta shiriya ko
Allah zai sa ta dawo ta kama sallah.
Dayar tace,
to Bishira ki roko mata sauki mana, cikin zolaya
tayi zancen, Bishira tace ba abinda zai kaini
makka in roko ma kishiya abin arziki.
Ummi ta
fito ta ce Anty Bishira zai fi kyau ki roko ma
kanki shirya ko in kin dawo kya fara sallah da
tsafta.
To ban san ma yanda zaki kwashe da
ibadar ba ko za a karba tunda ba yin sallah ki ke
ba.
Ta taso fuuu, kawayen suka reketa suka ce
kyaleta bakin ciki ne.
Abba ya fito wanka yana
cewa, Ok, za kuyi na bankwana ko?
Yana da kyau
hakan.
Ummi ta koma dakinta.
Tun bayan tafiyar
Bishira Abba ya shiga takura musamman irin
wannan lkc na sanyi.
Ya dawo da yiwa ummi 'yan
wasanni da ya daina, sai hakan yakara sa shi
damuwa don haka ya shiga lallashin ummi ta
fadawa umma.......
Kuyi hkr da typing din banda
lafia sstr dita nake sawa tana maku.els / ZURFIN CIKI book 4 part 24
ZURFIN CIKI book 4 part 24
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:24
Tace ita kam ba zata iya ba ranar wata juma'a
suka tafi da nufun su fadama umma matsalarsu,
sai dai har zuwa bayan isha'i da abban yazo don
su tafi sun kssa sanar da umman komai, har
sunyi sallama abba yayi kunar bakin wake yace
umma ta fada maki matsalarta?
Umma tace wa?
Yace ummi tace a'a suka koma suka zauna.
Abba
kanshi na kasa Yace umma dama bata da lafiya
ne?
Umma tace mike damunta kuma?
Yace ummi
fada mata.
Ummi ta sunne kai cikin cinya tare da
cewa shiya fada.
Cikin sa'a aka kira wayarshi,
nan yayi waje ya barsu, umma tasa ummi saita
fada.
Ummi ta rasa ta inda zata dauki zancen,
umma ta soma yi mata fada har tsohuwa ta leko
tambaya take lafiya ba sunyi sallama dama basu
tafi bane?
Umma tace wai bata da lafiya ne,
kuma ita da abban sun kasa fadaman shi yayi
waje, ita kuma ta kunshe kai cikin cinya wai injira
ya dawo ya fadaman.
Tsohuwa taja hannun
ummi zuwa dakinta, suka zauna bakin gado ta
riko hannunta.
Takwara fadaman abunda ke
damunki.
Ummi ta sunkuyar da kai ta kasa
magana.
Tsohuwa tace inda baki fadaman ba
akwai wanda zai taimaka maki ne?
Tunda naga
duk yarda mijinki yake da umman ku ya kasa
fadamata to abun mai girma ne.
Ummi ta daure
tace "Gabana ne fa a toshe....." tsohuwa ta rafka
salati, sannan tace yannan badai angurya ba?
Cikin tsoro ummi Tace, ni ma ban sani ba ko
shine.
Salati tsohuwa ne ta jawo hankalin umma
tazo dakin da sauri.
Tsohuwa Tace ina ga
yarinyar nan angurya ne a gabanta.
Umma Tace
shine don wauta daga ke har abban kukayi shiru,
dubi tsawon watanin da kuka dauka, tsohuwa
Tace yanzun yaya za'ayi umma tace ni ina nasan
yanda za'ayi, ai ni na zata yanzun babu masu irin
wannan ciwon.
Rabon da inji labarinshi tun muna
yan mata.
Tsohuwa Tace kai nima na jima banji
ba, amman kinsan dama wanzamai ke aikin.
Alhaji ya dawo daga sallar isha'i yaga abba tsaye
a waje, Yace a'a babana dama baku tafi ba, Abba
yace eh yanzun zamu wuce, ya biyo bayan Alhaji
suka shigo suka riski zancen dasu dasu umma
keyi.
Alhaji Yace lafiya?
Umma Tace yaran nan
ashe zaune suka da lalura, tame inji Alhaji, umma
Tace angurya ce ashe ta fito ma Ummi wai suka
zaune.
Alhaji yace meye kuma angurya Tace wani
abu ne dake toshe mace.
Nan fa suka shiga
tattauna yanda za'a shawo kan abin, tsohuwa
Tace wanzami za a kira ya yanka mata.
Alhaji
yace to gobe zai kira wanzami.
ZURFIN CIKI book 4 part 25
ZURFIN CIKI book 4 part 25
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 14:26
Abba da jin haka sai ya fito, kishi fal da
zuciyarshi, ya ce umma wanzami kuma?
Ta ce
eh, aikin sune.
Yace gsky umma ba za a kai ta
gurin wani wanzami ba , bagara muje asibiti ba.
Tsohuwa ta ce, kaci gdanku da asibiti komai ku
ce asibiti to wannan ba aikinsu ba ne.
Abba ya
ce, Nifa gsky ba xa a kai min mata gurin wani
wanzami ba, umma asibiti zamu.