Sashe 59
Zurfin Ciki Part 1 - 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar dakinta Abba yakwana, yanda bata ga
wata rawar jiki daga gare shi ba tayi zargin ummi
tasamu lafiya.
Hakan ya qara dagula mata lissafi,
tayi rabon tsarabarta daga kawayenta sai
maqota, don ko umman bashir daga zam-zam
bata qara mata komai ba.
Dama tana cike da
haushin umman data bari ummi ta daukar mata
'ya gashi nan muhibba ta liqe ma ummi.
Hakan
ya shaqar da umman bashir har tace amaida
mata zam-zam dinta ita bata sha.
Wato don taje
makka shine zato zo ta canza hali?
Ita kuma
bishira ta amsa tare da cewa, ai ba ita ta aike ni
makkan bada har sai tazabi abinda zan bata.
Ummi ko zam zam din ba abata ba, kuma ko
ajikinta.
Abba kam shita kawo masa dogayen
riguna da T-shirt masu kyau, amma su anty ne
suka matsa mata sai ta saya.
Ranar daya dawo
daga dakin bishira ummi tana fashin sallah gashi
yanuna yana dalarura alokacin.
Sai tace ta yafe
masa yau dagobe yaje gurin anty bishira, yace
A'a tace ba haramun bane nina amince, yace
nasani.
Shiba yason sai yatafi tafara damuwa ko
tazo tana jin haushinsa, tace ba komai saida
yatafin kuwa har kuka tayi don kishi.
Amma
tabawa zuciyarta hakuri tasan wata rana wannan
jarumtar datayi zata zame mata alkhairi.
Ita ko
bishira koda yazo mata sam bata damu ta
bincika ba, tunda taga ba girkinta ba, saima ta
hau murna yayo satar kwana ya bata musamman
dataga dayayi wanka yakoma dakin ummi, haka
washegari.
Don haka sai tashiga daga hanci har
da 'yan habaice habaice, kafin tadawo tun da
dama da namiji dan uwansa yake kwana.
Tana
nufin ummi bata ba tayi masa amfanin komai
wannan yasa ummi ta daura aniyar cusa mata
takaici, aranta tace tunda cinikinki labe nikuma
zansa miki hawan jini.
Kamal yazo daukar abincin
da ummi ta saba sawa yau har da kunun gyada
tayi.
Bishira ta kalle shi, wai kai wannan abincin
na waye kullum kake zuwa dauka?
Yace na
ummarmu ne.
Ta taba baki, ummar nan taku
kwadayinta yayi yawa, ko kuwa itama asirin ya
kamata ne?
Kamal kuwa yaje yafada sai ga
umman bashir agidan suna zage zage da bishira,
tana ce ma bishira dadin abin gidan dana nazo
kwadayin ba gidan ubanki ba.
Marowaciyar bnza
ai dama ina da cikinki, lokacin da Abba yasai
maku TV, yace ki bani naki sai ki kace gara kiyar.
Bishira tace, Eh na hana TV aiba wani shegen ya
sai minba, ubana yasai min, kuma nace mai
kwadayin yarinyar daki kace uwarta mai asiri,
menene na amsar abincinta kici banda kwadayi?
Shiyasa kika bata 'yata ashe don asami abinci
ne, umman tasa kuka ni ke ke zagi?
Yau ko abba
zai zo gidan nan zai zaba ko ni ko ke.
Ummi dai
tana daki tana jinsu. (aranta tace dadi na da
gobe saurin zuwa).
Bishira tace dama ya darajaki
ne shine za kice haka, yazo din nace mai kwadayi
harda rainawa na baki zam zam butulu duk
abinda na miki kin manta kece kika aikeni
makkan?
Umman tace, zuwa makkan naki dashi
gara babu, don nasan da kyar ne in za akarbi
wannan aikin nani ke da bakya sallah arniyar
banza qazama.
Ummi harda riqe ciki don dariya,
haka dai suka yi tayi wajuna gori har dai 'yan
kallon da suka taru suka soma bda haquri,
umman bashir tayi gida cikin kuka.
Tagayawa
'ya'yanta komai su bashir dasunce sai sunje sun
zaneta umman bashir din tace barta ku barta
kawai bari abban yadawo.
Da dare ta ritsa shi
agidan yasha mamakin wai yau mahaifiyarshi da
bishira ne suke fada yace hakane dama duk
zamantakewar da ba'a kafata don Allha ba wata
rana sai ta rushe.
Nan yayi tawa bishira fada da
cewa uwarshi sa'arta ce dazata tsaya ta dinga
gaya mata magana?
Nan fa aka sake kacamewa
har abba.
Yakai ga kwasa wa bishira mari,
sakamakon irin rashin kunyar data rike qugu take
tsulawa umman bashir din.
Ummi ganin abin yana
tsawo ta fita taja umman bashir tana bata haquri
ta zaci zata hantare ta amma sai taji tana cewa
ba komai ummi sakayya ce tunda na nuna ina
sonta dole tamin haka.
Abba yace ummi tasa
mayafi taraka umma gida, hakan ya qara qona
ran bishira gashi yanda taga Abba ya bata rai zai
iya yin komai, dole ta koma daki tana cizon yatsa
tare da tunanin mafita.
Ummi kuwa ahanya sai
lallashin umman take tare dayi mata alqawarin
cewa duk abinda take so ta tambayeta zata mata
shi tarakata har gida sannan tadawo.
Sabon kuka
umman bashir tazauna tanayi, takaicinta yanda
bishira ta zage ta taci mata mutunci agaban
ummi, tashare ido tare dayin ajiyar zuciya a fili
tace dani take magana.
Ynzun ummi tasan kishi
fiye da baya, don ta hau turbar ma'aurata kuma
tasan muhimmancin abinda ake yiwa kishi, don
haka zatayi komai na jan hankali don ganin taja
mijinta gareta.
Kuma inta lura cewa bishira ta
maqale mata aqofar daki sai tayi ta jan abba da
wasanni, don ta quntata ma me labe.
Amma
hakan baisa ta daina ba, don haka ta daura
aniyai saita mata abinda zata tona kanta ha abba
yasani.
Duk jumma'a abba yana dawowa gida
musamman in ranar girkin ummi ne don cin
abinci na musamman.
Jumma'a biyu kenan bata
fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis
taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin
tsohuwa tazo.
Don haka suna gaisawa da umma
tace gurin tsohuwa nazo.
Suka shige daki tace da
tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.
Tsohuwa tace, name ummi?
Ta ce na gyaran jiki
mana.
Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu
abubuwa.
Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?
Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,
bada ina fada miki kina sharewa ba?
Ummi tace
haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani
shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja
hankalin mijina.
Ta ce, toda farko ki dinga kula da
jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar
iska.
Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga
tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba
dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da
ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi.
Sannan ki
amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga
inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan
inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga
matsa farin miski a ehem dinki.
Sannan ki samu
saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,
mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari
dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi
biyu safe da yamma.
Sannan ki aya garinta,
kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,
sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar
ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai
ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,
citta, lemun tsami, ki markada su kisha.
In anan
maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum
daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta
musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban
da dukkan sauran mata.
Ki hada da biyayya
tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi.
Ummi
tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin
nan?
Tace, bari zanba matar ado dake yawan
zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu.
Amma
su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya
siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin
ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.
Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje
gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi
tasan duk wadannan hadin matan?
Amma data
tuna cewa 'yar katsina ce sai tace ba mamaki.
Tun ranar alhamis din ta soma aiwatar da
darussan da ta debo daga tsohuwa, safiyar
jumma'a ranar zai bar dakin bishira.
Ya fito tana
sharar tsakar gida ta gaidashi, ya amsa da fara'a,
tare dawani kallo mai fassarar in ba keba.
Cikin
muryar data adana don shi kadai tace, ya abba
ina son in je ayi min zanen fulawa.
Yace jiya kin
fita yau kam a'a. amma ki aika akira mai zanen
tazo ta miki.
Ta marairaice, towa zan aika yaya
abba?
Yace aike ni, ina ne gidan?
Tace layin su
umma ne yace to za'azo ai miki.
Bishira tafito
daga daki tazabga ma ummi harara, Tare dacewa
kisisina.
Abba yakalleta, kema sai tayi miki.
Tace
bana bukata, aikin banza, shikam yafice.
Ummi
kuwa tace gaba da aikinta, ita ko sai tasa kujera
tazauna tana sakin zantuka, eh don kwalliyar
tabanzanta tunda ba a iya biyawa miji bukata.
Allah dai yasa ya fada min komai, to ni me zai
dame ni don 'yar aiki kawai na dauki yarinya.
Tashare min gida, tayi wa mijina abinci, daga nan
fa?
Saita saki shewa, ummi ta ce aranta yau zan
bambance miki.
Birabiskon shinkafa tayi da miya,
ta wadata birabiskon da kayan lambu, miyar ta
dauki nama da bushasshen kifi.
Sannan ta hada
musu kunun aya yaji dabino da madara, ta
aikawa ummanta lokacin da kamal yazo daukar
na ummarsu.
Tasheka wanka taci doguwar rigar
shadda koriya mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau
ne daurin aurensu.
Ga fulawar da yaje ya biya
akazo aka zana mata.
Tanajin rigimar muhibba
tafito tazuba mata adan kwano tazaunar da ita
akofar falon mamanta.bishira tafito kicin baki
tasaki tana kallon ummi da tazo wucewa harda
bangazar ummi, nan ko kamshi ya bude ta na
turarukan da ummi ta fesa.
Abba yana yin
sallama ummi tafito da sauri, oyoyo yayana,
bishira tana daga kicin dinta tana kallon su.
Ummi ta rungume shi, sannu dazuwa sahibina.
Ta amshi ledar hannunshi dajakar, yace yauwa
sannu babyna tace inazan kai ledar?
Yace akwai
ta bishira aciki ki ciro.
Ta mika mishi ledar ta
wuce dajakar dakinta.
Ya mika wa bishira lemo
da abarba da yayo musu tsaraba sannan ya wuce
danasu, awulakance ta aje.
Yana shiga ummi
tadan karo kofar yanda bishiran zata iya lekensu
sosai ta gefen kofan.
Ta cire masa hula ta aje
akan madubi sannan ta kunna fanka.
Ta shirya
masa abinci, yauni zan baka har ka qoshi.
Haka
suka yita baiwa juna abaki har suka qoshi.
Yakamo hannunta mai qunshi yana ta sumbata,
wai kamar kada su goge.
wata rawar jiki daga gare shi ba tayi zargin ummi
tasamu lafiya.
Hakan ya qara dagula mata lissafi,
tayi rabon tsarabarta daga kawayenta sai
maqota, don ko umman bashir daga zam-zam
bata qara mata komai ba.
Dama tana cike da
haushin umman data bari ummi ta daukar mata
'ya gashi nan muhibba ta liqe ma ummi.
Hakan
ya shaqar da umman bashir har tace amaida
mata zam-zam dinta ita bata sha.
Wato don taje
makka shine zato zo ta canza hali?
Ita kuma
bishira ta amsa tare da cewa, ai ba ita ta aike ni
makkan bada har sai tazabi abinda zan bata.
Ummi ko zam zam din ba abata ba, kuma ko
ajikinta.
Abba kam shita kawo masa dogayen
riguna da T-shirt masu kyau, amma su anty ne
suka matsa mata sai ta saya.
Ranar daya dawo
daga dakin bishira ummi tana fashin sallah gashi
yanuna yana dalarura alokacin.
Sai tace ta yafe
masa yau dagobe yaje gurin anty bishira, yace
A'a tace ba haramun bane nina amince, yace
nasani.
Shiba yason sai yatafi tafara damuwa ko
tazo tana jin haushinsa, tace ba komai saida
yatafin kuwa har kuka tayi don kishi.
Amma
tabawa zuciyarta hakuri tasan wata rana wannan
jarumtar datayi zata zame mata alkhairi.
Ita ko
bishira koda yazo mata sam bata damu ta
bincika ba, tunda taga ba girkinta ba, saima ta
hau murna yayo satar kwana ya bata musamman
dataga dayayi wanka yakoma dakin ummi, haka
washegari.
Don haka sai tashiga daga hanci har
da 'yan habaice habaice, kafin tadawo tun da
dama da namiji dan uwansa yake kwana.
Tana
nufin ummi bata ba tayi masa amfanin komai
wannan yasa ummi ta daura aniyar cusa mata
takaici, aranta tace tunda cinikinki labe nikuma
zansa miki hawan jini.
Kamal yazo daukar abincin
da ummi ta saba sawa yau har da kunun gyada
tayi.
Bishira ta kalle shi, wai kai wannan abincin
na waye kullum kake zuwa dauka?
Yace na
ummarmu ne.
Ta taba baki, ummar nan taku
kwadayinta yayi yawa, ko kuwa itama asirin ya
kamata ne?
Kamal kuwa yaje yafada sai ga
umman bashir agidan suna zage zage da bishira,
tana ce ma bishira dadin abin gidan dana nazo
kwadayin ba gidan ubanki ba.
Marowaciyar bnza
ai dama ina da cikinki, lokacin da Abba yasai
maku TV, yace ki bani naki sai ki kace gara kiyar.
Bishira tace, Eh na hana TV aiba wani shegen ya
sai minba, ubana yasai min, kuma nace mai
kwadayin yarinyar daki kace uwarta mai asiri,
menene na amsar abincinta kici banda kwadayi?
Shiyasa kika bata 'yata ashe don asami abinci
ne, umman tasa kuka ni ke ke zagi?
Yau ko abba
zai zo gidan nan zai zaba ko ni ko ke.
Ummi dai
tana daki tana jinsu. (aranta tace dadi na da
gobe saurin zuwa).
Bishira tace dama ya darajaki
ne shine za kice haka, yazo din nace mai kwadayi
harda rainawa na baki zam zam butulu duk
abinda na miki kin manta kece kika aikeni
makkan?
Umman tace, zuwa makkan naki dashi
gara babu, don nasan da kyar ne in za akarbi
wannan aikin nani ke da bakya sallah arniyar
banza qazama.
Ummi harda riqe ciki don dariya,
haka dai suka yi tayi wajuna gori har dai 'yan
kallon da suka taru suka soma bda haquri,
umman bashir tayi gida cikin kuka.
Tagayawa
'ya'yanta komai su bashir dasunce sai sunje sun
zaneta umman bashir din tace barta ku barta
kawai bari abban yadawo.
Da dare ta ritsa shi
agidan yasha mamakin wai yau mahaifiyarshi da
bishira ne suke fada yace hakane dama duk
zamantakewar da ba'a kafata don Allha ba wata
rana sai ta rushe.
Nan yayi tawa bishira fada da
cewa uwarshi sa'arta ce dazata tsaya ta dinga
gaya mata magana?
Nan fa aka sake kacamewa
har abba.
Yakai ga kwasa wa bishira mari,
sakamakon irin rashin kunyar data rike qugu take
tsulawa umman bashir din.
Ummi ganin abin yana
tsawo ta fita taja umman bashir tana bata haquri
ta zaci zata hantare ta amma sai taji tana cewa
ba komai ummi sakayya ce tunda na nuna ina
sonta dole tamin haka.
Abba yace ummi tasa
mayafi taraka umma gida, hakan ya qara qona
ran bishira gashi yanda taga Abba ya bata rai zai
iya yin komai, dole ta koma daki tana cizon yatsa
tare da tunanin mafita.
Ummi kuwa ahanya sai
lallashin umman take tare dayi mata alqawarin
cewa duk abinda take so ta tambayeta zata mata
shi tarakata har gida sannan tadawo.
Sabon kuka
umman bashir tazauna tanayi, takaicinta yanda
bishira ta zage ta taci mata mutunci agaban
ummi, tashare ido tare dayin ajiyar zuciya a fili
tace dani take magana.
Ynzun ummi tasan kishi
fiye da baya, don ta hau turbar ma'aurata kuma
tasan muhimmancin abinda ake yiwa kishi, don
haka zatayi komai na jan hankali don ganin taja
mijinta gareta.
Kuma inta lura cewa bishira ta
maqale mata aqofar daki sai tayi ta jan abba da
wasanni, don ta quntata ma me labe.
Amma
hakan baisa ta daina ba, don haka ta daura
aniyai saita mata abinda zata tona kanta ha abba
yasani.
Duk jumma'a abba yana dawowa gida
musamman in ranar girkin ummi ne don cin
abinci na musamman.
Jumma'a biyu kenan bata
fado kanta ba sai wannan, don haka tun alhamis
taje ta yarfo kitsonta, ta biyo ta gidan su gurin
tsohuwa tazo.
Don haka suna gaisawa da umma
tace gurin tsohuwa nazo.
Suka shige daki tace da
tsohuwa nazo ne indan samu dan wani sirrin.
Tsohuwa tace, name ummi?
Ta ce na gyaran jiki
mana.
Fati tace min kwanaki kin fada mata wasu
abubuwa.
Tsohuwa ta ce, ja'ira, kinga uwar bari?
Dama nace zaki same ni ina kyakkyawan zamana,
bada ina fada miki kina sharewa ba?
Ummi tace
haba tsohuwa banaso aji mu yanzun dai ki bani
shawara sannan ki fada min abinda zanyi inja
hankalin mijina.
Ta ce, toda farko ki dinga kula da
jikinki ta hanyar rufe shi ruf, kada kibar kofar
iska.
Banda tafiya ba takalmi, iska tana shiga
tanan kuma mace narage ni'ima banda zama ba
dankwali inso samu ne hatta tsarki ki daina yi da
ruwan sanyi, ki dinga yida ruwan dumi.
Sannan ki
amshi bagaruwa gurin ummarki ki dinga shiga
inkin tafasa da alif dakuma saiwar mata, sannan
inkinyi al'ada kin gama kinyi wanka toki dinga
matsa farin miski a ehem dinki.
Sannan ki samu
saiwar kankana, saiwar zogale, kanunfari,
mazarkwaila dazuma amma kisa kanunfari
dayawa sai ki dafa su su dafu kullum kisha kofi
biyu safe da yamma.
Sannan ki aya garinta,
kwakwa ma kiyi garinta, dabino ma kiyi garinsa,
sai ki dinga diban cokali bibbiyu ki zuba amadarar
ruwa sannan ki zuba zumarki mai kyau kisha, sai
ki samu kuma gwanda, kankana, abarba, zogale,
citta, lemun tsami, ki markada su kisha.
In anan
maki katsaya yarinya zakiji ki kin cika cindum
daruwan ni'ima sai kin samu martaba ta
musamman agurin miji dan zaijiki kin fita daban
da dukkan sauran mata.
Ki hada da biyayya
tsafta da kuma iya tsara girki mai dadi.
Ummi
tace, toni yanzun yaya zanyi nasamu saiwoyin
nan?
Tace, bari zanba matar ado dake yawan
zuwa kasuwar qauye zata zo miki dasu.
Amma
su gwanda gasu nan bakin titi ko shi sai kice ya
siyo miki, zogale kuwa baki rasa shi gurin
ummarki, har da cittar da alif din da bagaruwan.
Ta ce to, ta tafi gurin umma ta amsa har taje
gida bata daina mamakin tsohuwa ba, ya akayi
tasan duk wadannan hadin matan?
Amma data
tuna cewa 'yar katsina ce sai tace ba mamaki.
Tun ranar alhamis din ta soma aiwatar da
darussan da ta debo daga tsohuwa, safiyar
jumma'a ranar zai bar dakin bishira.
Ya fito tana
sharar tsakar gida ta gaidashi, ya amsa da fara'a,
tare dawani kallo mai fassarar in ba keba.
Cikin
muryar data adana don shi kadai tace, ya abba
ina son in je ayi min zanen fulawa.
Yace jiya kin
fita yau kam a'a. amma ki aika akira mai zanen
tazo ta miki.
Ta marairaice, towa zan aika yaya
abba?
Yace aike ni, ina ne gidan?
Tace layin su
umma ne yace to za'azo ai miki.
Bishira tafito
daga daki tazabga ma ummi harara, Tare dacewa
kisisina.
Abba yakalleta, kema sai tayi miki.
Tace
bana bukata, aikin banza, shikam yafice.
Ummi
kuwa tace gaba da aikinta, ita ko sai tasa kujera
tazauna tana sakin zantuka, eh don kwalliyar
tabanzanta tunda ba a iya biyawa miji bukata.
Allah dai yasa ya fada min komai, to ni me zai
dame ni don 'yar aiki kawai na dauki yarinya.
Tashare min gida, tayi wa mijina abinci, daga nan
fa?
Saita saki shewa, ummi ta ce aranta yau zan
bambance miki.
Birabiskon shinkafa tayi da miya,
ta wadata birabiskon da kayan lambu, miyar ta
dauki nama da bushasshen kifi.
Sannan ta hada
musu kunun aya yaji dabino da madara, ta
aikawa ummanta lokacin da kamal yazo daukar
na ummarsu.
Tasheka wanka taci doguwar rigar
shadda koriya mai duhu, ta kafe dauri tamkar yau
ne daurin aurensu.
Ga fulawar da yaje ya biya
akazo aka zana mata.
Tanajin rigimar muhibba
tafito tazuba mata adan kwano tazaunar da ita
akofar falon mamanta.bishira tafito kicin baki
tasaki tana kallon ummi da tazo wucewa harda
bangazar ummi, nan ko kamshi ya bude ta na
turarukan da ummi ta fesa.
Abba yana yin
sallama ummi tafito da sauri, oyoyo yayana,
bishira tana daga kicin dinta tana kallon su.
Ummi ta rungume shi, sannu dazuwa sahibina.
Ta amshi ledar hannunshi dajakar, yace yauwa
sannu babyna tace inazan kai ledar?
Yace akwai
ta bishira aciki ki ciro.
Ta mika mishi ledar ta
wuce dajakar dakinta.
Ya mika wa bishira lemo
da abarba da yayo musu tsaraba sannan ya wuce
danasu, awulakance ta aje.
Yana shiga ummi
tadan karo kofar yanda bishiran zata iya lekensu
sosai ta gefen kofan.
Ta cire masa hula ta aje
akan madubi sannan ta kunna fanka.
Ta shirya
masa abinci, yauni zan baka har ka qoshi.
Haka
suka yita baiwa juna abaki har suka qoshi.
Yakamo hannunta mai qunshi yana ta sumbata,
wai kamar kada su goge.