Sashe 49
Zurfin Ciki Part 1 - 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har ya gyara mata kwanciya itama 'yar ya gyara
ta amma bishira bata farka ba, don haka yakashe
mata wuta yafita.
Yaso kashe injin amma garin
da zafi gashi basu kawo wutar nepa ba, gidan
yarufe yazo ya tura kofar ummi data rufe.
Karar
kofar ne ya farkar da ita amma bata motsa ba,
tun daga kofar yatsaya yana kallonta, can
tsakiyar gadon takwanta bata dora kanta saman
filo ba.
Amma tana manne da filo daya akirjinta
fuskarta yake kallo, a jikinta taji kallonta yakeyi.
Kusan minti 4 sannan ya aje ledar hannunshi.
Shirin bacci yake amma yakasa daina kollonta,
shikanshi yana mamakin wannar jarababben son
dayake ma ummi, duk da dakewar dayake don
kada yabada kanshi amma sai yadinga jin wani
abu yana fisgarshi.
Tamkar yafito mata da zallan
sonshi gareta, tsoronshi inta gano kila tarainashi.
Kadan-kadan takan bude ido ta saci kallonshi, sai
daya gama komai a tunanin ta ya kwanta a
gadon amma sai taga yadauki filo yakwanta a
kan kujera.
Haka suka rayu har tsawon sati daya,
ranar yabar dakin ummi ranar kuma tasoma salla,
ita ko bishira satin nan tayi shine tamkar
mahaukaciya sabon kamu.
Ranar kuma da abba
yadawo dakinta bata runtsa ba shima bata barshi
ya runtsa ba, daga bisani dole yabar dakin
yakoma falonta yakwanta.
Haka gidan yaci gaba
da kasancewa, in Abba yafita ummi bata da
sauran sakewa saboda zagi da habaicin bishira.
Wani sa'in har da kawayenta, ko makota 'yan
jam'iyarta su shigo suyi tayi, ummi bata kula su.qnovels / ZURFIN CIKI book 4 part 8
ZURFIN CIKI book 4 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:50
Duk abinda bishira zatayi kada takulata.
To ita
duk bawannan bne damuwarta ba, damuwarta
ynda Abba sam yaki nuna sha'awarta gare shi,
duk dayasan tana sallah, hka nan duk lokacin
dakwananshi yajuyo kanta sai dai ya jefa filo
akan kujera ya kwanta.
Takasa gane ma'anar
hakan, tun tanajin dadin ynda bai nemeta ba
saboda tsoronsa da take harta dawo tasoma jin
haushi.
Ita ma fa mutum ce cikakka mai lafiya,
sannan tana kwana daki daya da san kacecen
abun sonta ya ya ba zata damu ba?
Sai dai tayi
wa kanta alkawarin a yau in zasu shekara ahaka
ba za ta taba yi masa tallar kanta ba ma'ana
baza takai masa kanta ba.
Sai dai zatayi masa
kyale- kyale taga karshen girman kai, ta kosa su
hadu da fati don ta bata sakon kananan kaya
tasiyo mata don ta bata labarin cewa ta kwashe
su a wambai.
Kwananta goma taso ma girka, duk
tsawon kwanakin nan abincin siyarwa dana
umma suke ci, domin bishira taki dafa abinci.
Ranar da zata fara girki ta haukata gidan da
kamshi, tuwon shinkafa miyar shuwaka, tasan
Abba nason tuwon shinkafa.
Tun kafin ya dawo
yamata waya ta aika shagonshi, 'yan shago sun
ci suna santi, haka nan ya gayyaci abokansa
kofar gida ya shimfida musu tabarma suka ci tare
da lemu, zobo da kunun aya. (reall ehem tazubo
mun nawa na koma 1 site ina kimtsa cikina lolx)
ga nama ya wadata a ciki, abba yaji dadin yanda
abokanshi sukayi ta santi, safiyar ranar kuma
kunun gyada ta musu da kosai.
Duk wannan
abincin da ummi keyi bishira ko a harshenta ta ki
ci, cewa ma tayi ita fa kowa tayi girkinta don
baza ta ci abincin ummi ba.
Kuma ba shegiyar
dazatai wa girki, hakan yayi wa ummi dadi don
nata ganin ta bakin tsohuwa ce, da ta ce ko kwai
bishira tadafa shine dai dai a cikin bawo to baza
ta iya ci ba bare wani abinci.
Sun zauna tsawon
wata daya ahaka ummi bata taba leka ko kofar
gida ba, tana kewar ummanta gara ma tsohuwa
duk ranar juma'a in tadawo masallaci takan biyo
gidan taga takwararta.
Dakinta Abba yake
yagama karyawa ya shirya zai tafi aiki, ummi ta
kalle shi tana son tambayar zuwa gidan umma
tna jin tsoro.
Ya dubeta kamar kina son cewa
wani abu ko?
Ta ce am dama inaso inje gida in
gaida su umma, yajuyo yadubeta suka hada ido.
Gabanta yafadi, ta sunkuyar dakanta, yace a'a
tadaga ido takalle shi, wani kunci taji aranta, ga
matanshi nan yini take garari a layi bata ko
tambaya amma ita ta tambaya shine ma zai
hanata?
Ya dauki jakar shi, ta mike ta rakashi
har tsaka gida tare da yi masa addu'ar Allah
yatsare, yini tayi da takaici dama haka mata suke
ji in an hana su zuwa anguwa?
Daran ranar zai
koma ga bishira don haka bata san dawowarshi,
tana kwance kan doguwar kujera tana karanta
littafin hausa ( naleka muku kozanga sunan
littafin amma bangano mukuba) kamshin turaren
shi ne yasa tasan yashigo, don littafin yadauki
hankalinta.
Ta amsa sallamar daya sake yi tare
da mikewa zaune, yana sanye da kananan kaya
tamkar wani dan saurayi, yayi kyau a idonta
kamar ta rungumeshi.
Tace sannu dazuwa yace
yawwa, dauko mayafinki muje tazura takalma
bayan tagoge sannan ta ciro mayafi, yace a'a
dauko hijabin.
Ta maida ta dauko hijabi tafito
sannan yakulle kofar, saida suka fita waje sannan
yadubeta, hannu rabbana zakije musu?
Tace yaya
Abba toni bani da kudi ai.
Sukabi ta wani super
market suka sai sabulai da turare, akafa suke
takawa sannu ahankali suka jero duk da cewa
bawata hira suke ba, Abba ne yake amsa waya
jifa-jifa na jama'a masu sonshi.
Tun daga nesa
suka hangi mahaifansu suna cin abinci a inda
suka saba.
Alhaji babba dakarami.
Cikin zumudi
ummi ta ce, yauwa gasu alh.
Abba yaje haka
zakije musu da rawar kanki ko?
Cikin shagwaba
tace, wanne rawar kai nayi toni yaya Abba?
Yace,
na gani kinayi kamar zaki kwasa da gudu, kafin
tayi magana sun iso gurin dukkansu suka zube
akan tabarmar daga gefe.
Abba ne yasoma cewa,
sannunku alh.
Alh.
Yace, a'a kune?
Alh karami
yace, uwata harda ke?
Tace, eh ina yininku?
Sukace lpy lau.
Alh.
Karami yace, uwata kunanan
lpy ba wta matsala ko?
Ta ce, ba komai alh..
Yace to Allah yyi maku albarka, ya azurtaku da
'ya'ya ma su albarka wadanda kuma zasu biku.
Abba yace amin suka hada baki da Alhaji babba,
alh babba yaci gaba da cewa, Abba ya hakurin
shirmen ummi kuma?
Ince dai bawata matsala?
Abba yakalleta mun gode Allah alh, amma bwata
matsala, ummi tamike dazumudi bari a karasa.
Tun daga soro take kwala ma umma kira.
Umma
tce, A'a muryar wa nake ji haka?
Ummi tashigo
da gudu ta cakume umma, tsohuwa tafito tana
fadin lale.
Dakin tsohuwa tasoma shiga suka
gaisa sannan tadawo dakin umma, sun gaisa
umma tasake mata nasiha, ummi tace umma ni
matsalata daya matarsa.
Kullum saitayi min
habaici tana zagina wata rana r harda kawayentaRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 9 ZURFIN CIKI book 4 part 9 Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:54 Ita ko bishira gidan su umman bashir ta tafi dakuka wiwi, tace Abba yamata duka takan sun taka hakkinta sun fita ranar girkinta.
Tayi magana ummi ta mata tsaki shi kuma yazo yazo yahauta da duka, umman bashir tace duka!
Duka akan ummi?
Tabdi, tashi muje gurin wadanda suka daure masu gindi.
Umma na kokarin shiga daukin alhaji taji sallamarsu sama-sama, gabanta yafadi ta amsa tare da dawowa baya.
Sahura tace to suwaiba, abinda kuka shiirya yasoma tasiri.
Abba yayi wa bishira shegen duka saboda 'yarku, umma tace haba sahura, yaya ki ke irin wannan maganar?
Mu ne zamu sa Abba ya cutar da iyalinsa?
Sahura kiyi nazari.
Alhaji yafito, me yafaru ne ni kejin hayaniya suwaiba?
Umma tace, oho.
Sahura tace, bishira fada musu.
Nan bishira ta shaida masu yanda ta tsara ma umman bashir, alhaji yadaga waya yakira Abba, Abba yana dagawa alhaji cikin zafi yace Abba maza kazo yanzun duk in da kake.
Abba yace to alhaji, ummi ta mike zan bika tsoro nake ji ni daya, cikin zafin rai yace abin daki ke tsoro ya cinye ki, ya fita fuuu.
Cirko-cirko ya same su a tsakar gida, sai muryar sahura kake ji tana rashin mutunci.
Alhaji karami yadawo gidan shi sai ya jiyo muryar sahura a can gidan, ya nufi gidan don haka kusan tare suka shiga gidan da Abba.
Alhaji cikin bacin rai yafada Abba da fada, abba bai katse shi ba har sai daya kai ga tambayarshi cewa me yasa yayi mata duka?
Yace, banyi mata duka ba alhaji marinta kawai nayi, umma ta ce mari kawai ne Abba?
Alhaji karami yace, to kan wane dalili ma zaka mare ta?
Abba ya koro musu komai, ya kara da cewa, wannan har zata ce an mata tsaki, zata yi duka ni wane irin zagi ne bata min ina hakura darajar iyayenta?
Ya nuna ta, wallahi in kika kai ni bango zaki koma gidanku don bazan iya ba na gaji, nan kuma su alhaji suka shiga bashi hakuri.
Ita kuma suka bata rashin gaskiya, sai dai duk da haka umma tai masa fadan kada ya sake daukan ummi ranar girkin bishira ya fita da ita, yace to.
Umman bashir taja bishira zo muje ai dama nasan baza suga laifin 'yar su ba.
To wllh marin da yamiki ki tabbata bashine.
Ko nan da yaushe ne ki rama shi kan ummin, in ba haka ba duk da banice uwar data haife kiba sai na tsine miki.
Alhaji karami yace, to katuwa mara lissafi, ke dai kinji haushin rayuwarki, to ki sani duk randa ta rama duka akan ummi ni kuma akan ki zan rama wa ummin inga ta tsiya.
Alhaji babba yace, kada kai ma kazama su mana aminu.
Tsohuwa tace, gskiya ne, in har tazama silar dukan ummi itama sai ya mata taji.
Umma tace, a'a duk abin ba zai kai haka ba insha Allahu, kai dai abba kayi ta hakuri sannan kadaina sa hannu kana dukan mace.
Yace, umma dukana fa tayi, sai kace wani soko zan tsaya mce tna dukana, umma tace, to ai tace ummi taje duka, yace ummin 'yarta ce?
ta amma bishira bata farka ba, don haka yakashe
mata wuta yafita.
Yaso kashe injin amma garin
da zafi gashi basu kawo wutar nepa ba, gidan
yarufe yazo ya tura kofar ummi data rufe.
Karar
kofar ne ya farkar da ita amma bata motsa ba,
tun daga kofar yatsaya yana kallonta, can
tsakiyar gadon takwanta bata dora kanta saman
filo ba.
Amma tana manne da filo daya akirjinta
fuskarta yake kallo, a jikinta taji kallonta yakeyi.
Kusan minti 4 sannan ya aje ledar hannunshi.
Shirin bacci yake amma yakasa daina kollonta,
shikanshi yana mamakin wannar jarababben son
dayake ma ummi, duk da dakewar dayake don
kada yabada kanshi amma sai yadinga jin wani
abu yana fisgarshi.
Tamkar yafito mata da zallan
sonshi gareta, tsoronshi inta gano kila tarainashi.
Kadan-kadan takan bude ido ta saci kallonshi, sai
daya gama komai a tunanin ta ya kwanta a
gadon amma sai taga yadauki filo yakwanta a
kan kujera.
Haka suka rayu har tsawon sati daya,
ranar yabar dakin ummi ranar kuma tasoma salla,
ita ko bishira satin nan tayi shine tamkar
mahaukaciya sabon kamu.
Ranar kuma da abba
yadawo dakinta bata runtsa ba shima bata barshi
ya runtsa ba, daga bisani dole yabar dakin
yakoma falonta yakwanta.
Haka gidan yaci gaba
da kasancewa, in Abba yafita ummi bata da
sauran sakewa saboda zagi da habaicin bishira.
Wani sa'in har da kawayenta, ko makota 'yan
jam'iyarta su shigo suyi tayi, ummi bata kula su.qnovels / ZURFIN CIKI book 4 part 8
ZURFIN CIKI book 4 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:50
Duk abinda bishira zatayi kada takulata.
To ita
duk bawannan bne damuwarta ba, damuwarta
ynda Abba sam yaki nuna sha'awarta gare shi,
duk dayasan tana sallah, hka nan duk lokacin
dakwananshi yajuyo kanta sai dai ya jefa filo
akan kujera ya kwanta.
Takasa gane ma'anar
hakan, tun tanajin dadin ynda bai nemeta ba
saboda tsoronsa da take harta dawo tasoma jin
haushi.
Ita ma fa mutum ce cikakka mai lafiya,
sannan tana kwana daki daya da san kacecen
abun sonta ya ya ba zata damu ba?
Sai dai tayi
wa kanta alkawarin a yau in zasu shekara ahaka
ba za ta taba yi masa tallar kanta ba ma'ana
baza takai masa kanta ba.
Sai dai zatayi masa
kyale- kyale taga karshen girman kai, ta kosa su
hadu da fati don ta bata sakon kananan kaya
tasiyo mata don ta bata labarin cewa ta kwashe
su a wambai.
Kwananta goma taso ma girka, duk
tsawon kwanakin nan abincin siyarwa dana
umma suke ci, domin bishira taki dafa abinci.
Ranar da zata fara girki ta haukata gidan da
kamshi, tuwon shinkafa miyar shuwaka, tasan
Abba nason tuwon shinkafa.
Tun kafin ya dawo
yamata waya ta aika shagonshi, 'yan shago sun
ci suna santi, haka nan ya gayyaci abokansa
kofar gida ya shimfida musu tabarma suka ci tare
da lemu, zobo da kunun aya. (reall ehem tazubo
mun nawa na koma 1 site ina kimtsa cikina lolx)
ga nama ya wadata a ciki, abba yaji dadin yanda
abokanshi sukayi ta santi, safiyar ranar kuma
kunun gyada ta musu da kosai.
Duk wannan
abincin da ummi keyi bishira ko a harshenta ta ki
ci, cewa ma tayi ita fa kowa tayi girkinta don
baza ta ci abincin ummi ba.
Kuma ba shegiyar
dazatai wa girki, hakan yayi wa ummi dadi don
nata ganin ta bakin tsohuwa ce, da ta ce ko kwai
bishira tadafa shine dai dai a cikin bawo to baza
ta iya ci ba bare wani abinci.
Sun zauna tsawon
wata daya ahaka ummi bata taba leka ko kofar
gida ba, tana kewar ummanta gara ma tsohuwa
duk ranar juma'a in tadawo masallaci takan biyo
gidan taga takwararta.
Dakinta Abba yake
yagama karyawa ya shirya zai tafi aiki, ummi ta
kalle shi tana son tambayar zuwa gidan umma
tna jin tsoro.
Ya dubeta kamar kina son cewa
wani abu ko?
Ta ce am dama inaso inje gida in
gaida su umma, yajuyo yadubeta suka hada ido.
Gabanta yafadi, ta sunkuyar dakanta, yace a'a
tadaga ido takalle shi, wani kunci taji aranta, ga
matanshi nan yini take garari a layi bata ko
tambaya amma ita ta tambaya shine ma zai
hanata?
Ya dauki jakar shi, ta mike ta rakashi
har tsaka gida tare da yi masa addu'ar Allah
yatsare, yini tayi da takaici dama haka mata suke
ji in an hana su zuwa anguwa?
Daran ranar zai
koma ga bishira don haka bata san dawowarshi,
tana kwance kan doguwar kujera tana karanta
littafin hausa ( naleka muku kozanga sunan
littafin amma bangano mukuba) kamshin turaren
shi ne yasa tasan yashigo, don littafin yadauki
hankalinta.
Ta amsa sallamar daya sake yi tare
da mikewa zaune, yana sanye da kananan kaya
tamkar wani dan saurayi, yayi kyau a idonta
kamar ta rungumeshi.
Tace sannu dazuwa yace
yawwa, dauko mayafinki muje tazura takalma
bayan tagoge sannan ta ciro mayafi, yace a'a
dauko hijabin.
Ta maida ta dauko hijabi tafito
sannan yakulle kofar, saida suka fita waje sannan
yadubeta, hannu rabbana zakije musu?
Tace yaya
Abba toni bani da kudi ai.
Sukabi ta wani super
market suka sai sabulai da turare, akafa suke
takawa sannu ahankali suka jero duk da cewa
bawata hira suke ba, Abba ne yake amsa waya
jifa-jifa na jama'a masu sonshi.
Tun daga nesa
suka hangi mahaifansu suna cin abinci a inda
suka saba.
Alhaji babba dakarami.
Cikin zumudi
ummi ta ce, yauwa gasu alh.
Abba yaje haka
zakije musu da rawar kanki ko?
Cikin shagwaba
tace, wanne rawar kai nayi toni yaya Abba?
Yace,
na gani kinayi kamar zaki kwasa da gudu, kafin
tayi magana sun iso gurin dukkansu suka zube
akan tabarmar daga gefe.
Abba ne yasoma cewa,
sannunku alh.
Alh.
Yace, a'a kune?
Alh karami
yace, uwata harda ke?
Tace, eh ina yininku?
Sukace lpy lau.
Alh.
Karami yace, uwata kunanan
lpy ba wta matsala ko?
Ta ce, ba komai alh..
Yace to Allah yyi maku albarka, ya azurtaku da
'ya'ya ma su albarka wadanda kuma zasu biku.
Abba yace amin suka hada baki da Alhaji babba,
alh babba yaci gaba da cewa, Abba ya hakurin
shirmen ummi kuma?
Ince dai bawata matsala?
Abba yakalleta mun gode Allah alh, amma bwata
matsala, ummi tamike dazumudi bari a karasa.
Tun daga soro take kwala ma umma kira.
Umma
tce, A'a muryar wa nake ji haka?
Ummi tashigo
da gudu ta cakume umma, tsohuwa tafito tana
fadin lale.
Dakin tsohuwa tasoma shiga suka
gaisa sannan tadawo dakin umma, sun gaisa
umma tasake mata nasiha, ummi tace umma ni
matsalata daya matarsa.
Kullum saitayi min
habaici tana zagina wata rana r harda kawayentaRFIN CIKI novels / ZURFIN CIKI book 4 part 9 ZURFIN CIKI book 4 part 9 Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 01:54 Ita ko bishira gidan su umman bashir ta tafi dakuka wiwi, tace Abba yamata duka takan sun taka hakkinta sun fita ranar girkinta.
Tayi magana ummi ta mata tsaki shi kuma yazo yazo yahauta da duka, umman bashir tace duka!
Duka akan ummi?
Tabdi, tashi muje gurin wadanda suka daure masu gindi.
Umma na kokarin shiga daukin alhaji taji sallamarsu sama-sama, gabanta yafadi ta amsa tare da dawowa baya.
Sahura tace to suwaiba, abinda kuka shiirya yasoma tasiri.
Abba yayi wa bishira shegen duka saboda 'yarku, umma tace haba sahura, yaya ki ke irin wannan maganar?
Mu ne zamu sa Abba ya cutar da iyalinsa?
Sahura kiyi nazari.
Alhaji yafito, me yafaru ne ni kejin hayaniya suwaiba?
Umma tace, oho.
Sahura tace, bishira fada musu.
Nan bishira ta shaida masu yanda ta tsara ma umman bashir, alhaji yadaga waya yakira Abba, Abba yana dagawa alhaji cikin zafi yace Abba maza kazo yanzun duk in da kake.
Abba yace to alhaji, ummi ta mike zan bika tsoro nake ji ni daya, cikin zafin rai yace abin daki ke tsoro ya cinye ki, ya fita fuuu.
Cirko-cirko ya same su a tsakar gida, sai muryar sahura kake ji tana rashin mutunci.
Alhaji karami yadawo gidan shi sai ya jiyo muryar sahura a can gidan, ya nufi gidan don haka kusan tare suka shiga gidan da Abba.
Alhaji cikin bacin rai yafada Abba da fada, abba bai katse shi ba har sai daya kai ga tambayarshi cewa me yasa yayi mata duka?
Yace, banyi mata duka ba alhaji marinta kawai nayi, umma ta ce mari kawai ne Abba?
Alhaji karami yace, to kan wane dalili ma zaka mare ta?
Abba ya koro musu komai, ya kara da cewa, wannan har zata ce an mata tsaki, zata yi duka ni wane irin zagi ne bata min ina hakura darajar iyayenta?
Ya nuna ta, wallahi in kika kai ni bango zaki koma gidanku don bazan iya ba na gaji, nan kuma su alhaji suka shiga bashi hakuri.
Ita kuma suka bata rashin gaskiya, sai dai duk da haka umma tai masa fadan kada ya sake daukan ummi ranar girkin bishira ya fita da ita, yace to.
Umman bashir taja bishira zo muje ai dama nasan baza suga laifin 'yar su ba.
To wllh marin da yamiki ki tabbata bashine.
Ko nan da yaushe ne ki rama shi kan ummin, in ba haka ba duk da banice uwar data haife kiba sai na tsine miki.
Alhaji karami yace, to katuwa mara lissafi, ke dai kinji haushin rayuwarki, to ki sani duk randa ta rama duka akan ummi ni kuma akan ki zan rama wa ummin inga ta tsiya.
Alhaji babba yace, kada kai ma kazama su mana aminu.
Tsohuwa tace, gskiya ne, in har tazama silar dukan ummi itama sai ya mata taji.
Umma tace, a'a duk abin ba zai kai haka ba insha Allahu, kai dai abba kayi ta hakuri sannan kadaina sa hannu kana dukan mace.
Yace, umma dukana fa tayi, sai kace wani soko zan tsaya mce tna dukana, umma tace, to ai tace ummi taje duka, yace ummin 'yarta ce?