Sashe 38
Zurfin Ciki Part 1 - 4 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yayin da
zuciyarta take fara kar, ta sani kuma tayi Imani
Allah ba ya tozarta addu'ar bawansa, matsawar
bawan yayi hakuri tare da dogewa.
Haka nan in
baka samu biyan bukatarka nan duniya ba lallai
gobe kiyama zaka tarar da abinka.
Ta jima tana
rokon Allah yasa 'ya'yan nata biyu su zam miji
da mata su haifa mata jikoki masu albarka.
Suma
su Alhaji suna ta sallamar baki sai dai yanzun ba
wanda ya damu ya gani irin Abba.
Fatanshi Allah
yasa Abban yayi farin ciki da wannan hukunci da
suka yanke.
Salis kuwa burinshi ya zama shi ne
mutum na farko da zai wa Abba wannan albishir
sai dai ya kira layin Abba sama da sau hamsim
bai daga ba.
Abinda bai sani ba shi Abba ma gida
ya bar wayar, haka suka gama dauke-daukensu
yayi hira da Jama'a da kuma iyayen Ango da
Amarya don jin ta bakinsu a kan yanda auren ya
juye zuwa na zumunci.
Haka nan suka tafi ya
samu abin sawa a Taskar labarai, burinshi yanzu
shi ne ya je ya nemo angon. 28 50.....Abba kam
kofar dan Agundi ya yada zango gidan su Mansir
abokinsu, shi ne kurum cikin abokan Abba da bai
yi aure ba.
Yana isa kofar gidan Mansur na
fitowa za shi daurin auren, wani dan layinsu a
Gwammaja suka gaisa.
Abba ya ce "Bari in dan
kwanta a dakinka".
Mansur cikin mamaki ya ce,
Lafiya?
Abba ya ce lafiya lau.
Yana kwance dakin
Mansur idanunshi suna kallon agogo, zuciyarshi
tana raya yanzun abar sonshi ta zama matar
Sahabi.
Sai dai bai san dalilin da bugawar
agogon karfe sha daya daidai tazo gwame da
bugawar zuciyarshi ba.
Zuciyarshi ta fada mishi
cewa wannan alamu ne na an kammala daurin
auren.
Wasu hawaye ne suka biyo ta gefen
idanunshi suna sauka a kan filon.
Yini zur yana
dakin in lokacin sallah yayi sai ya fito kofar dakin
yayi alwala har duhun Magriba ya gabato.
Ya fito
tare da kulle dakin, don Mansur bai dawo ba,
kuma dama ya ce ba zai dawo da wuri ba.
Gidan
nashi ba kowa lokacin da ya shiga, kai tsaye
dakinshi ya wuce, ban da idanunshi da suka kai
kan wayarshi ya manta ma yana mallakinta.
Ya
kai hannu ya dauka, bai ji mamakin yawan
missed calls din da ya gani ba, kiran Salis ya
sake shigowa.
A kasale ya daga, muryar Salis ta
ratsa dodon kunnanshi, fadi yake yana
maimaitawa Ango- Ango.
Abba cikin sanyin
murya ya ce "Salis ya haramta a gare ka ka
zolaye ni a halin da nake ciki.
Sanin kanka kai
kadai ne kasan yanayin da nake ciki".
Salis cikin
zumudi ya ce, "Kana nufin ba ka sani ba?" Abba
ya ce, "Me?" Salis ya ce "To bani goron albishir in
sanar da kai".
Abba ya ce, "Don Allah Salis kada
ka min karya".
Salis ya ce, "Ina rantsuwa da
wanda ya yi mu Ummi matarka ce, da kai a ka
daura.
Ina ka shige lokacin da al'amarin ya canza
salo?" Abba ya mike zumbur.
"Ka fa rantse Salis!"
cikin dariya Salis ya ce, "Wai har yanzun ba ka
sani ba?
To ka aje min goron albishir dina".
Abba
yasa hannunshi a baki ya gatsa, zafin da ya ji ne
ya tabbatar da mishi da ba mafarki yake ba. 51...
Ai sai ya katse wayar ya zube yayi sujjada ya fita
tsakar gida yana furta "Alhamdulillah." Ruwa yaja
ya watsa ma jikinshim sannan ya yi alwala.
Sabuwar shadda ya saka kalar kunkumadi, ya
fesa turare sama da kala hudu.
Hula da takalmin
bakake, ya nufi Masallaci, daga can za shi gidan
su Umma don jin karin bayani.
Bayan sun idar da
Sallah, mutane suka yi ta masa murna, nan ya
hadu da su Alhaji kawai yau sai ya samu kansa
da kunyar Alhajin.
Alhaji ya ce, "Ubana ina ka
shige duk yau?" Ya rasa me zai ce, sai in-ina
"Am...na kwanta ne bana jin dadi".
Alhaji yayi
'yar dariya, "Kai dai ka ce kana taya kanwarka
fushi don mun ce ba zamu daga aure ba, to ba
mu daga ba amma Allah cikin ikonsa ya sauya
lamarin".
Abba tamkar bai san komai ba, ya ce
"Alhaji me kuma ya faru?" Alhaji Karami ya
karaso gurin su yana cewa, "Kai Abba ina ka
shige ne?" Abba ya dube shi "Nan dan Agundi na
shiga".
Alhaji ya ce, "Oho, shi yasa aka yi ta
nemanka.
To ka ji kuma yadda lamari ya sauya
ko?" Alhaji Babba ya amsa tare da cewa, "Shi ne
nake massa bayani, wato Abba iyayen yaron nan
Sahabi muka yi ta jiransu su zo gurin daurin
aure, wai ashe su sun fasa.
Amma ba su shaida
mana ba har bin su fa nasa aka yi, gashi mun
tara jama'a kawai sai Aminu da Ummanka suka
ce a daura da kai, da ni na ce a daura da Bashir".
Dadi ya lullu6e Abba irin wanda bai ta6a ji ba,
Alhaji ya ci gaba da cewa, kayi hakuri mun kara
maka nauyi ba tare da mun ji ra'ayinka ba".
Abba
cikin matukar murna ya ce, "Haba, ai ko ba 'yar
uwata ba ku ka daura min aure da ita zan aminta
bare jinina.
Nagode".
Sun ji mamakin yanda Abba
yayi murna, duk da sun san biyayya irin tashi ba
zai 'ki ba, tare suka rankaya gidan su Umman, so
kurum yake yaga Ummi.
Ba mutane sosai, don
haka har ciki ya kutsa, sai dai suna hada ido da
Umma sai ya ji nauyinta, ta fada da fara'a.
"Ina
ka shige Abba?" Yayi dan murmushi, ta ci gaba
"Sai kuma ka ji yanda abu ya kasance?" Ya ce,
"Na ji Umma, Allah yasa haka shi ne alkairi".
Ta
ce, "Amin, Insha Allahu".
Tamkar ya tambayi ina
Ummin, amma ya kasa.
Umma ta ce "A baka
abinci ko?" sai lokacin ya tuna da batun abinci,
amma baya gabanshi, ya ce "Na koshi Umma".
Ta ce, "To ga na 'yan asibiti can in kayi isha'i".
Da sauri ya ce "Wa ke asibiti kuma?" Ta ce,
"Ummi ce, ko 'yan daurin auran ba su watse ba
don ka ji yarintar nan ta hau farin suma don
haushi ko leka su ban yi ba.
Tana can it da
Saratu sai Tsohuwa da ta matsa yanzun Alhaji
Karami ya kai ta".
Jikin Abba ya yi sanyi, kenan
tsabar rashin sonshi ne ya saka Ummi suma?
Ya
ce Umma bani abincin asibitin.
Sai da yaje
gidanshi ya dauko dan mukullin motar, a
zuciyarshi yana tambayar kanshi ina kuma
Bishira tayi ne?
Zai bude motar kenan muryar
Bashir ta dakar da shi, "Kaci nasarar samun furen
zuciyata, amma ka sani ka kulla abota da rashin
zaman lafiya a novels / ZURFIN CIKI book 3 part 7
ZURFIN CIKI book 3 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:33
kulla abota da rashin zaman lafiya a gidanka". *
52..A fusace abba ya dubeshi"xansa yan sanda
su rufe min kai inhar zaka cigaba da kiran matata
da furen zuciyarka,rashin zaman lfy kake cewa?
An dade ba'ayi yaki abgdn ba kullum,bashir yace
oho dai ni zanta zuga umma abba yaja tsaki
tareda shigewa motarshi.
Bashir yashiga gdnsu
inda su ummanshi dasu bishirabke zaune jugum
jugum tamkar masu zaman makoki,bishira tabi
bashir da kallo lkcn dayace ga ya abba ya can a
waje yashiga mota ya kure wanka,kila ma asibiti
zaije ana fada maku yanaso kuna wani tilasta shi
akayi,bishira cikin dasahhshiyar murya tace aiko
da bala'i don ko bazan yarda ba,umman bashir
tace sha kutuminki bishira,barni dasu zan
maganinsu, bishira tafita fuu,amma saidai.
Kafin
ta isa gurin motar tuni ya, Cilla yabar mata
hayaki.
Da innna saratu kanwar umma ya soma
cin karo a asibitun suka gaisa,tace ashe kuma
haka abu ya zama?
Yace eh"nima dana dawo
dazu nasamu lbrin,tace Allah yasa hakan shine
mafi alkhairi,abba yace ameen inna,ya mai jikin?
Tace dasauki,yace bacci take?
Tace a'a ta farka
tun kusan karfe uku,koda fatima ta fada mata
yanda abubuwa zuka zama,tayita yan koke
kokenta,gaban abba yafadi****tabbas ummi ba
son shi take ba inba hka ba meye na kuka?
Ya
kalli inna bari in karasa,tace to kaje tshuwa na
ciki,a ranshi yace jaraba road,yasan dai ko yane
sai tshuwa tayi mishi surutu,yana tura kofar
tareda salama suka hada ido da ummi,sun kure
juna da kallo,kowanne nason ya fahimci ya dan
uwansa yadauki abin"tshuwa ta katse su dacewa
to zakin fama sai ynz kaga daman zuwa?
Ya
dubeta eh" ai eh ace?
To me kikeso ince,tace to
madalla ai na dade da sanin halinka,kuma da ace
iyayenku sunyi shawara dani lallai da baza suyi
wanna hadin ba Domin na tabbata kai zaka
karasa takwara don baka kaunarta, haushi ya
cika abba abba yana kallon tsohuwa yana tuna
amsar data dace da ita, ummi kuwa tsura mishi
ido tayi tana son jin me zaice,yace kamar kin
sani,tace ahaf shiyasa tausan yar nan kebani
tausayi, ta soma matsar ido,yace nima yakamata.
ki tausayamin tnda cusa min ita akayi,ummi
takoma ta kwanta lakwas tareda hakikancewabl
kalaman abba sako ne zuwa gareta,matar cushe
kuma bata daraja,to inaso kasan wani abu
guda,duk randa naji wani abu daidai da
wulakanci, toba kaiba har iyayenka saisun san
naje makura. 52..Dazun nake gaya masu basun
hada kai sun kulla auren nan ba,duk randa suka
kuskura sukazo min da batun warwareshi saina
basu mamaki,abba ya tabe baki tareda kallon
ummi wadda takasa jurewa tashiga rera kuka,ya
isa gaban gadon,"jikin ne ummi?
Tayi shuru,kinci
abinci?
Nan ma ta share,sai kurum ya nufi wurin
likitan zuciyarshi na kuna bako shakka kukan kin
shi ummi keyi,sun zo da likita ya shiga yimata
fadan kukan da takeyi,a cewar likitan kukan illa
ne ga lafiyarta,tshuwa ta kalli likita dan nan dole
ta koka a dauke ka ahadaka da wanda baya
kaunarka"abba cikin takaici yace subhanallla!
Don
Allah tshuwa kibarni inji da abinda ke
gabana,tace ina ruwana da abinda ke
gabanka,likita yayi dariya yace mama yakamata
ki koma gd haka,abba yace bari inkaita
indawo,tace ban binka da can dani kazo?
zuciyarta take fara kar, ta sani kuma tayi Imani
Allah ba ya tozarta addu'ar bawansa, matsawar
bawan yayi hakuri tare da dogewa.
Haka nan in
baka samu biyan bukatarka nan duniya ba lallai
gobe kiyama zaka tarar da abinka.
Ta jima tana
rokon Allah yasa 'ya'yan nata biyu su zam miji
da mata su haifa mata jikoki masu albarka.
Suma
su Alhaji suna ta sallamar baki sai dai yanzun ba
wanda ya damu ya gani irin Abba.
Fatanshi Allah
yasa Abban yayi farin ciki da wannan hukunci da
suka yanke.
Salis kuwa burinshi ya zama shi ne
mutum na farko da zai wa Abba wannan albishir
sai dai ya kira layin Abba sama da sau hamsim
bai daga ba.
Abinda bai sani ba shi Abba ma gida
ya bar wayar, haka suka gama dauke-daukensu
yayi hira da Jama'a da kuma iyayen Ango da
Amarya don jin ta bakinsu a kan yanda auren ya
juye zuwa na zumunci.
Haka nan suka tafi ya
samu abin sawa a Taskar labarai, burinshi yanzu
shi ne ya je ya nemo angon. 28 50.....Abba kam
kofar dan Agundi ya yada zango gidan su Mansir
abokinsu, shi ne kurum cikin abokan Abba da bai
yi aure ba.
Yana isa kofar gidan Mansur na
fitowa za shi daurin auren, wani dan layinsu a
Gwammaja suka gaisa.
Abba ya ce "Bari in dan
kwanta a dakinka".
Mansur cikin mamaki ya ce,
Lafiya?
Abba ya ce lafiya lau.
Yana kwance dakin
Mansur idanunshi suna kallon agogo, zuciyarshi
tana raya yanzun abar sonshi ta zama matar
Sahabi.
Sai dai bai san dalilin da bugawar
agogon karfe sha daya daidai tazo gwame da
bugawar zuciyarshi ba.
Zuciyarshi ta fada mishi
cewa wannan alamu ne na an kammala daurin
auren.
Wasu hawaye ne suka biyo ta gefen
idanunshi suna sauka a kan filon.
Yini zur yana
dakin in lokacin sallah yayi sai ya fito kofar dakin
yayi alwala har duhun Magriba ya gabato.
Ya fito
tare da kulle dakin, don Mansur bai dawo ba,
kuma dama ya ce ba zai dawo da wuri ba.
Gidan
nashi ba kowa lokacin da ya shiga, kai tsaye
dakinshi ya wuce, ban da idanunshi da suka kai
kan wayarshi ya manta ma yana mallakinta.
Ya
kai hannu ya dauka, bai ji mamakin yawan
missed calls din da ya gani ba, kiran Salis ya
sake shigowa.
A kasale ya daga, muryar Salis ta
ratsa dodon kunnanshi, fadi yake yana
maimaitawa Ango- Ango.
Abba cikin sanyin
murya ya ce "Salis ya haramta a gare ka ka
zolaye ni a halin da nake ciki.
Sanin kanka kai
kadai ne kasan yanayin da nake ciki".
Salis cikin
zumudi ya ce, "Kana nufin ba ka sani ba?" Abba
ya ce, "Me?" Salis ya ce "To bani goron albishir in
sanar da kai".
Abba ya ce, "Don Allah Salis kada
ka min karya".
Salis ya ce, "Ina rantsuwa da
wanda ya yi mu Ummi matarka ce, da kai a ka
daura.
Ina ka shige lokacin da al'amarin ya canza
salo?" Abba ya mike zumbur.
"Ka fa rantse Salis!"
cikin dariya Salis ya ce, "Wai har yanzun ba ka
sani ba?
To ka aje min goron albishir dina".
Abba
yasa hannunshi a baki ya gatsa, zafin da ya ji ne
ya tabbatar da mishi da ba mafarki yake ba. 51...
Ai sai ya katse wayar ya zube yayi sujjada ya fita
tsakar gida yana furta "Alhamdulillah." Ruwa yaja
ya watsa ma jikinshim sannan ya yi alwala.
Sabuwar shadda ya saka kalar kunkumadi, ya
fesa turare sama da kala hudu.
Hula da takalmin
bakake, ya nufi Masallaci, daga can za shi gidan
su Umma don jin karin bayani.
Bayan sun idar da
Sallah, mutane suka yi ta masa murna, nan ya
hadu da su Alhaji kawai yau sai ya samu kansa
da kunyar Alhajin.
Alhaji ya ce, "Ubana ina ka
shige duk yau?" Ya rasa me zai ce, sai in-ina
"Am...na kwanta ne bana jin dadi".
Alhaji yayi
'yar dariya, "Kai dai ka ce kana taya kanwarka
fushi don mun ce ba zamu daga aure ba, to ba
mu daga ba amma Allah cikin ikonsa ya sauya
lamarin".
Abba tamkar bai san komai ba, ya ce
"Alhaji me kuma ya faru?" Alhaji Karami ya
karaso gurin su yana cewa, "Kai Abba ina ka
shige ne?" Abba ya dube shi "Nan dan Agundi na
shiga".
Alhaji ya ce, "Oho, shi yasa aka yi ta
nemanka.
To ka ji kuma yadda lamari ya sauya
ko?" Alhaji Babba ya amsa tare da cewa, "Shi ne
nake massa bayani, wato Abba iyayen yaron nan
Sahabi muka yi ta jiransu su zo gurin daurin
aure, wai ashe su sun fasa.
Amma ba su shaida
mana ba har bin su fa nasa aka yi, gashi mun
tara jama'a kawai sai Aminu da Ummanka suka
ce a daura da kai, da ni na ce a daura da Bashir".
Dadi ya lullu6e Abba irin wanda bai ta6a ji ba,
Alhaji ya ci gaba da cewa, kayi hakuri mun kara
maka nauyi ba tare da mun ji ra'ayinka ba".
Abba
cikin matukar murna ya ce, "Haba, ai ko ba 'yar
uwata ba ku ka daura min aure da ita zan aminta
bare jinina.
Nagode".
Sun ji mamakin yanda Abba
yayi murna, duk da sun san biyayya irin tashi ba
zai 'ki ba, tare suka rankaya gidan su Umman, so
kurum yake yaga Ummi.
Ba mutane sosai, don
haka har ciki ya kutsa, sai dai suna hada ido da
Umma sai ya ji nauyinta, ta fada da fara'a.
"Ina
ka shige Abba?" Yayi dan murmushi, ta ci gaba
"Sai kuma ka ji yanda abu ya kasance?" Ya ce,
"Na ji Umma, Allah yasa haka shi ne alkairi".
Ta
ce, "Amin, Insha Allahu".
Tamkar ya tambayi ina
Ummin, amma ya kasa.
Umma ta ce "A baka
abinci ko?" sai lokacin ya tuna da batun abinci,
amma baya gabanshi, ya ce "Na koshi Umma".
Ta ce, "To ga na 'yan asibiti can in kayi isha'i".
Da sauri ya ce "Wa ke asibiti kuma?" Ta ce,
"Ummi ce, ko 'yan daurin auran ba su watse ba
don ka ji yarintar nan ta hau farin suma don
haushi ko leka su ban yi ba.
Tana can it da
Saratu sai Tsohuwa da ta matsa yanzun Alhaji
Karami ya kai ta".
Jikin Abba ya yi sanyi, kenan
tsabar rashin sonshi ne ya saka Ummi suma?
Ya
ce Umma bani abincin asibitin.
Sai da yaje
gidanshi ya dauko dan mukullin motar, a
zuciyarshi yana tambayar kanshi ina kuma
Bishira tayi ne?
Zai bude motar kenan muryar
Bashir ta dakar da shi, "Kaci nasarar samun furen
zuciyata, amma ka sani ka kulla abota da rashin
zaman lafiya a novels / ZURFIN CIKI book 3 part 7
ZURFIN CIKI book 3 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:33
kulla abota da rashin zaman lafiya a gidanka". *
52..A fusace abba ya dubeshi"xansa yan sanda
su rufe min kai inhar zaka cigaba da kiran matata
da furen zuciyarka,rashin zaman lfy kake cewa?
An dade ba'ayi yaki abgdn ba kullum,bashir yace
oho dai ni zanta zuga umma abba yaja tsaki
tareda shigewa motarshi.
Bashir yashiga gdnsu
inda su ummanshi dasu bishirabke zaune jugum
jugum tamkar masu zaman makoki,bishira tabi
bashir da kallo lkcn dayace ga ya abba ya can a
waje yashiga mota ya kure wanka,kila ma asibiti
zaije ana fada maku yanaso kuna wani tilasta shi
akayi,bishira cikin dasahhshiyar murya tace aiko
da bala'i don ko bazan yarda ba,umman bashir
tace sha kutuminki bishira,barni dasu zan
maganinsu, bishira tafita fuu,amma saidai.
Kafin
ta isa gurin motar tuni ya, Cilla yabar mata
hayaki.
Da innna saratu kanwar umma ya soma
cin karo a asibitun suka gaisa,tace ashe kuma
haka abu ya zama?
Yace eh"nima dana dawo
dazu nasamu lbrin,tace Allah yasa hakan shine
mafi alkhairi,abba yace ameen inna,ya mai jikin?
Tace dasauki,yace bacci take?
Tace a'a ta farka
tun kusan karfe uku,koda fatima ta fada mata
yanda abubuwa zuka zama,tayita yan koke
kokenta,gaban abba yafadi****tabbas ummi ba
son shi take ba inba hka ba meye na kuka?
Ya
kalli inna bari in karasa,tace to kaje tshuwa na
ciki,a ranshi yace jaraba road,yasan dai ko yane
sai tshuwa tayi mishi surutu,yana tura kofar
tareda salama suka hada ido da ummi,sun kure
juna da kallo,kowanne nason ya fahimci ya dan
uwansa yadauki abin"tshuwa ta katse su dacewa
to zakin fama sai ynz kaga daman zuwa?
Ya
dubeta eh" ai eh ace?
To me kikeso ince,tace to
madalla ai na dade da sanin halinka,kuma da ace
iyayenku sunyi shawara dani lallai da baza suyi
wanna hadin ba Domin na tabbata kai zaka
karasa takwara don baka kaunarta, haushi ya
cika abba abba yana kallon tsohuwa yana tuna
amsar data dace da ita, ummi kuwa tsura mishi
ido tayi tana son jin me zaice,yace kamar kin
sani,tace ahaf shiyasa tausan yar nan kebani
tausayi, ta soma matsar ido,yace nima yakamata.
ki tausayamin tnda cusa min ita akayi,ummi
takoma ta kwanta lakwas tareda hakikancewabl
kalaman abba sako ne zuwa gareta,matar cushe
kuma bata daraja,to inaso kasan wani abu
guda,duk randa naji wani abu daidai da
wulakanci, toba kaiba har iyayenka saisun san
naje makura. 52..Dazun nake gaya masu basun
hada kai sun kulla auren nan ba,duk randa suka
kuskura sukazo min da batun warwareshi saina
basu mamaki,abba ya tabe baki tareda kallon
ummi wadda takasa jurewa tashiga rera kuka,ya
isa gaban gadon,"jikin ne ummi?
Tayi shuru,kinci
abinci?
Nan ma ta share,sai kurum ya nufi wurin
likitan zuciyarshi na kuna bako shakka kukan kin
shi ummi keyi,sun zo da likita ya shiga yimata
fadan kukan da takeyi,a cewar likitan kukan illa
ne ga lafiyarta,tshuwa ta kalli likita dan nan dole
ta koka a dauke ka ahadaka da wanda baya
kaunarka"abba cikin takaici yace subhanallla!
Don
Allah tshuwa kibarni inji da abinda ke
gabana,tace ina ruwana da abinda ke
gabanka,likita yayi dariya yace mama yakamata
ki koma gd haka,abba yace bari inkaita
indawo,tace ban binka da can dani kazo?