Sashe 80
Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ashe mijinki mutumen banza ne, fyade yayi ma Hana shiyasa kuka rabu, kuma aka boye min? Magana mai girma haka? To ba zan bar wannan ba, Wallahi sai na ja hakkin yata ba zan bari a tafi a banza ba, sai na yi karar ubansa”
Na saki wayar hannuna da jakata da mayafin duka suka zube a kasa.
“Baba a ina ka ji wannan? Ba gaskiya ba ne sheri ne...”
“Sheri? Ai abun duniya baya boya ina zamana wata mata ta zo ta fada min”
Na dafe kaina.
“Innalillahi Wa'inna Illaihirraji'un, Baba ba gaskiya ba ne, kawai na gaji da zama da shi ne muka rabu”
“Kika sake magana sai na tsine miki albarka ma, har matar da ta cirewa Hana ciki na ganta da idona na yi magana da ita, kuma ba zan bar maganar nan ba”
Hana ta girgiza min kai tana kuka ni ma kukan na fara Umma kuma ta saka salati yana tabi da rike baki...
Pay 500 to
2451879008
Zenith Bank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.Ya rigata isa domin shi yake son magana da ita a yanzu, a yanzu ikon a gurinta yake hakan ya saka ta bata masa lokaci na tsawon mintuna arba'in sannan ta shigo gidan. Yana tsaye ta window falon yana kallonta har ta fito motarsa ta turo kofar falon ta shigo.
“Lafiya kake son ganina?”
“Me kike so Safeena”
Kamar jira take sai ta sauke gyalenta ta aje jakar a kujera ta nufo shi tana nuna shi.
“Kai Kareem kai nake so!”
“To miye matsalarki da Noor? Miyasa kike cusata a cikin matsalarmu?”
Ya tambaya ba tare da ua juyo ba hannayensa duka biyu suna zube a aljihunsa.
“Saboda Noor ce ta raba ni da kai, Noor ce macen da ta cike gurbina da ita, kuma ita ce ta kashe min auren da takardar kawai ya rage Abdull ya ba ni”
“Ban cike gurbinki da na noor ba, wani gurbi na gina mata mai kyau mai tsabta, mai cike da kauna da soyayya, dan Allah ki cireta a cikin matsalarki”
Har lokacin da yake maganar be juyo ya kalleta ba.
“Ita ce babbar matsalata a rayuwar nan Kareem, ta lalata min aure tun da mijina ya dauki yaran nan ya tafi da su ya auna jininsu be sake dawowa gidan nan ba, last week ya aiko kanensa ya dauki yaransa biyu aka bar karamin da na haifa da kai, yanzu haka mijina yana garin nan amman be tako kafarsa gidana ba, ya daina min aike ya daina kulani baya amsa wayata baya ba ni amsar sakona, na sani saki na zai yi bayaj ya gama kwance min zane a kasuwa, zai saka kowa ya tsane ni a danginmu saboda abun da na aikata Mijina cousin dina ne, kuma duk sanadin Noor ce ne domin ita kadai ta san sirrina ita kadai zata iya fallasa wannan”
Ya juyo ya kalleta.
“Ta aikata kuskure na fahimta, mu ma mun aikata dukanmu mutane ne, amman saboda me zaki lalata rayuwar kanwata me ya shigo da kanwarta ciki? Kina da tabbacin Abdull din ne ya aikata?”
Ta matsa kusa da shi tana masa wani kallo na tsana for the first time.
“To waya aikata kai? Ko kuma dai ita ta aikatawa kanta?”
“Baki da tabbacin Safeena karki jefa rayuwarki a matsala”
Ta yi wani shu'imin murmushi.
“Na san komai Kareem kai ka san wacece ni, ina da tabbaci mana, a gabana ka kira kawata ina jin muryarka lokacin da kake fada mata cewar wata yarinya kake son ta yi ma wankin ciki ka mata allura amman dai ka fi son a wanke saboda ka samu tabbacin komai ya zube, ka fada mata kaddara ce ta hau kan yarinyar fyade aka yi mata ko ba haka ba?”
“Ita Juwairiyya ce ta fada miki haka?”
“No Wallahi bata fada min komai ba, amman na ari wayarta na duba bangaren kira sai na ga number ka, daman kuma na ji muryarka domin wayarta ana ji duk abun da mutum ke fada sound din kiranta a karshe yake, lokacin da na duba zuciyata ta fada min Hana ce, there is no way da zai saki Noor da ciki ba tare da wani abu ba, kuma ya fadawa yan'uwansa wai ta tayar masa da fitina ne sai ya sake ta shi kuma ya sake ta saboda TA KI ZAMAN AURE, kana ganin hankalina zai dauka? Idan babu wani abu me zai saka Noor ta fada masa cewar dan da na haifa ba na shi ba ne? Mw zai saka yar'uwarta ya yanke karatunta da duk wani gata da yake musu ta dawo ita da kanwarta su zauna a gida? Daman ni ban yarda ba na san akwai wani abu a kasa, domin na san waye mijina ba kasafai yake iya rike kansa ba, a tsawon watanin da yake a Lagos da sunan aiki na san me yake aikatawa, kawai na zuba masa ido ne saboda babu yadda zan yi, kana tunanin namiji zai saka al'adar neman mata a gaba kamar yadda Abdull yake kuma ace matarsa bata sani ba?”
Ta share hawayen da suka zubo mata cikin daga murya ta cigaba da fadar.
“Neman matansa ya taimaka min gurin bibiyarka da kokarin kulla alaka da kai Kareem, na san yana neman mata tun kamin na aure shi, na aure shi ne saboda an matsa min a gidanmu na yi aure, kai kumaka guje ni, duniya ta min zafi, shi kadai ne mutumen da ya zo zai share min hawaye a lokacin, bayan mun yi aure ya zama bana burge shi saboda ya saba da matan waje, mijina ba shi da lokacina, baya ganin kyauna, ba ya ganin ado na, kullum idonsa akan matan waje ne, mijina baya iya gamsar da ni yadda kake min Kareem, gaba daya ban yi dacen rayuwa ba, amman a haka nake zaune kullum burina idan har na bar Abdull kai ne”
Wannan karon da cinyar hannu ta goge hawaye idonta na dama.
“Na san na yi kuskure na haihuwar ba ta sunna ba, dukanmu yin yi kuskure amman sai mu rumgumi wannan kaddarar, nan gaba kadan Abdull sakina zai yi, to sai ka aure ni mana Kareem”
Ya juyo da kyau ya fuskance ta.
“Ba zan taba aurenki ba, amman zan tabbatar maki da abu daya, Noor ba zata aure ni ba, saboda bana cikin mazan da take so, please ki cireta a cikin matsalarki”
“I don't care ka auri Noor ko karka aureta ba matsalata ba ce, abun da kawai na damu da shi, shi ne idan Abdull ya sake ni zaka aure ni”
“Har abada ba zan taba aurenki ba, aure ya haramta a tsakaninmu”
Ta rausayar da kai tana murmushi.
“Na fahimci hakan ai, shiyasa na bullowa ubanta ta wannan sigar na fada masa gaskiya kuma na kwadaita masa dukiyar da zai samu idan ya Abdull ko mahaifinsa suka bukaci a sirrinta abun, na samu wata kawata muka je a zuwan ita ce nurse din da ta cire ciki, kuma na samu kudi mai kauri na ba shi. Ka ga yanzu hankalin Abdull zai koma gurin abun da ya aikata ne ba wanda zai aikata a gareni ba, kuma idan ya fallasa sirrina duniya zata zage mu a gaba dayanmu mu uku, kai ni da kuma shi”
Kareem ya sasauta fuskarsa ba dan tsoron furucinta ba sai dan yana son ta fahimcin illar fa hakan zai mata ba mijinta kadai ba. Ya busar da iskar bakinsa ya jin kirjinsa na ciwo sosai.
“Ki rika yin tunani kamin ki aikata abu, kina da yaya Safeena, tun farko baki rike aurenki kika biyewa shaidan muka aikata alfasha, hakan be wadatar da ke ba sai da kika ga mun haihuwa, yanzu gashi abun ya dawo yana bibiyarmu, kuma duk yadda wannan abun zai taba ni be kai yadda ke zai miki illa ba Safeena, saboda ke mace ce ni kuma namiji ne, shiyasa da Allah zai ambacin mazinata a kur'ane sai ya fara da mace, domin ita ce mai rauni kuma ita ce mai shiga kaso 90 na matsala sama da namiji”
“Zaka aure ni Kareem? Ka min alkawari kawai zaka aure ni Wallahi zan yi duk yadda zan iya mahaifinta ya janye shari'ar nan”
Ya cire hannunsa daya a aljihu yana nuna mata.
“Let me make this clear to you, idan har zan sake wani aure a rayuwata, to mace daya ce zan aura Noor, idan har ba zan auri ba ba zan sake aure ba, so ki saka a ranki ni da ke ba mu taba sanin juna ba, ba zan taba aurenki ba Safeena!!”
Wani mugun kallo take masa zuciyarta na bugawa da karfi. Cikin ihu da takiya ta ce
“Ba zan saka ya janye shari'a ba Kareem kuma zan daukar masa lauya, domin ina bukatar abun da zai daga hankalin Noor ya zubar da mutuncinta da na iyayenta ya kashe auren uwarta ya jafata a matsala, ba ni da makiyaya a duniya irin Noor yarinyar da saboda ita igiyar aurena take rawa? Saboda ita juya min baya, yar sikar yarinya shashasha mahaukaciya, yarinya da bata kai ta goge talkamin kafata ba, yarinyar da bata kai ka rika hannunta ba, amman ita kake so? Yarinyar da ubanta baya jin wani yare sai na kudi? Yarinyar da ubanta be san wani mutuncin ba sai na kudi? Yarinyar da babu komai akanta sai hauka da gidadanci, fasika da bata iya komai ba sai bibiyar mazan mutane yarinyar da...”
Tassssss ta ji saukar lafiyayyen mari a fuskarta daga hannun masoyinta Kareem, Wani irin numfashi taja da karfi ta kai hannu ta dafe kuncin hawaye masu zafi na sauko mata. Cikin wani irin bacin rai da Kareem be san yana da shi ba ya nuna ta da yatsa ya ce.
“Kul bakinki ya sake kiran Noor dita da wata kalma marar kyau, iyakar kiyayar da kike mata saboda tana da alaka da ni ne, ni kuma ba aurena zata yi ba, ki fadawa mahaifinta karya kike ya janye shari'ar nan idan ba haka ba...”
Na saki wayar hannuna da jakata da mayafin duka suka zube a kasa.
“Baba a ina ka ji wannan? Ba gaskiya ba ne sheri ne...”
“Sheri? Ai abun duniya baya boya ina zamana wata mata ta zo ta fada min”
Na dafe kaina.
“Innalillahi Wa'inna Illaihirraji'un, Baba ba gaskiya ba ne, kawai na gaji da zama da shi ne muka rabu”
“Kika sake magana sai na tsine miki albarka ma, har matar da ta cirewa Hana ciki na ganta da idona na yi magana da ita, kuma ba zan bar maganar nan ba”
Hana ta girgiza min kai tana kuka ni ma kukan na fara Umma kuma ta saka salati yana tabi da rike baki...
Pay 500 to
2451879008
Zenith Bank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660.Ya rigata isa domin shi yake son magana da ita a yanzu, a yanzu ikon a gurinta yake hakan ya saka ta bata masa lokaci na tsawon mintuna arba'in sannan ta shigo gidan. Yana tsaye ta window falon yana kallonta har ta fito motarsa ta turo kofar falon ta shigo.
“Lafiya kake son ganina?”
“Me kike so Safeena”
Kamar jira take sai ta sauke gyalenta ta aje jakar a kujera ta nufo shi tana nuna shi.
“Kai Kareem kai nake so!”
“To miye matsalarki da Noor? Miyasa kike cusata a cikin matsalarmu?”
Ya tambaya ba tare da ua juyo ba hannayensa duka biyu suna zube a aljihunsa.
“Saboda Noor ce ta raba ni da kai, Noor ce macen da ta cike gurbina da ita, kuma ita ce ta kashe min auren da takardar kawai ya rage Abdull ya ba ni”
“Ban cike gurbinki da na noor ba, wani gurbi na gina mata mai kyau mai tsabta, mai cike da kauna da soyayya, dan Allah ki cireta a cikin matsalarki”
Har lokacin da yake maganar be juyo ya kalleta ba.
“Ita ce babbar matsalata a rayuwar nan Kareem, ta lalata min aure tun da mijina ya dauki yaran nan ya tafi da su ya auna jininsu be sake dawowa gidan nan ba, last week ya aiko kanensa ya dauki yaransa biyu aka bar karamin da na haifa da kai, yanzu haka mijina yana garin nan amman be tako kafarsa gidana ba, ya daina min aike ya daina kulani baya amsa wayata baya ba ni amsar sakona, na sani saki na zai yi bayaj ya gama kwance min zane a kasuwa, zai saka kowa ya tsane ni a danginmu saboda abun da na aikata Mijina cousin dina ne, kuma duk sanadin Noor ce ne domin ita kadai ta san sirrina ita kadai zata iya fallasa wannan”
Ya juyo ya kalleta.
“Ta aikata kuskure na fahimta, mu ma mun aikata dukanmu mutane ne, amman saboda me zaki lalata rayuwar kanwata me ya shigo da kanwarta ciki? Kina da tabbacin Abdull din ne ya aikata?”
Ta matsa kusa da shi tana masa wani kallo na tsana for the first time.
“To waya aikata kai? Ko kuma dai ita ta aikatawa kanta?”
“Baki da tabbacin Safeena karki jefa rayuwarki a matsala”
Ta yi wani shu'imin murmushi.
“Na san komai Kareem kai ka san wacece ni, ina da tabbaci mana, a gabana ka kira kawata ina jin muryarka lokacin da kake fada mata cewar wata yarinya kake son ta yi ma wankin ciki ka mata allura amman dai ka fi son a wanke saboda ka samu tabbacin komai ya zube, ka fada mata kaddara ce ta hau kan yarinyar fyade aka yi mata ko ba haka ba?”
“Ita Juwairiyya ce ta fada miki haka?”
“No Wallahi bata fada min komai ba, amman na ari wayarta na duba bangaren kira sai na ga number ka, daman kuma na ji muryarka domin wayarta ana ji duk abun da mutum ke fada sound din kiranta a karshe yake, lokacin da na duba zuciyata ta fada min Hana ce, there is no way da zai saki Noor da ciki ba tare da wani abu ba, kuma ya fadawa yan'uwansa wai ta tayar masa da fitina ne sai ya sake ta shi kuma ya sake ta saboda TA KI ZAMAN AURE, kana ganin hankalina zai dauka? Idan babu wani abu me zai saka Noor ta fada masa cewar dan da na haifa ba na shi ba ne? Mw zai saka yar'uwarta ya yanke karatunta da duk wani gata da yake musu ta dawo ita da kanwarta su zauna a gida? Daman ni ban yarda ba na san akwai wani abu a kasa, domin na san waye mijina ba kasafai yake iya rike kansa ba, a tsawon watanin da yake a Lagos da sunan aiki na san me yake aikatawa, kawai na zuba masa ido ne saboda babu yadda zan yi, kana tunanin namiji zai saka al'adar neman mata a gaba kamar yadda Abdull yake kuma ace matarsa bata sani ba?”
Ta share hawayen da suka zubo mata cikin daga murya ta cigaba da fadar.
“Neman matansa ya taimaka min gurin bibiyarka da kokarin kulla alaka da kai Kareem, na san yana neman mata tun kamin na aure shi, na aure shi ne saboda an matsa min a gidanmu na yi aure, kai kumaka guje ni, duniya ta min zafi, shi kadai ne mutumen da ya zo zai share min hawaye a lokacin, bayan mun yi aure ya zama bana burge shi saboda ya saba da matan waje, mijina ba shi da lokacina, baya ganin kyauna, ba ya ganin ado na, kullum idonsa akan matan waje ne, mijina baya iya gamsar da ni yadda kake min Kareem, gaba daya ban yi dacen rayuwa ba, amman a haka nake zaune kullum burina idan har na bar Abdull kai ne”
Wannan karon da cinyar hannu ta goge hawaye idonta na dama.
“Na san na yi kuskure na haihuwar ba ta sunna ba, dukanmu yin yi kuskure amman sai mu rumgumi wannan kaddarar, nan gaba kadan Abdull sakina zai yi, to sai ka aure ni mana Kareem”
Ya juyo da kyau ya fuskance ta.
“Ba zan taba aurenki ba, amman zan tabbatar maki da abu daya, Noor ba zata aure ni ba, saboda bana cikin mazan da take so, please ki cireta a cikin matsalarki”
“I don't care ka auri Noor ko karka aureta ba matsalata ba ce, abun da kawai na damu da shi, shi ne idan Abdull ya sake ni zaka aure ni”
“Har abada ba zan taba aurenki ba, aure ya haramta a tsakaninmu”
Ta rausayar da kai tana murmushi.
“Na fahimci hakan ai, shiyasa na bullowa ubanta ta wannan sigar na fada masa gaskiya kuma na kwadaita masa dukiyar da zai samu idan ya Abdull ko mahaifinsa suka bukaci a sirrinta abun, na samu wata kawata muka je a zuwan ita ce nurse din da ta cire ciki, kuma na samu kudi mai kauri na ba shi. Ka ga yanzu hankalin Abdull zai koma gurin abun da ya aikata ne ba wanda zai aikata a gareni ba, kuma idan ya fallasa sirrina duniya zata zage mu a gaba dayanmu mu uku, kai ni da kuma shi”
Kareem ya sasauta fuskarsa ba dan tsoron furucinta ba sai dan yana son ta fahimcin illar fa hakan zai mata ba mijinta kadai ba. Ya busar da iskar bakinsa ya jin kirjinsa na ciwo sosai.
“Ki rika yin tunani kamin ki aikata abu, kina da yaya Safeena, tun farko baki rike aurenki kika biyewa shaidan muka aikata alfasha, hakan be wadatar da ke ba sai da kika ga mun haihuwa, yanzu gashi abun ya dawo yana bibiyarmu, kuma duk yadda wannan abun zai taba ni be kai yadda ke zai miki illa ba Safeena, saboda ke mace ce ni kuma namiji ne, shiyasa da Allah zai ambacin mazinata a kur'ane sai ya fara da mace, domin ita ce mai rauni kuma ita ce mai shiga kaso 90 na matsala sama da namiji”
“Zaka aure ni Kareem? Ka min alkawari kawai zaka aure ni Wallahi zan yi duk yadda zan iya mahaifinta ya janye shari'ar nan”
Ya cire hannunsa daya a aljihu yana nuna mata.
“Let me make this clear to you, idan har zan sake wani aure a rayuwata, to mace daya ce zan aura Noor, idan har ba zan auri ba ba zan sake aure ba, so ki saka a ranki ni da ke ba mu taba sanin juna ba, ba zan taba aurenki ba Safeena!!”
Wani mugun kallo take masa zuciyarta na bugawa da karfi. Cikin ihu da takiya ta ce
“Ba zan saka ya janye shari'a ba Kareem kuma zan daukar masa lauya, domin ina bukatar abun da zai daga hankalin Noor ya zubar da mutuncinta da na iyayenta ya kashe auren uwarta ya jafata a matsala, ba ni da makiyaya a duniya irin Noor yarinyar da saboda ita igiyar aurena take rawa? Saboda ita juya min baya, yar sikar yarinya shashasha mahaukaciya, yarinya da bata kai ta goge talkamin kafata ba, yarinyar da bata kai ka rika hannunta ba, amman ita kake so? Yarinyar da ubanta baya jin wani yare sai na kudi? Yarinyar da ubanta be san wani mutuncin ba sai na kudi? Yarinyar da babu komai akanta sai hauka da gidadanci, fasika da bata iya komai ba sai bibiyar mazan mutane yarinyar da...”
Tassssss ta ji saukar lafiyayyen mari a fuskarta daga hannun masoyinta Kareem, Wani irin numfashi taja da karfi ta kai hannu ta dafe kuncin hawaye masu zafi na sauko mata. Cikin wani irin bacin rai da Kareem be san yana da shi ba ya nuna ta da yatsa ya ce.
“Kul bakinki ya sake kiran Noor dita da wata kalma marar kyau, iyakar kiyayar da kike mata saboda tana da alaka da ni ne, ni kuma ba aurena zata yi ba, ki fadawa mahaifinta karya kike ya janye shari'ar nan idan ba haka ba...”