Sashe 12
Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Wallahi ban sani ba... Ba.. Ba.. Ban saka.. Magani ba... Ni ban...”
Na kasa magana tsoro da kuka suka ci karfina, ban san me yake fada ba maganin ne condoms ko kuma robar, ko ma duka? To miye illarsu? Miye kawo su a jakata? Taya? Ya hauro saman gadon da talkaminsa ya riko ni da duka karfinsa.
“Ina kika siye Noor? Saboda me kika siya?”
“Ban saya ba, ban san amfaninsa ba, ni ban saka komai a jaka na ba, ban san maganin miye ba, ban san robar ta miye ba, ba nawa ba ne Wallahi”
“To ina aka samu ya aka yi na ganshi a jakarki?”
Na rike hannunsa daya jikina na rawa.
“Wallahi Wallahi ba nawa ba ne, ban san miye ba”
“Da na aje ki gidanku ina kika je?”
“Ban tafi ko'ina ba Wallahi”
“Amman kin yi magana da Zafeer?”
“Ban yi ba, Wallahi ban ga Zafeer ba”
“To wannan abun su suka kawo kansu a jakarki kenan?”
“Wallahi ban san na miye ba, Hafiz sai idan saka min shi aka yi a jaka..”
Fwauuu ya buge min baki.
“Ban ce ki daina fadar sunana ba? Ke gaba daya kanki babu tunani babu tarbiya babu hankali? Gaba daya baki da lissafi? Waya saka miki maganin to? Waye? Ko ki fada min ko na ci ubanki da duka Wallahi”
“daga gida ban je ko'ina ba, kanwata kuma ba zata saka min wannan abun ba, ni da ita duk ba mu taba ganin wannan abun ba”
“To waya saka miki? Ina kika samu? Ni zan dauko na saka miki a jaka?”
“Sai idan Aisha ce ta saka min saboda ta yi min sheri, Wallahi ban san na miye ba”
Ina fadar hakan sai ya sake ni, ya sauka daga kan gadon ya fita daga dakin. A nan an samu damar daukar maganin na duba na sake duba balloon din har biyu sannan na nufo falo na duba jakata da ke kasa sarka da yan kunne da na cire na saka a ciki tun a gida suna watse a kasa. Naira biyar ma ba ni da ita a jakar to a ina zan siye magani? Kuma maganin miye zan siya, wane chemist bayan cikin gidan mu ban san na taka ko'ina ba. Ban gama shiga tashin hankali ba har sai da Aisha ta shigo falon tare da Hafiz.
“Noor ni na saka miki magani da condom a jaka? Ta ina? Da zaki fita na karbi jakarki ne? Kuma ai tare kuka dawo da Barrister idan na saka miki wani abu a ciki zai gani, Kuma na rantse da Allah bayan fitarku ban shigo dakin nan ba, me zai saka ma na yi haka?”
Ta juya gurinsa da sauri ta zube kasa.
“Na shiga uku kar ta kashe min aure, daman burin yan matan yanzu kenan, Wallahi ba ni na saka, idan ni na saka mata shi a jakarta kada Allah ya ba ni abun da nake so Wallahi ba ni ba ce Barrister Innalillahi Na shiga uku...”
Ya rika ta ya mikar da ita tsaye, gaba daya sai suka daure ni na rasa ya zan zarga ita ko kanwata? Ko kuma shi da ya saka min jakar a lefe? Yanzu ta ya zan wanke kaina.
“Tafi bangarenki”
Ta kalleni tana kuka.
“Allah ya saka min gareki, na barki da Allah saboda kar a zarge ki shi ne zaki maida laifin a kaina? Ba ni ba ke Noor daga yau kowa ya tsaya bangarensa....”
Na kasa cewa komai sai kallonta nake hawaye suna sauko min kamar ba gobe. Ta rufe fuska tana kuka sosai ta fice daga falon, kamar fitarta yake jira ya juyo kaina.
“Ta rantse ba ita ta saka miki ba, daman makasudin kiran kenan, fada min ina kika samu wannan? Yanxu kika samu ko kin dade?”
Na yi shiru kamar wadda kalamai suka karewa.
“Ba magana nake miki ba?”
Ya sake daka min tsawa. Still ban iya ce masa komai ba, domin babu wasu kalmomi da zan hada na wanke kaina.
“Shiyasa auren mace mai mutunci mai tarbiya da natsuwa yana da dadi, ka aureki saboda na rufa miki asiri amman kullum matsala kike ba ni, ni ban taba samun matsala da matata irin wannan!”
Yana matsowa ina matsawa baya jira kawai nake ya kai min duka a jiki domin alamar hakannta bayyana a jikinsa da fuskarsa. Kwafa yayi ya nufi ledodin da muka shigo da su ya kwashe gaba daya ya fice daga falon. Ranar kwana ne amman be kwana a dakina ba sai ya kwana a dakin Aisha, ni kuma na kwana a falon cikin kunci da rudani mai tsananin daure kai.
A haka muka kwashe sati biyu be shigo bangare na ba, da girkina da ba nawa ba duk baya zuwa gurina, sai dai na hango shi ta window idan zai fita ko ya dawo. A lokacin damuwa ya fara shiga raina, na tabbatar Zafeer ba zai iya min haka ba, gashi Baba ya aurar da ni ga wanda bana so kuma be iya zama da ni ba. Kukan safe dabam na rana dabam da dare ma idan zan kwanta dabam ga abinci amman bana iya sarrafawa na ci saboda damuwa sai ruwan sha yi babu bread domin ya daina kawo min komai, wani lokacin kuma na dafa taliyar yara kadan na ci.
Idan na zauna da tunani sai na rasa wa zan kaiwa kukana, Baba zan je na fadawa ko kuma Mama ko kuma dai Kareem zan fadawa shi da yake abokinsa? Ko kuma gidan iyayensa zan bincika na fada musu ko kuma na zauna a haka? Na zuba masa ido? Gashi babu wani dan'uwa da ya sake zuwa gurina na balle na bude masa ciki na fada masa damuwata. Amman har zuwa yaushe zai yi ta fushin da Ni? Zuwa yaushe zai sauko? Agogon dakin na duba karfe biyu da mintuna na rana, tashi na yi na dauki green hijab dina na saka na dauki jakar nan da na yi fitar farko da ita na sake dauka na bude marfin madubina na dauko balloon din nan da maganin na saka a jakata na saka talkamina na fito falon na leka windows din waje ban motarsa ba hakan na tabbatar min da baya cikin gidan kenan. Bude kofar falon na yi na fita sannan na janyo kofar ba gabana na faduwa na sauka entrance din na nufi gate. Kamin na fice har wani gumi ke karyo min domin idan ya tare ni a kofar gate din ko hanya ban san me zan fada masa ba. Mai gadin ne ya bude min na fita dama ko hagu sai na rasa ina zan dosa can wata zuciyar ta raya min dama domin ta nan muka bi lokacin da zamu tafi gida tare da shi.
#KhadeejaCandyPAID PAGE 7️⃣
©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024
Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....
You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153
_______•••_______
Na yi tafiya mai nisa kamin na samu Napep na tara ya fada masa inda zai kai ni na shiga. Sai da ya fara tafiya sannan na fara sake saken idan na tafi gida me zan fada? Na nuna musu abun da ya gani a jakar tawa ko kuma dai na fada ma Baba cewar ya daina shigowa bangarena? Gidanmu zan tafi ko kuma na su gidan? Idan ma na ce zan tafi gidansu ina zan bi domin ban taba tafiya ba be kai ni kamin auren ba, bayan aure kuma ba mu samu kwanciyar hankalin da zai kai ni gidan ba. Wata zuciyar kuma na raya min na tafi gurin Mama kai tsaye sai dai kuma ita ma zan iya shafa mata laifi. Ya mace bata da gidan da ya fi na mahaifinta saboda haka na fada masa unguwarmu kai tsaye.
Har kofar gidanmu ya faka Napep din na fita na shiga gidan da sallama. Yaya na fara cin karo da shi yana wanki sai kuma Hana dake gaban murhu tana girki har yanzu da sauran kuna a jikinta domin na same ta babu riga a jiki.
“Yaya dan Allah dari biyar zaka ba ni zan sallami mai napep”
“Lafiya?”
Ya tambaya yana kallon yanayi na, domin na shigo gidan ne cike da damuwar da ta kasa boyuwa a fuskata. Na yo shiru be sake ce min komai ba ya tashi ya shiga dakinsa ya dauko dari biyu da naira dari ya miko min.
“Su kenan suka rage min, nawa ya kawo ki?”
“Ban yi ciniki da shi ba, bari na tambaya”
Na juya na fita, ta inda na yi sa'a ina tambayar mai Napep din nawa ya ce min dari uku sai na mika masa na dawo cikin gidan na nufi kofar dakin Mama na zauna.
“Noor kin rame? Ko baki da lafiya?”
Hana ta fada satar kallon Yaya na yi dake kallona sannan na ce.
“Har yanzu konan be warke ba?”
“Eh da saura, kin san wuta bata warkewa da wuri, kowa ma cewa yake na yi sa'a jikina yana da kyau ne”
“Ina Baba?”
“Dazun ya kawo cefa ne ya fita, anjima na san zai dawo cin abinci ai tun da yace ya gama da wuri”
Na sake kallon Yaya sannan na kalli rufin kwanon da aka yi da tsohon kwano a dakunan da suke kone, shi ma kuma daga dakinmu sai na Mama da take ciki na Yaya har lokacin a bude yake.
“Ashe an rufe”
“Eh Ya Nabil ne suka rufe shi da abokinsa, tsofin kwanon da suka kone ne suka rufe da su”
Na kasa magana tsoro da kuka suka ci karfina, ban san me yake fada ba maganin ne condoms ko kuma robar, ko ma duka? To miye illarsu? Miye kawo su a jakata? Taya? Ya hauro saman gadon da talkaminsa ya riko ni da duka karfinsa.
“Ina kika siye Noor? Saboda me kika siya?”
“Ban saya ba, ban san amfaninsa ba, ni ban saka komai a jaka na ba, ban san maganin miye ba, ban san robar ta miye ba, ba nawa ba ne Wallahi”
“To ina aka samu ya aka yi na ganshi a jakarki?”
Na rike hannunsa daya jikina na rawa.
“Wallahi Wallahi ba nawa ba ne, ban san miye ba”
“Da na aje ki gidanku ina kika je?”
“Ban tafi ko'ina ba Wallahi”
“Amman kin yi magana da Zafeer?”
“Ban yi ba, Wallahi ban ga Zafeer ba”
“To wannan abun su suka kawo kansu a jakarki kenan?”
“Wallahi ban san na miye ba, Hafiz sai idan saka min shi aka yi a jaka..”
Fwauuu ya buge min baki.
“Ban ce ki daina fadar sunana ba? Ke gaba daya kanki babu tunani babu tarbiya babu hankali? Gaba daya baki da lissafi? Waya saka miki maganin to? Waye? Ko ki fada min ko na ci ubanki da duka Wallahi”
“daga gida ban je ko'ina ba, kanwata kuma ba zata saka min wannan abun ba, ni da ita duk ba mu taba ganin wannan abun ba”
“To waya saka miki? Ina kika samu? Ni zan dauko na saka miki a jaka?”
“Sai idan Aisha ce ta saka min saboda ta yi min sheri, Wallahi ban san na miye ba”
Ina fadar hakan sai ya sake ni, ya sauka daga kan gadon ya fita daga dakin. A nan an samu damar daukar maganin na duba na sake duba balloon din har biyu sannan na nufo falo na duba jakata da ke kasa sarka da yan kunne da na cire na saka a ciki tun a gida suna watse a kasa. Naira biyar ma ba ni da ita a jakar to a ina zan siye magani? Kuma maganin miye zan siya, wane chemist bayan cikin gidan mu ban san na taka ko'ina ba. Ban gama shiga tashin hankali ba har sai da Aisha ta shigo falon tare da Hafiz.
“Noor ni na saka miki magani da condom a jaka? Ta ina? Da zaki fita na karbi jakarki ne? Kuma ai tare kuka dawo da Barrister idan na saka miki wani abu a ciki zai gani, Kuma na rantse da Allah bayan fitarku ban shigo dakin nan ba, me zai saka ma na yi haka?”
Ta juya gurinsa da sauri ta zube kasa.
“Na shiga uku kar ta kashe min aure, daman burin yan matan yanzu kenan, Wallahi ba ni na saka, idan ni na saka mata shi a jakarta kada Allah ya ba ni abun da nake so Wallahi ba ni ba ce Barrister Innalillahi Na shiga uku...”
Ya rika ta ya mikar da ita tsaye, gaba daya sai suka daure ni na rasa ya zan zarga ita ko kanwata? Ko kuma shi da ya saka min jakar a lefe? Yanzu ta ya zan wanke kaina.
“Tafi bangarenki”
Ta kalleni tana kuka.
“Allah ya saka min gareki, na barki da Allah saboda kar a zarge ki shi ne zaki maida laifin a kaina? Ba ni ba ke Noor daga yau kowa ya tsaya bangarensa....”
Na kasa cewa komai sai kallonta nake hawaye suna sauko min kamar ba gobe. Ta rufe fuska tana kuka sosai ta fice daga falon, kamar fitarta yake jira ya juyo kaina.
“Ta rantse ba ita ta saka miki ba, daman makasudin kiran kenan, fada min ina kika samu wannan? Yanxu kika samu ko kin dade?”
Na yi shiru kamar wadda kalamai suka karewa.
“Ba magana nake miki ba?”
Ya sake daka min tsawa. Still ban iya ce masa komai ba, domin babu wasu kalmomi da zan hada na wanke kaina.
“Shiyasa auren mace mai mutunci mai tarbiya da natsuwa yana da dadi, ka aureki saboda na rufa miki asiri amman kullum matsala kike ba ni, ni ban taba samun matsala da matata irin wannan!”
Yana matsowa ina matsawa baya jira kawai nake ya kai min duka a jiki domin alamar hakannta bayyana a jikinsa da fuskarsa. Kwafa yayi ya nufi ledodin da muka shigo da su ya kwashe gaba daya ya fice daga falon. Ranar kwana ne amman be kwana a dakina ba sai ya kwana a dakin Aisha, ni kuma na kwana a falon cikin kunci da rudani mai tsananin daure kai.
A haka muka kwashe sati biyu be shigo bangare na ba, da girkina da ba nawa ba duk baya zuwa gurina, sai dai na hango shi ta window idan zai fita ko ya dawo. A lokacin damuwa ya fara shiga raina, na tabbatar Zafeer ba zai iya min haka ba, gashi Baba ya aurar da ni ga wanda bana so kuma be iya zama da ni ba. Kukan safe dabam na rana dabam da dare ma idan zan kwanta dabam ga abinci amman bana iya sarrafawa na ci saboda damuwa sai ruwan sha yi babu bread domin ya daina kawo min komai, wani lokacin kuma na dafa taliyar yara kadan na ci.
Idan na zauna da tunani sai na rasa wa zan kaiwa kukana, Baba zan je na fadawa ko kuma Mama ko kuma dai Kareem zan fadawa shi da yake abokinsa? Ko kuma gidan iyayensa zan bincika na fada musu ko kuma na zauna a haka? Na zuba masa ido? Gashi babu wani dan'uwa da ya sake zuwa gurina na balle na bude masa ciki na fada masa damuwata. Amman har zuwa yaushe zai yi ta fushin da Ni? Zuwa yaushe zai sauko? Agogon dakin na duba karfe biyu da mintuna na rana, tashi na yi na dauki green hijab dina na saka na dauki jakar nan da na yi fitar farko da ita na sake dauka na bude marfin madubina na dauko balloon din nan da maganin na saka a jakata na saka talkamina na fito falon na leka windows din waje ban motarsa ba hakan na tabbatar min da baya cikin gidan kenan. Bude kofar falon na yi na fita sannan na janyo kofar ba gabana na faduwa na sauka entrance din na nufi gate. Kamin na fice har wani gumi ke karyo min domin idan ya tare ni a kofar gate din ko hanya ban san me zan fada masa ba. Mai gadin ne ya bude min na fita dama ko hagu sai na rasa ina zan dosa can wata zuciyar ta raya min dama domin ta nan muka bi lokacin da zamu tafi gida tare da shi.
#KhadeejaCandyPAID PAGE 7️⃣
©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024
Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....
You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153
_______•••_______
Na yi tafiya mai nisa kamin na samu Napep na tara ya fada masa inda zai kai ni na shiga. Sai da ya fara tafiya sannan na fara sake saken idan na tafi gida me zan fada? Na nuna musu abun da ya gani a jakar tawa ko kuma dai na fada ma Baba cewar ya daina shigowa bangarena? Gidanmu zan tafi ko kuma na su gidan? Idan ma na ce zan tafi gidansu ina zan bi domin ban taba tafiya ba be kai ni kamin auren ba, bayan aure kuma ba mu samu kwanciyar hankalin da zai kai ni gidan ba. Wata zuciyar kuma na raya min na tafi gurin Mama kai tsaye sai dai kuma ita ma zan iya shafa mata laifi. Ya mace bata da gidan da ya fi na mahaifinta saboda haka na fada masa unguwarmu kai tsaye.
Har kofar gidanmu ya faka Napep din na fita na shiga gidan da sallama. Yaya na fara cin karo da shi yana wanki sai kuma Hana dake gaban murhu tana girki har yanzu da sauran kuna a jikinta domin na same ta babu riga a jiki.
“Yaya dan Allah dari biyar zaka ba ni zan sallami mai napep”
“Lafiya?”
Ya tambaya yana kallon yanayi na, domin na shigo gidan ne cike da damuwar da ta kasa boyuwa a fuskata. Na yo shiru be sake ce min komai ba ya tashi ya shiga dakinsa ya dauko dari biyu da naira dari ya miko min.
“Su kenan suka rage min, nawa ya kawo ki?”
“Ban yi ciniki da shi ba, bari na tambaya”
Na juya na fita, ta inda na yi sa'a ina tambayar mai Napep din nawa ya ce min dari uku sai na mika masa na dawo cikin gidan na nufi kofar dakin Mama na zauna.
“Noor kin rame? Ko baki da lafiya?”
Hana ta fada satar kallon Yaya na yi dake kallona sannan na ce.
“Har yanzu konan be warke ba?”
“Eh da saura, kin san wuta bata warkewa da wuri, kowa ma cewa yake na yi sa'a jikina yana da kyau ne”
“Ina Baba?”
“Dazun ya kawo cefa ne ya fita, anjima na san zai dawo cin abinci ai tun da yace ya gama da wuri”
Na sake kallon Yaya sannan na kalli rufin kwanon da aka yi da tsohon kwano a dakunan da suke kone, shi ma kuma daga dakinmu sai na Mama da take ciki na Yaya har lokacin a bude yake.
“Ashe an rufe”
“Eh Ya Nabil ne suka rufe shi da abokinsa, tsofin kwanon da suka kone ne suka rufe da su”