Sashe 41
Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya daga min kai.
“Yes Noor na lura kina cikin damuwa a lokacin kuma kin fada min kina son komawa ai, babu wani abun da zaki roka ban miki shi ba Noor sai idan ba zan iya ba”
“Na dauka ina takura maka ne, na ga har baka son zuwana gurinka, na san ni ina da takura ai”
Yayi murmushi.
“To ki yi hakuri, idan Baba yana ciki shiga ki masa magana”
“Baya nan yana majalisa”
“Shiga ciki zan je can na same shi, ki kwantar da hankalinki Allah zai baki abun da ba su ba ki ba, kayan dakin ma sun ce ba za su baki ba ai saboda shi yayi komai”
“Ni fa ba abun da ya dame ni da wani gado, su je su yi ta riko, amman ka yi magana da Baba shi ne dai na ji yana zancen zai yi kara idan ba a bada ba”
“Okay”
Kallona yake har na shige cikin gidan, ina shigowa Ya Nabil ya fita waje.Duk wata maganar da zai yi da Baba na san ba zai saurare shi, amman kudi za su iya sakawa ya fahimci komai kuma ya sassauto. Da alaka kuma Kareem yayi amfani da su ne domin babu ya shigo da far'a har da tsarabar nama yayi ma Umma. Cewa yake a yanzu ya hakura zai kyalesu amman saboda Kareem be kawai ba dan haka ba da babu abun da zai hana shi jan min hakkina. Yanka biyu aka ba mu, sai da muka cinye sannan yayi mana albishir wai Kareem ya fada masa ya nemawa Ya Nabil karanta a Sudan. Farinciki ya cika ni a lokacin da Baba yake fada min Kareem yana neman izininsa idan ya aminta sai ya fadawa Ya Nabil din ya kai masa takardunsa na SSCE.
Sanin da na yi ba karamin dadi Ya Nabil zai ji ba, ya saka ni farincikin da na kwana biyu ban yi ba. Hakan kuma ya karantar da ni cewar Kareem yana da kirki ta wani bangaren, domin gashi ya danne kudirin mahaifina kuma yana kokarin nemawa dan'uwana karatu alhalin be hada komai da mu ba. Farinciki a gurin Yaya Nabil ba a magana kamar zai zuba ruwa kasa ya sha domin murna, daman abun da yake nema ne yana son karatu shi da Hana ba kamar ni ba.
Washe gari da safe Kanen Hafiz ya sake kawo min ziyara sai dai wannan karon ba, maganar gado ce ta kawo shi ba, ya zo min ne da tsaraba ta atamfa biyu da kuma turare sai sabulu da talkami da kudi 10k wai yana taya ni murna fita waka, kuma na yi hakuri da yadda yan'uwansa suka nuna min halin ko'ina kula. Na karba na yi masa godiya muka yi sallama na shiga ciki, bana tunanin ina da wata bukata ta kudi a yanzu wannan ya saka na dauki kudin na bawa Hana na ce ta kaiwa Mama idan ta tafi gidan, domin ita ce mai yawan zuwa ni ban taba zuwa ba domin an yi auren ne a lokacin da ba ni da halin yawo.
Abu kamar wasa, shiryen shiryen tafiyar Yaya Nabil Sudan ya fara, duk wani abu da za'ayi Kareem ne yake ba shi kudi yayi, har aka kammala komai within three months. Ranar da zai je yi ma Mama bankwana na bi shi muka tafi tare, ni da shi sai a ranar muka fara zuwa gidan.
Babba gida ne mai bangare kusan hudu, gida ne mai kyau da tsari Mama da kanta na san ba ta taba mafarkin aure irin wannan gidan ba.
Da muka shiga ciki sai ta zame mana kamar wata bakuwarmu saboda yadda rayuwa ta canja mata, ta yi kiba ta kara haske ga tufafi masu tsada kayan kallo kai har da dinning da ac kamar daman can Mama bata taba auren talaka ba, duk inda ta wulga kallonta nake kamar wata bakauya.
“Noor na zame miki sabuwa yanzu ko?”
Na yi dariya ina kallon plate din taliyar da ta aje min nama batsa batsa kamar wanke.
“Mama ina ta mamaki ne, ina kika hadu da wannan mutumen ne?”
Ta dan hade rai.
“Mutume? Toh idan ba zaki iya kiransa da Baba ba, ki kirashi da suna Alhaji kamar yadda kowa yake kiransa a gidan nan, wato ke dai sakarcin ki ba zai canja ba ko?”
Na yi shiru ina kallon Yaya dake cin taliyar, sannan na soma cin tawa. Rabin abincin kawai Yaya ya ci ya sha ruwa yace zai tafi.
“Da wuri Nabil na yi zaton sai dare, saboda Alhaji ya dawo ku gaisa, yana ta fadar ban taba gabatar masa da sauran yarana ba, be san kowa a cikinku ba sai Hana da ke yawana zuwa”
“Bana son na kai dare Mama, akwai guraren da ya kamata na tafi kamin ba bar garin nan, kuma kin ga kwana biyu ya rage min”
“To sai dai kai ka tafi Noor kuma zata tsaya sai ya dawo kun gaisa tukuna ta wuce”
Mama ta shiga dakinta ta dauko masa babbar leda cike da kaya sannan ta danka masa 20k tana ta sakawa Kareem albarka wai daman a yanzu tana ta tunanin wace makaranta zata nemawa tarin kudin da take shi take yi ma, amman gashi ya dauke mata nauyi. Bayan Ya Nabil ya wuce muka zauna da Mama muna hira take tambaya ko Zafeer ya ji rayuwar Mijina.
“Zai iya ji tun da iyayensa suna cikin unguwar, ko basa nan ma ai yan gulma suna nan, fitowar nan ma cewa suke ta yi hakkinsa ne”
“Zafeer yana sonki sosai, zai iya dawowa yanzu ma, wata kila kuma iyayensa su hana shi, ko da yake a can baya ma sun yi ta kokarin hana amman ya nace sai ke, gashi kuma an watsa masa a ido, Wallahi mahaifinku be kyauta ba”
“Baba ma da yace be yafe ba idan na sake masa magana, shi ne abun da ya fi damuna”
“Wai har yanzu? Toh ai Hafiz din baya raye kuma, yanzu idan Zafeer ya dawo ba zai bari ya aureki ba?”
“Ban sani ba, amman da kamar wahala saboda yana ganin Zafeer talaka ne”
“Haka ne, ubanki be ji wani yare sai na kudi, gashi babu mai iya ja masa liyi a dangi komai yayi daidai ne a idonsu”
Na daga kai ina kallon POP din falon.
“Taso mu tafi ki gaisa da mutanen gidan, suna ta tambayar, da kika fita wanka ma sai da matarsa tace zata tafi ta duba ki kuma Allah be yi ba”
“Ita bata kishi ne Mama?”
“Ana tabawa mana ayi mace babu kishi, amman boyewa ake na ciki na ciki, ita dai tana da kirki ba kamar wasu ba”
“Ko dai irin na Aisha take miki ba, haka take nuna min ba komai ashe wayo take min”
“Ke dai da halinki Noor, na san ki ba, kuma zamanmu a nan Alhaji ya fada mace kamar riga take a wuyansa duk wanda ta daga masa hankali cire ta kawai zai yi ya aje, duk tarin yaransa babu wanda uwarsu take cikin gidan nan, sai wannan matar da yaranta uku, sauran duk iyayensu sun fita, ni ma sai bayan auren nake ji, wata kila shiyasa ta kama kanta”
Ina jin haka na san an gudu ba a tsira ba ne, kenan ita ma idan ta yi masa ba daidai ba zai iya sakinta. Daga bangaren Mama muka fito muka shiga bangaren matar da take gidan a yanzu. A cike muka samu falon da mata da maza, Mama ta yi sallama suka amsa suna gaisheta da mutunci.
“Noor Ya hakuri?”
Wata budurwar da ban waye ta ba ta fada sai na amsa da Alhamdullahi na gaishe da Hajiyar.
“Lafiya Kalau Noor, an fita wanka ko? Tohm Allah ya bada hakuri ya kawo na gari”
Mama ta amsa da Ameen.
“Alhaji ne be santa ba sai mita yake ina boye masa yara, tare da yayanta take jibi zai wuce Sudan gurin karatu, ya zo bankwana amman be tsaya ba, ita kuma ba ce ya tsaya ta gaisa da yan gida”
“Ta kyauta gaskiya, da ma dai kin maido nan kila zata fi jin sanyi kin san gidan na mu cike yake da mutane”
“Mahaifinta ne ai be yarda ba, ko takaba a nan ya so ta yi amman uban yace ba zata yi ba”
“Kin san wasu mazan akwai kishi”
Haka dai suke ta hirarsu ni dai kaina na kasa ban dago har sai da na ji an bude kofar falo alamar mutum ya shigo. Dagowar da na yi sai muka yi ido hudu da Safeena tana dauke da cikinta da be gama girma ba. Bata kallon kowa sai ni ni ma kuma bana kallon kowa sai ita muka rika kallon kallo wata kila ita ma tana mamakin ganina ne kamar yadda nake mamakin ganinta. Gidansu ne? Ko kuma zuwa ta yi? Ko kuma dai tana da wata alaka ce da mutanen gidan?
“Kin dawo Safeena?”
Hajiyar ta fada sai Safeena ta amsa mata ba tare da ta kalleni ba, har lokacin ni take kallo.
“Na dawo Hajiya, na karbo files din gobe zan tafi asibitin na kai”
“Toh Allah ya taimaka ya raba lafiya”
“Ameen”
Ta amsa sannan ta dauke idonta ta zauna a kujerar dake facing dina, sai kuma ta sake dasawa daga inda ta tsaya.
“Anty Safeena kin santa ne?”
Na kalli mai tambayar wata kila su ma sun lura da kallon da take min yayi yawa. Ga mamakina sai ta amsa da cewar
“Aa ban san ta ba, wacece hala? Ta yi min kama da wata kawata ce ta yarinya”
“Noor ce yar wajen Anty Amarya, wanda mijinta ya rasu”
“Allah sarki Allah ya masa rahama”
Ya juya tana kallon Mama dake amsawa da Ameen sannan ta sake kallona. Har muka baro bangaren babu abun da take sai kallona kamar wata bakuwarta. Ban kuma san dalilinta na boye cewar ta san ni ba. A bangaren Mama na koma na zauna har dare ina jiran dawowar mijinta saboda mu gaisa, be shigo ba sai bayan Magariba a lokacin da ake hada hadar Sallah Isha'i.
“Yes Noor na lura kina cikin damuwa a lokacin kuma kin fada min kina son komawa ai, babu wani abun da zaki roka ban miki shi ba Noor sai idan ba zan iya ba”
“Na dauka ina takura maka ne, na ga har baka son zuwana gurinka, na san ni ina da takura ai”
Yayi murmushi.
“To ki yi hakuri, idan Baba yana ciki shiga ki masa magana”
“Baya nan yana majalisa”
“Shiga ciki zan je can na same shi, ki kwantar da hankalinki Allah zai baki abun da ba su ba ki ba, kayan dakin ma sun ce ba za su baki ba ai saboda shi yayi komai”
“Ni fa ba abun da ya dame ni da wani gado, su je su yi ta riko, amman ka yi magana da Baba shi ne dai na ji yana zancen zai yi kara idan ba a bada ba”
“Okay”
Kallona yake har na shige cikin gidan, ina shigowa Ya Nabil ya fita waje.Duk wata maganar da zai yi da Baba na san ba zai saurare shi, amman kudi za su iya sakawa ya fahimci komai kuma ya sassauto. Da alaka kuma Kareem yayi amfani da su ne domin babu ya shigo da far'a har da tsarabar nama yayi ma Umma. Cewa yake a yanzu ya hakura zai kyalesu amman saboda Kareem be kawai ba dan haka ba da babu abun da zai hana shi jan min hakkina. Yanka biyu aka ba mu, sai da muka cinye sannan yayi mana albishir wai Kareem ya fada masa ya nemawa Ya Nabil karanta a Sudan. Farinciki ya cika ni a lokacin da Baba yake fada min Kareem yana neman izininsa idan ya aminta sai ya fadawa Ya Nabil din ya kai masa takardunsa na SSCE.
Sanin da na yi ba karamin dadi Ya Nabil zai ji ba, ya saka ni farincikin da na kwana biyu ban yi ba. Hakan kuma ya karantar da ni cewar Kareem yana da kirki ta wani bangaren, domin gashi ya danne kudirin mahaifina kuma yana kokarin nemawa dan'uwana karatu alhalin be hada komai da mu ba. Farinciki a gurin Yaya Nabil ba a magana kamar zai zuba ruwa kasa ya sha domin murna, daman abun da yake nema ne yana son karatu shi da Hana ba kamar ni ba.
Washe gari da safe Kanen Hafiz ya sake kawo min ziyara sai dai wannan karon ba, maganar gado ce ta kawo shi ba, ya zo min ne da tsaraba ta atamfa biyu da kuma turare sai sabulu da talkami da kudi 10k wai yana taya ni murna fita waka, kuma na yi hakuri da yadda yan'uwansa suka nuna min halin ko'ina kula. Na karba na yi masa godiya muka yi sallama na shiga ciki, bana tunanin ina da wata bukata ta kudi a yanzu wannan ya saka na dauki kudin na bawa Hana na ce ta kaiwa Mama idan ta tafi gidan, domin ita ce mai yawan zuwa ni ban taba zuwa ba domin an yi auren ne a lokacin da ba ni da halin yawo.
Abu kamar wasa, shiryen shiryen tafiyar Yaya Nabil Sudan ya fara, duk wani abu da za'ayi Kareem ne yake ba shi kudi yayi, har aka kammala komai within three months. Ranar da zai je yi ma Mama bankwana na bi shi muka tafi tare, ni da shi sai a ranar muka fara zuwa gidan.
Babba gida ne mai bangare kusan hudu, gida ne mai kyau da tsari Mama da kanta na san ba ta taba mafarkin aure irin wannan gidan ba.
Da muka shiga ciki sai ta zame mana kamar wata bakuwarmu saboda yadda rayuwa ta canja mata, ta yi kiba ta kara haske ga tufafi masu tsada kayan kallo kai har da dinning da ac kamar daman can Mama bata taba auren talaka ba, duk inda ta wulga kallonta nake kamar wata bakauya.
“Noor na zame miki sabuwa yanzu ko?”
Na yi dariya ina kallon plate din taliyar da ta aje min nama batsa batsa kamar wanke.
“Mama ina ta mamaki ne, ina kika hadu da wannan mutumen ne?”
Ta dan hade rai.
“Mutume? Toh idan ba zaki iya kiransa da Baba ba, ki kirashi da suna Alhaji kamar yadda kowa yake kiransa a gidan nan, wato ke dai sakarcin ki ba zai canja ba ko?”
Na yi shiru ina kallon Yaya dake cin taliyar, sannan na soma cin tawa. Rabin abincin kawai Yaya ya ci ya sha ruwa yace zai tafi.
“Da wuri Nabil na yi zaton sai dare, saboda Alhaji ya dawo ku gaisa, yana ta fadar ban taba gabatar masa da sauran yarana ba, be san kowa a cikinku ba sai Hana da ke yawana zuwa”
“Bana son na kai dare Mama, akwai guraren da ya kamata na tafi kamin ba bar garin nan, kuma kin ga kwana biyu ya rage min”
“To sai dai kai ka tafi Noor kuma zata tsaya sai ya dawo kun gaisa tukuna ta wuce”
Mama ta shiga dakinta ta dauko masa babbar leda cike da kaya sannan ta danka masa 20k tana ta sakawa Kareem albarka wai daman a yanzu tana ta tunanin wace makaranta zata nemawa tarin kudin da take shi take yi ma, amman gashi ya dauke mata nauyi. Bayan Ya Nabil ya wuce muka zauna da Mama muna hira take tambaya ko Zafeer ya ji rayuwar Mijina.
“Zai iya ji tun da iyayensa suna cikin unguwar, ko basa nan ma ai yan gulma suna nan, fitowar nan ma cewa suke ta yi hakkinsa ne”
“Zafeer yana sonki sosai, zai iya dawowa yanzu ma, wata kila kuma iyayensa su hana shi, ko da yake a can baya ma sun yi ta kokarin hana amman ya nace sai ke, gashi kuma an watsa masa a ido, Wallahi mahaifinku be kyauta ba”
“Baba ma da yace be yafe ba idan na sake masa magana, shi ne abun da ya fi damuna”
“Wai har yanzu? Toh ai Hafiz din baya raye kuma, yanzu idan Zafeer ya dawo ba zai bari ya aureki ba?”
“Ban sani ba, amman da kamar wahala saboda yana ganin Zafeer talaka ne”
“Haka ne, ubanki be ji wani yare sai na kudi, gashi babu mai iya ja masa liyi a dangi komai yayi daidai ne a idonsu”
Na daga kai ina kallon POP din falon.
“Taso mu tafi ki gaisa da mutanen gidan, suna ta tambayar, da kika fita wanka ma sai da matarsa tace zata tafi ta duba ki kuma Allah be yi ba”
“Ita bata kishi ne Mama?”
“Ana tabawa mana ayi mace babu kishi, amman boyewa ake na ciki na ciki, ita dai tana da kirki ba kamar wasu ba”
“Ko dai irin na Aisha take miki ba, haka take nuna min ba komai ashe wayo take min”
“Ke dai da halinki Noor, na san ki ba, kuma zamanmu a nan Alhaji ya fada mace kamar riga take a wuyansa duk wanda ta daga masa hankali cire ta kawai zai yi ya aje, duk tarin yaransa babu wanda uwarsu take cikin gidan nan, sai wannan matar da yaranta uku, sauran duk iyayensu sun fita, ni ma sai bayan auren nake ji, wata kila shiyasa ta kama kanta”
Ina jin haka na san an gudu ba a tsira ba ne, kenan ita ma idan ta yi masa ba daidai ba zai iya sakinta. Daga bangaren Mama muka fito muka shiga bangaren matar da take gidan a yanzu. A cike muka samu falon da mata da maza, Mama ta yi sallama suka amsa suna gaisheta da mutunci.
“Noor Ya hakuri?”
Wata budurwar da ban waye ta ba ta fada sai na amsa da Alhamdullahi na gaishe da Hajiyar.
“Lafiya Kalau Noor, an fita wanka ko? Tohm Allah ya bada hakuri ya kawo na gari”
Mama ta amsa da Ameen.
“Alhaji ne be santa ba sai mita yake ina boye masa yara, tare da yayanta take jibi zai wuce Sudan gurin karatu, ya zo bankwana amman be tsaya ba, ita kuma ba ce ya tsaya ta gaisa da yan gida”
“Ta kyauta gaskiya, da ma dai kin maido nan kila zata fi jin sanyi kin san gidan na mu cike yake da mutane”
“Mahaifinta ne ai be yarda ba, ko takaba a nan ya so ta yi amman uban yace ba zata yi ba”
“Kin san wasu mazan akwai kishi”
Haka dai suke ta hirarsu ni dai kaina na kasa ban dago har sai da na ji an bude kofar falo alamar mutum ya shigo. Dagowar da na yi sai muka yi ido hudu da Safeena tana dauke da cikinta da be gama girma ba. Bata kallon kowa sai ni ni ma kuma bana kallon kowa sai ita muka rika kallon kallo wata kila ita ma tana mamakin ganina ne kamar yadda nake mamakin ganinta. Gidansu ne? Ko kuma zuwa ta yi? Ko kuma dai tana da wata alaka ce da mutanen gidan?
“Kin dawo Safeena?”
Hajiyar ta fada sai Safeena ta amsa mata ba tare da ta kalleni ba, har lokacin ni take kallo.
“Na dawo Hajiya, na karbo files din gobe zan tafi asibitin na kai”
“Toh Allah ya taimaka ya raba lafiya”
“Ameen”
Ta amsa sannan ta dauke idonta ta zauna a kujerar dake facing dina, sai kuma ta sake dasawa daga inda ta tsaya.
“Anty Safeena kin santa ne?”
Na kalli mai tambayar wata kila su ma sun lura da kallon da take min yayi yawa. Ga mamakina sai ta amsa da cewar
“Aa ban san ta ba, wacece hala? Ta yi min kama da wata kawata ce ta yarinya”
“Noor ce yar wajen Anty Amarya, wanda mijinta ya rasu”
“Allah sarki Allah ya masa rahama”
Ya juya tana kallon Mama dake amsawa da Ameen sannan ta sake kallona. Har muka baro bangaren babu abun da take sai kallona kamar wata bakuwarta. Ban kuma san dalilinta na boye cewar ta san ni ba. A bangaren Mama na koma na zauna har dare ina jiran dawowar mijinta saboda mu gaisa, be shigo ba sai bayan Magariba a lokacin da ake hada hadar Sallah Isha'i.