← Book details Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 82

Sashe 16

Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Zan gyara, amman kamar yadda baka yarda Noor bata san komai akan samun maganin a jakarta ba ni ma ban yarda Aisha ta saka mata ba, na san wacece Aisha shekara nawa muna tare da ita, mace ce mai kirki mai mutunci”

Kareem be sake cewa komai ba, domin baya son ya zafafa kasancewar ba shi da hujja kuma baya son Hafiz ya dauki abun ta wata sigar. Sai dai abun da be sani ba Hafiz ya gama fahimtar har yanzu akwai Soyayyar Noor a zuciyarsa hakan kuma ya saka shi jin kamar aurenta ba shi da amfani a gareshi. Sai bayan Sallah Magariba suka rabu da juna Hafiz ya nufi gidan Kareem kuma ya fito ya zauna a harabar kamar yadda ya saba domin baya shiga gida sai bayan Isha'i lokacin da yake tare da Safeena gidansa da suke badala yake tafiya sai kusan 11 ko 10pm suke rabuwa...
A hanya yayi sallah Isha'i sannan ya shiga gidansa, yana faka mota yaransa suka fito da gudu suka tarbe shi sai ya daga su sama yana ajewa yana dariya.

“Baku yi bachi ba”

“Eh Daddy me ka siyo mana”

“Ban siyo komai ba amman dai akwai chocolate a daki muje na baku”

Ya kama hannunsu suka shiga ciki babbar ta rufe kofar falon, Yusura ta mike tsaye daga zaune da take.

“Sannu da zuwa”

“Yauwa Sannu”

Yana rike da hannun yaransa ya haura sama suka shiga dakin, gaban maduni ya tsaya ya fara cire agogonsa akan Areef ya hau gado yayi tsalle ya haye masa baya yana dariya, shi ko yana juyowa ya fara masa chakulkuli sai dariya suke har shi gogan. Gurin da yake aje kayan dadin ya bude ya dauko ya mika musu. Yusura ce ta shigo dakin hannayenta a baya tana kallonsu.

“Tine ku je falo zan yi magana da Daddy”

Ya juyo ya kalleta, su suka sauka daga kan gadon suka fice daga dakin. Karasa ta yi kusa da shi ta dora masa abun da ta samu a aljihunsa kan gado. Ya kalli maganin da sabuwar robar ya kalleta irin kallon nan na me aka yi? Ita ma ta yi masa irin kallon ya aka yi suka zo aljihunka. Ya dan tabe baki

“Ba nawa ba ne”

“Su suka kawo kansu?”

“Ni ban taba amfani da condom ba a rayuwata, da maganin da cdm din ba nawa ba ne, dalili ya kawo su”

“Dalilin nake son ji”

“Miye matsalarki da shiga hurumi har kina bincikar kayana? Ki tsaya matsayinki kar ki sake yi min haka”

“Okay so kake na zuba maka ido ka lalace? Matan auren har gida suke zuwa nemanka? Ka ba su fuska na nuna musu ba ni da muhimmanci a gurinka?”

“Babu wata alaka tsakanina da su, can you excuse me please...”

“No idan wani abu ya faru yanzu ai ni za a zaga saboda Momy bata raye ni za a dorawa laifi”

Da mamaki yake kallonta wato gata uwarsa.

“Me ya same ki ne? Why are you behaving like this? Ba ma shiga hurumin juna, me ya canja yanzu”

“Babu abun da ya canja, kawai duk abun da nake ina yi ne saboda yarana, kuma ba zan sake daukar wata karuwa ta shigo cikin gidan nan nemanka, ka tsaya can waje ka yi tun da ka lalata rayuwarka, ka dauki hakkina ga hakkin yara ga hakkin Momy ga hakkin Daddy ga hakkin Allah ga hakkin matan da kake lalatawa ga hakkin mazansu da yayansu kana zuwa lahira wuta a a saka ka kai tsaye...”

Shi dai kallonta kawai yake har ta gama balbalin bala'in ta fice daga dakin. Because he's not a fan of argue. Juyawa yayi yana kallon kofar be taba aikata wani abu da ya shafi rayuwarsa ya ga Yusura ta fusata haka ba irin wannan, kuma ta nuna a fili sai wannan karon, and the most funniest part is yadda ta jero masa hakkin kowa a kai kamar ita zata kai shi wutar. Kai ya girgiza sannan ya shiga bandaki yayi wanka ya fito ya shirya cikin Pajamas.

NOOR POV.

Yadda nake kwana sati biyu da suka wuce haka na kwana a yau ma. Wato kwanan bakinciki da damuwa da kuka da kuma kadaici. Da safe na fito na gyara falon da be yi dattin komai ba na shiga kitchen na hada tea na fito falon na zauna ina sha. Muryar Aisha na ji tana yi ma Hafiz Allah ya tsare. Hakan ya saka ni mikewa tsaye na isa gurin windows din na bude sai na hango shi zai shiga mota ita kuma tana tsaye da murmushi a fuskarta sai hannu take daga masa. Har ga Allah bana son Hafiz kuma bana jin zan iya son sa ba shi kadai ba har zuciyata ba zata taba kaunar wani namijin ba bayan Zafeer amman tabbas ina jin zafi sosai yadda ya aje ni a karkashinsa amman ya kasa yi min inuwa kuma yana min ba ni muhimmanci a gurinsa.

Ina kallonsa ya tuka mota ya fice daga gidan ba tare da ya shigo bangarena ba, na yi tunanin zai shigo ko da fada ne yayi min ya tambayi ina na tafi ba tare da izininsa ba.
Kuka na yi har sai da numfashina ya fara sakerwa na kasa cin komai a wunin sai kuka. Sallah ma daker na yi saboda jikin babu karfi, I'm so hopeless babu mai taimakona, ko da zan mutu a wannan halin na kunci da nake ciki babu wanda zai kawo min dauki.
A falo na yi sallah magariba ina sanye da hijab dina milk color na ji tsayawar motar Hafiz, sanin ba zai leko bangarena ba ya saka ban leka waje ba, kar na yi arba da bakinciki. Sai dai abun da ban yi zato ba ne ya faru, ganinsa na yi a falon kamar an jefoshi gabana ya shiga bugawa da mugun karfi ganin yayi tsaye a kaina yana kallona ni kuma na gagara cewa komai.

“Ina kika je jiya?”

Gabana ya fadi na gagara cewa komai sai hade yawu nake.

“Gurin Kareem? Office kika same shi ko gida.?”

Na sauke kaina kasa nan ma bana iya fadar komai.

“Ke wai sai yaushe zaki yi hankali?”

Na ji sanyi hawaye ya jika fuskata.

“Ta so muje”

Na dube shi da sauri. Kamin na yi wani yunkuri har ya mike tsaye, a dole ni ma na yi tsayen na bi bayansa sai ya juyo ya kalleni.

“Je ki saka talkaminki”

Na nufi gurin da talkamin suke na saka shi kam tuni ya fice daga falon ma. Ko da na fito ya tashi motarsa da kansa ya bude min front na shiga na zauna ya rufe sannan yaja motar muka fara tafiya, be kalli inda nake ba ni ma ban kalleshi ba sai sake saken nake a zuciyata ina zai kai ni? Me Kareem ya fada masa? Ina son na tambaya amman na kasa saboda bakinnya rufe min gam. Unguwarmu ya nufa yana ratsa gidajen dake ciki har ya isa kofar gidanmu, a nan na fahimci so yake ya hada ni da iyayena. Na kalleshi hawaye na min zuba.

“Fita ki shiga gida, ki zauna sai na neme ki...”

Ya fada ba tare da ya kalleni ba, na juyar da kaina dake rawa na bude motar na fita sai na yi tsaye na kasa daina kallonsa na kasa juyawa na shiga cikin gidan. Mun dauki mintuna a haka sannan ya miko hannu yaja gambun motar ya rufe yayi mata key ya bar ni a gurin tsaye cikin ruwan hawaye. Me kuma aka ce na ce? Yanzu kuma wane kalar laifin na aikata? Na zauna sai ya neme ni ya sake ni kenan ko kuma yaya?

#KhadeejaCandyPAID PAGE 9️⃣

©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024

Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar

And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....

You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153

_______•••_______

Na kusan minti talati tsaye kofar gidanmu kamar wanda aka cewa shiga ki tararda hisabinki haka tsoron shiga gidan ya kamani, domin na san waye mahaifina. Amman ba ni da wani gurin da ya fi gidan ina zan je? Ai ba ni na kawo kaina ba shi ya kawo ni. Cikin kasala da fargaba irin na wanda ya rasa makoma na saka kafata a gidan, duk yadda nake son hana hawayena zuba kasawa na yi. Sai kuma na yi rashin sa'a Baba na tsakar gidan yana alwala, ban yi sallama ba domin bakin har lokacin a rufe yake. Baba ya hasko ni da fitilarsa mai haske.

“Wa nake gani kamar Norriya?”

Tafiya kawai nake cikin gidan na kasa Cewa komai.

“Lafiya?”

Na durkusa a gabansa.

“Wani abu ne ya samu Hafizun?”

Na girgiza kai.

“Toh me ya faru?”

Hana ta fito daga daki tana kallona cikin tashin hankali.

“Cewa na zauna sai ya neme ni”

Fitilar dake hannun Baba ta subuce ta fadi kasa.

“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un, daman ai sai ba ke ba Noor, yanzu duk irin abubuwan da mutunen nan yayi min yayi miki sai da kika kai shi makura? Tafiya kika yi kina masa shashanci da sakarcin na ki ko? Har ya gaji yanzu ya koroki gida”

Na matsa baya da sauri jikina na rawa domin fadan da Baba yake min irin na son duka ne.

“Yaushe aka yi auren da zaki biyo dare yanzu ki ce wai yace ki zo gida?”

Na bude baki zan yi magana ya daka min tsawa ya cire talkaminsa ya jefani da shi.

“Ban son jin komai daga bakinki, marar mutunci daman ai na san sai kin masa shashanci, kina kallon yadda rayuwa take a gidan nan kin samu mai rufa miki asiri ne shi ne kika fara masa rashin kunya ko? Saboda ya sake ki ki auri Zafeer ke ga ki shim mai ruwa uku shashasha, sakinki yayi?”

Na girgiza kai.
Chapter 16 · 0% Book details