Sashe 14
Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yayi shiru yana kallona.
“Bayan aurenki baki hadu da Zafeer ba?”
“Aa Wallahi ban sake ganinshi, kuma Baba yace idan na sake magana da shi be yafe min ba, ance ma ya tafi baya garin nan”
“Akwai mai shiga dakinki ko ya taba jakarki?”
Na girgiza kai alamar aa.
“Dole akwai yadda aka yi Noor magani ba zai kawo kanshi ba, dole akwai yadda aka yi”
“Ni dai na yi zargin Aisha amman tace ita bata saka ba, ban san ya zan wanke kaina ba Kareem, yanzu baya min magana kuma baya shigowa gurina fushi yake da ni”
“Me yasa kika zargeta?”
“Saboda tace wai na fada mata sirrinsa kuma ban taba fada mata ba, kuma a gabansa tace na ce zan kira saurayina a waya kuma Wallahi ban taba ce mata ba”
“To kin taba barin jakarki a bangarenta?”
“Aa, amman Wallahi ban san a ina aka samu maganin ba, ni ban taba ganin wannan ballom din ba ban san me ake yi da shi ba”
Yayi shiru alamar tunani ni ma shirun nake ina hawaye.
“Kawo?”
Ya miko min hannunsa na bashi maganin da balloon din ya saka aljihu, sannan ya dago ya kalleni ido cikin ido ya sauke ajiyar zuciya.
“Noor ba zan iya miki komai ba, sai dai na baki hakuri, akwai dalilin da ya san ba zan shiga maganar ba”
“Wallahi ban san wanda ya saka ba Kareem ba nawa ba ne”
“Na yarda da ke Wallahi Noor i trust you, ko ma waye yana son yayi amfani da innocent you ya cutar da ke, Hafiz ya san abun da baki sani ba a game da ni, ba zan iya shiga maganar nan ba, wata kila shiga ciki zai iya janyo miki matsalar da ta fi wannan ba, iyaye ya kamata ki samu da wannan maganar iyayenki ko nasa”
“Baba ba zai yarda ba, Mama kuma bata ma saurare ni, ban san gidansu ba, kuma idan naje wata kila ba za su yarda ba”
Ya busar da iskar bakinsa damuwa ta bayyana a fuskarsa.
“Kawai ki yi hakuro Noor ki tafi gida kar ma ki fada masa kin zo nan”
“Tohm”
Na share hawayena wasu na sauko min na juya na fara tafiya, sai ya kira ni.
“Noor”
Na juyo.
“Kina da kudin Napep?”
Na girgiza kai, sai ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudi 2k ya ba ni, na karba ina kallon matarsa take tsaye jikin windows din sama tana kallonmu, shi ma daga kai yayi ya kalleta. Na juya sai kuma na sake juyowa a karo na biyu na kalleshi.
“Kareem ya keke?”
Yayi min kallon rashin fahimta.
“Rasuwar Mahaifiyarka ban samu yi maka gaisuwa ba, amman abun yana raina, na san kai ma kana cikin wata matsala kuma na zo maka da wata am sorry...”
Yayi min murmushi kawai. Ban sake cewa komai ba na kama hanya ina tafiya hawaye na sauko min har na fita cikin gidan. Ashe haka auren yake, ashe haka rayuwar auren take? Idan mutum yana cikin matsala babu wanda zai saurare shi, babu mai kawo masa dauki, shiyasa Baba yayi ta ganawa Mahaifiyarmu Azaba kala kala kuma ake ta ba shi gaskiya a duk lokacin da za a fadi matsalar.
A lokacin da na tari Napep na hau sai fargaba ta ta koma gurin hukuncin da zarar tarar a gida, domin be min izini ba na fita gashi kuma dare yayi ban dawoda wuri ba, kuma abun da naje nema ban same shi ba. Dubu daya na mikawa mai napep din da ya kawo ni gida, ban tsaya karbar canjin ba na shiga ciki, ina hango motar Hafiz wani irin faduwar gaba da tsoro suka mamayeni, a haka dai na daure na karasa bangare na taba kofar falon na murda sai na ji ta a rufe na sake murdawa na tura na jita a rufe gam da alama an saka mata key an rufe ne. A gurin na sulale kasa na zauna gaba daya na rasa me ke min dadi.
Ina zaune a gurin na hango Aisha ta fito da saurinta ta nufo inda nake babu jimawa Barrister ya biyo bayanta, ina ganin haka na mike tsaye ina kallonsa fargaba ta saka ni gaba kamar ance ga mutuwarki nan zuwa.
“Ba magana make miki ba?”
“Wallahi Barrister ba zan yarda ba, ko dai ka bude mata ta shiga ko kuma na kaita bangarena ta kwana ko kuma ni ma na bar maka gidan, cikin uku dole ayi daya, yanzu duk abun da ya faru mutane ni za su dorawa laifi, ace na hana muku zama lafiya, babu wanda zai iya wanke ni, Wallahi sai na yi ma Walida tsinanen duka a gidan nan, sai da na gargade ta karta fada maka amman saboda kunnen kashe ne da ita sai da ta fada”
“Karki kuskura ki taba min yarinya, kuma ki cire bakinki ki cire idonki akan zamantakewarmu, ba ke kike aurenta ba ni nake aurenta”
Yana fada ya jefo min keys din, sannan ya nuna mata bangarenta.
“Wuce mu je”
Ta share hawayenta, ta dora hannunta a cikinta da be gama girma ba.
“Dan Allah Noor ki natsu, ko da baka son auren mutum ba haka ake rayuwar aure ba, be kamata ki fita baki fada masa ba, ki sani yanzu baki da ikon kanki ikonki yana gurin mijinkin ne, kuma idan ba ki yi dan Allah ba baki yi dan shi ba ki yi dan ni mana, Wallahi idan wani abu ya faru tsakaninku ni za a zaga, kuma a zarge ni”
Cikin kuka take maganar sannan ya juya ta nufi bangarenta. Tsaye yayi yana kallona irin kallon na tsana da jin haushin mutum, sannan ya juya ya shige bangaren nata. Ni kuma na sunkuya jiki babu karfi na dauki keys din na saka na bude kofar na shiga, na rufe na jingina da kofar falon suuuu na tafi kasa na zauna ina kuka...
KAREEM POV.
Tsaye yayi yana kallonta har ta fice sannan ya juya ya nufi hanyar shiga cikin gidan. Murda kofar ya shiga.
“Sannu da zuwa...”
Yusura ta fada masa, sai ya kalleta fuska ya yabo ba fallasa ya amsa.
“Yauwa”
Ta sabuntawa kanta wasu dabi'u da hallaya da bata masa a baya, kamar kaima masa abinci a dakinsa yi masa sannu da zuwa ko a dawo lafiya idan zai fita. Tun a wacan ranar da Safeena ta leko gidan duk wasu hallaya da dabi'u nata sai suka sauya. Ya wuceta zai haura sama sai ta juyo tana kallonsa.
“Ina tunanin a matsayina na matarka ina da hakkin tsare mutunci da martaba ta”
Ya juyo.
“Akwai wani furuci ko wani aiki da nake yi da ke zubar da kimarki?”
“Kamar zuwan yan matanka, ya kamata ka san ina da girma a matsayina na matarka”
“Noor Matar Hafiz ce, amaryarsa Safeena matar aure ce miye baki sani ba a ciki?”
Ta masa wani kallo sannan ta ce.
“Ga abinci can a dakinka”
Ba tare da ya sake cewa komai ba ya haura saman ya shiga dakinsa. ko'ina kamshin sinasir yake da miyar da ta ji nama da manshanu. Amman ko kadan be kula abincin ba ya cire tufafinsa ya shiga yayi wanka kmar yadda ya saba ya fito ya saka kayan bachi, daman baya dawowa gidan sai ya cika cikinsa.
(Idan kika karanta min littafi baki biya ban yafe ba.)
A daren ya kwanta da tausayin Noor da kuma tunanin yadda zai bullowa lamarin, ta ko wane bangare idan ya hango sai ya ga kamar shiga maganar zai iya zama matsala. Sai dai ya yarda da wani abu daya, Noor bata aje maganin a jakarta domin idan har ajewa ta yi ba zata bari ya gani ba, wata kila dai tsakanin Aisha da Zafeer akwai mai shirya mata wani abun bata fahimta ba. Washe gari misalin 7am ya bar gidan saboda operation da za su a 8am a asibiti. Be wuce 10 -15 Min da fita ba Yusura ta shigo dakin kamar yadda ta saba ta fara bude kayan abincin da ta kawo ta ga be ci, daman kuma ta san ba zai ci ba domin yar kullum ce be cin abincinta ita ma kuma bata fasa girkawa. Sai da ta fitar da kayan sannan ta dawo dakin ta nufi gurin da yake aje kayan dauda ta bude ta dauko green shaddarsa ta jiya ta zauna gefen gadon tana lalaben aljihun kowane bangaren. Domin zuciyarta bata natsu da abun da ta hango Kareem ya karba a hannun yarinyar da ta taba fasawa goshi ba jiya...
#KhadeejaCandyPAID PAGE 8️⃣
©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024
Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....
You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153
_______•••_______
Wani irin faduwa gabanta yayi a lokacin da ta yi arba da abun da ke cikin rigar aljihun Kareem. Me hakan yake nufi Kareem yana tare da yarinyar nan kenan? Ba ita kadai ba wata kila har da Safeena, matan aure yake bi kenan? Shiyasa yake takura mata a lokacin da take fita gani yake kamar ita ma gurin wani zata tafi? Anya ma wannan Amaryar Hafiz ce? Idan har gaskiya ne me zai saka yayi tarayya da ita?
Ta mike tsaye da sauri ta fice daga dakin rike da maganin da robar ta shiga dakinta sai da ta dauki wayarta sannan ta tuna bata da number matar Hafiz domin ba kowa take hulda da shi ba a cikin matan abokan Kareem, iyakar ta da wasu gaisuwa. Number wayar Samira ta nema ta kirata suka gaisa cikin mutunci sannan ta bukaci Samira ta turo mata da number Aisha matar Hafiz.
“Wai daman baki da number ta”
“Ban taba karba ba”
“Kai kawata baki da kirki, bari na turo miki yanzu”
“Yauwa na gode, Ai na san kuma good time da ita ba zaki rasa number ta”
“Okay”
“Bayan aurenki baki hadu da Zafeer ba?”
“Aa Wallahi ban sake ganinshi, kuma Baba yace idan na sake magana da shi be yafe min ba, ance ma ya tafi baya garin nan”
“Akwai mai shiga dakinki ko ya taba jakarki?”
Na girgiza kai alamar aa.
“Dole akwai yadda aka yi Noor magani ba zai kawo kanshi ba, dole akwai yadda aka yi”
“Ni dai na yi zargin Aisha amman tace ita bata saka ba, ban san ya zan wanke kaina ba Kareem, yanzu baya min magana kuma baya shigowa gurina fushi yake da ni”
“Me yasa kika zargeta?”
“Saboda tace wai na fada mata sirrinsa kuma ban taba fada mata ba, kuma a gabansa tace na ce zan kira saurayina a waya kuma Wallahi ban taba ce mata ba”
“To kin taba barin jakarki a bangarenta?”
“Aa, amman Wallahi ban san a ina aka samu maganin ba, ni ban taba ganin wannan ballom din ba ban san me ake yi da shi ba”
Yayi shiru alamar tunani ni ma shirun nake ina hawaye.
“Kawo?”
Ya miko min hannunsa na bashi maganin da balloon din ya saka aljihu, sannan ya dago ya kalleni ido cikin ido ya sauke ajiyar zuciya.
“Noor ba zan iya miki komai ba, sai dai na baki hakuri, akwai dalilin da ya san ba zan shiga maganar ba”
“Wallahi ban san wanda ya saka ba Kareem ba nawa ba ne”
“Na yarda da ke Wallahi Noor i trust you, ko ma waye yana son yayi amfani da innocent you ya cutar da ke, Hafiz ya san abun da baki sani ba a game da ni, ba zan iya shiga maganar nan ba, wata kila shiga ciki zai iya janyo miki matsalar da ta fi wannan ba, iyaye ya kamata ki samu da wannan maganar iyayenki ko nasa”
“Baba ba zai yarda ba, Mama kuma bata ma saurare ni, ban san gidansu ba, kuma idan naje wata kila ba za su yarda ba”
Ya busar da iskar bakinsa damuwa ta bayyana a fuskarsa.
“Kawai ki yi hakuro Noor ki tafi gida kar ma ki fada masa kin zo nan”
“Tohm”
Na share hawayena wasu na sauko min na juya na fara tafiya, sai ya kira ni.
“Noor”
Na juyo.
“Kina da kudin Napep?”
Na girgiza kai, sai ya saka hannunsa aljihu ya ciro kudi 2k ya ba ni, na karba ina kallon matarsa take tsaye jikin windows din sama tana kallonmu, shi ma daga kai yayi ya kalleta. Na juya sai kuma na sake juyowa a karo na biyu na kalleshi.
“Kareem ya keke?”
Yayi min kallon rashin fahimta.
“Rasuwar Mahaifiyarka ban samu yi maka gaisuwa ba, amman abun yana raina, na san kai ma kana cikin wata matsala kuma na zo maka da wata am sorry...”
Yayi min murmushi kawai. Ban sake cewa komai ba na kama hanya ina tafiya hawaye na sauko min har na fita cikin gidan. Ashe haka auren yake, ashe haka rayuwar auren take? Idan mutum yana cikin matsala babu wanda zai saurare shi, babu mai kawo masa dauki, shiyasa Baba yayi ta ganawa Mahaifiyarmu Azaba kala kala kuma ake ta ba shi gaskiya a duk lokacin da za a fadi matsalar.
A lokacin da na tari Napep na hau sai fargaba ta ta koma gurin hukuncin da zarar tarar a gida, domin be min izini ba na fita gashi kuma dare yayi ban dawoda wuri ba, kuma abun da naje nema ban same shi ba. Dubu daya na mikawa mai napep din da ya kawo ni gida, ban tsaya karbar canjin ba na shiga ciki, ina hango motar Hafiz wani irin faduwar gaba da tsoro suka mamayeni, a haka dai na daure na karasa bangare na taba kofar falon na murda sai na ji ta a rufe na sake murdawa na tura na jita a rufe gam da alama an saka mata key an rufe ne. A gurin na sulale kasa na zauna gaba daya na rasa me ke min dadi.
Ina zaune a gurin na hango Aisha ta fito da saurinta ta nufo inda nake babu jimawa Barrister ya biyo bayanta, ina ganin haka na mike tsaye ina kallonsa fargaba ta saka ni gaba kamar ance ga mutuwarki nan zuwa.
“Ba magana make miki ba?”
“Wallahi Barrister ba zan yarda ba, ko dai ka bude mata ta shiga ko kuma na kaita bangarena ta kwana ko kuma ni ma na bar maka gidan, cikin uku dole ayi daya, yanzu duk abun da ya faru mutane ni za su dorawa laifi, ace na hana muku zama lafiya, babu wanda zai iya wanke ni, Wallahi sai na yi ma Walida tsinanen duka a gidan nan, sai da na gargade ta karta fada maka amman saboda kunnen kashe ne da ita sai da ta fada”
“Karki kuskura ki taba min yarinya, kuma ki cire bakinki ki cire idonki akan zamantakewarmu, ba ke kike aurenta ba ni nake aurenta”
Yana fada ya jefo min keys din, sannan ya nuna mata bangarenta.
“Wuce mu je”
Ta share hawayenta, ta dora hannunta a cikinta da be gama girma ba.
“Dan Allah Noor ki natsu, ko da baka son auren mutum ba haka ake rayuwar aure ba, be kamata ki fita baki fada masa ba, ki sani yanzu baki da ikon kanki ikonki yana gurin mijinkin ne, kuma idan ba ki yi dan Allah ba baki yi dan shi ba ki yi dan ni mana, Wallahi idan wani abu ya faru tsakaninku ni za a zaga, kuma a zarge ni”
Cikin kuka take maganar sannan ya juya ta nufi bangarenta. Tsaye yayi yana kallona irin kallon na tsana da jin haushin mutum, sannan ya juya ya shige bangaren nata. Ni kuma na sunkuya jiki babu karfi na dauki keys din na saka na bude kofar na shiga, na rufe na jingina da kofar falon suuuu na tafi kasa na zauna ina kuka...
KAREEM POV.
Tsaye yayi yana kallonta har ta fice sannan ya juya ya nufi hanyar shiga cikin gidan. Murda kofar ya shiga.
“Sannu da zuwa...”
Yusura ta fada masa, sai ya kalleta fuska ya yabo ba fallasa ya amsa.
“Yauwa”
Ta sabuntawa kanta wasu dabi'u da hallaya da bata masa a baya, kamar kaima masa abinci a dakinsa yi masa sannu da zuwa ko a dawo lafiya idan zai fita. Tun a wacan ranar da Safeena ta leko gidan duk wasu hallaya da dabi'u nata sai suka sauya. Ya wuceta zai haura sama sai ta juyo tana kallonsa.
“Ina tunanin a matsayina na matarka ina da hakkin tsare mutunci da martaba ta”
Ya juyo.
“Akwai wani furuci ko wani aiki da nake yi da ke zubar da kimarki?”
“Kamar zuwan yan matanka, ya kamata ka san ina da girma a matsayina na matarka”
“Noor Matar Hafiz ce, amaryarsa Safeena matar aure ce miye baki sani ba a ciki?”
Ta masa wani kallo sannan ta ce.
“Ga abinci can a dakinka”
Ba tare da ya sake cewa komai ba ya haura saman ya shiga dakinsa. ko'ina kamshin sinasir yake da miyar da ta ji nama da manshanu. Amman ko kadan be kula abincin ba ya cire tufafinsa ya shiga yayi wanka kmar yadda ya saba ya fito ya saka kayan bachi, daman baya dawowa gidan sai ya cika cikinsa.
(Idan kika karanta min littafi baki biya ban yafe ba.)
A daren ya kwanta da tausayin Noor da kuma tunanin yadda zai bullowa lamarin, ta ko wane bangare idan ya hango sai ya ga kamar shiga maganar zai iya zama matsala. Sai dai ya yarda da wani abu daya, Noor bata aje maganin a jakarta domin idan har ajewa ta yi ba zata bari ya gani ba, wata kila dai tsakanin Aisha da Zafeer akwai mai shirya mata wani abun bata fahimta ba. Washe gari misalin 7am ya bar gidan saboda operation da za su a 8am a asibiti. Be wuce 10 -15 Min da fita ba Yusura ta shigo dakin kamar yadda ta saba ta fara bude kayan abincin da ta kawo ta ga be ci, daman kuma ta san ba zai ci ba domin yar kullum ce be cin abincinta ita ma kuma bata fasa girkawa. Sai da ta fitar da kayan sannan ta dawo dakin ta nufi gurin da yake aje kayan dauda ta bude ta dauko green shaddarsa ta jiya ta zauna gefen gadon tana lalaben aljihun kowane bangaren. Domin zuciyarta bata natsu da abun da ta hango Kareem ya karba a hannun yarinyar da ta taba fasawa goshi ba jiya...
#KhadeejaCandyPAID PAGE 8️⃣
©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024
Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar
And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....
You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153
_______•••_______
Wani irin faduwa gabanta yayi a lokacin da ta yi arba da abun da ke cikin rigar aljihun Kareem. Me hakan yake nufi Kareem yana tare da yarinyar nan kenan? Ba ita kadai ba wata kila har da Safeena, matan aure yake bi kenan? Shiyasa yake takura mata a lokacin da take fita gani yake kamar ita ma gurin wani zata tafi? Anya ma wannan Amaryar Hafiz ce? Idan har gaskiya ne me zai saka yayi tarayya da ita?
Ta mike tsaye da sauri ta fice daga dakin rike da maganin da robar ta shiga dakinta sai da ta dauki wayarta sannan ta tuna bata da number matar Hafiz domin ba kowa take hulda da shi ba a cikin matan abokan Kareem, iyakar ta da wasu gaisuwa. Number wayar Samira ta nema ta kirata suka gaisa cikin mutunci sannan ta bukaci Samira ta turo mata da number Aisha matar Hafiz.
“Wai daman baki da number ta”
“Ban taba karba ba”
“Kai kawata baki da kirki, bari na turo miki yanzu”
“Yauwa na gode, Ai na san kuma good time da ita ba zaki rasa number ta”
“Okay”