← Book details Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 82

Sashe 22

Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“I win the case Doctor, we won it...”

Kareem yayi murmushi jindadi ya rufe even though dai baya cikin farinciki a yanzu.

“Congratulations to us, daman na san zaka yi winning ai, bana da shakkun akanka congrats”

“Thank you, ba karamin dadi na ji ba nasarar nan da na samu, domin babban case ne wannan zai kara min martaba sosai zai daga darajar aikina”

“Haka ne, ko da yaushe kana nasara Hafiz, kai mutumen mai tsananin jajirce da hikima da wayo tun muna yara, sai dai abun da yake ba ni mamaki shi ne yadda ka gagara fahimtar matanka ka gagara saita gidanka, kuma ka gagara fahimtar wacece ne? Wane irin zama ya dace ka yi da ita, kuma ya kamata ka tafiyar da rayuwarta”

“Na fahimci gidana Kareem, na san waye Noor, akwai abun da na fahimta a game ita da zai hanata kuma ni ma ya hana ni jindadin zaman aure da junanmu”

“Ka jefa yarinyar a cikin matsala Hafiz, ka rabata da masoyinta mutumen da she can dia for him, ka siye mahaifinta ka aureta yanzu kuma ka sake ta a wace hujja?”

Yayi shiru be ce komai ba sai tukin motar yake.

“Hafiz, zan roke wannan alfarmar a gareka, zan saka ka aikata saboda ina jin na isa da kai, bayan wannan ba zan sake rokon komai ba, ina son ka maida aurenka da Noor yau... Yarinyar tana wahala ka jefa rayuwarta a masifa, wani abun bakinciki kuma duk saboda ni ne, ka san baka sonta you don't have to married her What kind of wickedness is this? Na taina wayonka Hafiz”

“Wait... What....”

“Ka mai da aurenka da ita a yau Hafiz...”

“Amman kansan bana gari ina hanyar dawowa, na maka alkawari Kareem ina dawowa gidansu zan sauka zan daukota mu tafi gida tare, hakan ya maka..?”

“Yayi, thank you my friend”

“Ka fi karfin haka, amman ban taba jin ranka ya bace irin haka ba, baka taba bani umarni ko rokona wata alfarma irin wannan ba”

Kareem ya sauke ajiyar zuciya shi kanshi ya san he's too harsh for his friend, abun da be saba ba.

“ABun ne naka ya daure min kai Hafiz, na rasa gane ma kake nufi fa yarinyar nan, kuma a rasa wanda zai fada maka abun da ka aikata ba daidai ba ne ko Mama ko Baba”

“Babu wanda ya san ya sake ta sai Aisha ita kuma na gargadeta kar ta fadawa kowa, Mahaifinta kuma na fada masa zan waiwaye shi, tun daga lokacin ban sake amsa wayarsa ba”

“Ka bar abun da ya wuce ya wuce, a fuskanci gaba ita kanta a yanzu na san ta yi sanyi ba zata yi maka laifi ba, sai dai hakan ba zai saka na kasa fada maka ka yi hakuri da Noor ba, ba zan ce ka daina bawa matarka yarda 100% ba, na san maya suna sa wuyar fahimta wuyar sha'ani, but still ka rika bincike kamin ka aiwatar da abu, ka daina compare Noor da AISHA Noor yarinyar kuma bata san komai ba akan aure, Aisha kuma ta waye ta san komai ka tuna ba kai ne first husband dinta ba, kuma Aisha ta yi karatu har degree ba zaka hada ta da Noor da bata ma son zuwa makaranta ba, bawa ta irin wannan wayewar da duniyancin da yan matan yanzu suke da shi, and kishiyace ta koro Aisha daga gidan mijinta na farko, abu ne da ka san shi na san shi, har abada na zata taba son kishiya ba, babu ma macen da zata so kishiya you should think about it Hafiz”

“Hmmm...”

Kawai Hafiz yace, hango soyayyar Noor da yake a zuciyar abokinsa ne ya hana shi walwala da bude mata nata shafin soyayyar a zuciyarsa, yana rayuwa da matar da ba shi ya kamata ya aureta ba, kuma matar da abokinsa amininsa wanda ya zama dan'uwansa yake sonta, kuma a haka ita kuma a zuciyarta tana son wani dabam ba shi ba.

“Sai na dawo...”

Ya fada sannan ya kashe wayar. Kareem ya sauke ajiyar zuciya ya yi ma motarsa key ya karasa restaurant. Yana shiga office dinsa Cashier ya shigo suka fara lissafin abubuwa da suka kamata. Be fita ba sai 6pm Kareem ya saka aka kawo masa coffee ya sha saboda ya samu sauki stressed, domin jin yake jikinsa ya mutu gaba daya har wani abu yake ji kamar bachi kamar ba bachi ba.
Be bar office din ba sai da aka fara kiran sallah magariba. Yana fitowa sallah kira ya shigo wayarsa, yana ciro wayar ya duba. Number Hafiz ce ba tare da wani dalili ba gabansa ya fadi, babu tsoro ko fargaba amman haka zuciyarsa ta rika bugawa da mugun karfi yana ta kallon wayar tana ringing har ta katse ya kasa amsawa. A karo na biyu da aka sake kiran sai hannunsa da zuciyarsa suka hau rawa.

“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”

Ya furta domin be taba jin yanayi irin wannan ba, haka kuma Hafiz be taba kiransa ya gagara amsa wayar ba a yayinda take rike a hannunsa sai yau. Sai da aka sake kira a karo na uku sannan ya iya amsa wayar.

“Hello”

“Assalamu Alaikum... Barka dai”

“Barka ina mai wayar?”

Ya tambaya yana jin kirjinsa na masa wani irin nauyi.

“Wayar ya samu hatsari a hanyarsa ta shigowa garin Kano, mun samu wayarsa a motarsa sai muka bude da fingerprint dinsa, da muka shiga log calls na sa sai muka samu number ka ne da yayi waya da ita last”

“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un... Yana ina?”

“Mu sami'an kula da hadarukka ne, yanzu haka muna hanyar asibitin Malam Aminu Kano ne tare da shi”

Kareem ya yanke wayar da sauri ya nufi motarsa da gudu ya hau motar ya taka titi kamar wanda baya son rayuwarsa. Kamin su isa asibitin har ya rigasu ya fitowa motarsa ana fitowa da shi daga motar Road safety. Da gudu ya nufi abokinsa dake numfashi daker jini na fita ta cikin kansa.

“Hafiz... Hafiz...”

Haka ya bi gadonsa da aka dora shi akai aka wuce da shi ICU, Kareem ya dora hannu saman kai kamin ya sauke ya nufi motarsa, wayarsa ya dauko ya kira mahaifin Hafiz, yana dagawa ya ce.

“Hafiz din ya rasu ne?”

“Aa yanzu suka shigo da shi, Baba kar a fadawa Mama dan Allah”

“Tohm ni ma ai sun kira ni, gani nan hanyar asibitin”

Ya sauke wayar ya kira mahaifinsa ya fada masa. Yana sauke wayar wani likitan da ya san shi ya fito ya dafa Kareem.

“Doctor Kareem, Mutumen yana son magana da kai, ka shiga ka ganshi ka yi abun da ya dace...”

Kareem na jin haka gabansa ya tsinke ya fadi, domin shi ma likita ne ya gama fahimtar yaren na su. Cikin rashin kwarin guiwa ya shiga sai ya samu likita uku da Nurses suna kokarin tsayar da jini dake ta zuba amman sun kasa, not because of ba su iya ba, sai dan lokacin tafiya yayi mai ajiya zai karbi abarsa, dabara bata tare damuwa.

“Kareem... Allah yayi ba zan samu cika maka burinka ba, ba zan samu dawowa na tafi da Noor ba, ka gyara inda kake ganin na bata, ka san son yarinyar nan Kareem na ga haka a idonta da aikinka, na so ka da farinciki ne shiyasa na so ka aureta, ko yanzu lokaci be kure ba, dan Allah ka auri Noor Kareem ka samawa kanka farinciki, ga Iyeyena nan na bar mana amanarsu, ga Yayana ka ce a kula min da su, na yafewa kowa ka ce kowa ya yafe min, ba zan tashi ba, na san me nake ji na san me nake gani lokacin yayi babu tsayawa...”

Magana kawai yake ba dan yana ganin kowa ba domin an yanke ganin, ana saka masa oxygen yana cirewa yana magana daker. Kareem ya rike hannunsa yana kuka.

“Yaushe Momy ta tafi, ban gama warkewa daga ciwonta ba zaka tafi ka bar ni Hafiz?”

Hafiz ya cire Oxygen din zai yi magana bakinsa ya cika da jini. Sai ya fara kalmar shahada yana tari jinin yana koma masa yana sake fitowa. Mahaifinsa na shigowa wa'adin yana cika rai yayi halinsa Hafiz ya amsa kira...

#KhadeejaCandyPAID PAGE 1️⃣2️⃣

©KhadeejaCandy
©®Copyright
2024

Littafin nan na kudi ne, don't read if you didn't pay... One word kika karanta baki biya ni ba, ban yafe hakkina ba.
To be part of the journey pay 500 to 2451879008
ZenithBank
Hadiza Abubakar

And send the evidence of payment to my WhatsApp number 08036126660....

You can read my latest update on arewabooks a handle dina @KhadeejaCandy
https://www.arewabooks.com/book?id=659a94c8be87d7a51f831153

_______•••_______

Ina ta tsammanin zuwan Hafiz ko Kareem da sunan gyara amman ban ga ko dayansu, hakan kuma ba karamin Mamaki ya ba ni ba, sai na ke ganin kamar daman can Hafiz ba sona yake ba, ya aure ni ne kawai saboda yana son raba ni da wanda ke tsananin kaunata. Sai dai Kareem ya fi ba ni mamaki domin sanadinsa na san Hafiz ko kuma nace Hafiz ya san ni, kuma na kai masa kukana ba sau daya ba amman har yanzu be yi komai ba.

Idan na zauna ina tunani sai na ji zuciyata kamar zata fashe, gaba daya na rasa tudun dafawa na rasa ina zan saka kaina na ji sanyi, Mijin da ya dauke ni ya saki ni be waiwayo ba, abokinsa da shi ne sanadin auren be yi wani yunkuri ba, a gidanmu kuma Baba baya min magana saboda yana ganin laifina, Kanwata bata hira da ni, yayana baya kulani na rasa, hakan ya saka na dauki laifin na dorawa kaina. Kullum burina taya zan bullowa lamarin na samu komawa dakin mijina. Da yammancin wata labara na saka hijabina na saka talkamina na fito tsakar gidan. A lokacin Hana ce kadai zaune tana karatun biology, sau daya ta kalleni ta maida kanta bata ce min uffan ba duk kuwa da ta san fita nake da niyar ni.

“Hana”

Ta juyo ta kalleni ba tare da ta amsa ba.

“Abun da kuke min ya dace kenan? Kun maida ni bare a gidan nan?”

“Toh ya kike son ayi miki Noor, idan fa ba ki canja hali ba, zaman rayuwar duniya zai miki wuya”
Chapter 22 · 0% Book details