Sashe 19
Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita kadai take magana da kanta a lokacin da ya dade da fice daga dakin, so take ta kyautata masa kamin ta bar gidan, tun a wacan daren da Safeena ta zo gidan, wani bangare na zuciyarta ke raya mata wata kila saboda rashin samuwa kulawar da ya dace ne ya saka shi tunanin aron hannu ko kuma ma aron gaba daya, tana jin kamar idan ta mutu Allah zai tambaye ta ko da kuwa bayan ta bar gidan ne. But what happened yesterday ya canja tunaninta idan rashin samun kulawa ne ya kai shi ga kula Safeena a yadda take zargi, to ita wannan Noor din fa? Bayan abun da ta kama a aljihunsa wadda ta hango Noor din tana hannanta masa ga kuma abun da Aisha ta fada mata.
Now ta ji kamar ba zata iya tarar yakin ba, ba zata iya rumgumar wani dacin ba bayan wanda take ciki.
Takowa ta yi ta fito daga dakin ta shiga nata dakin, arba da ta yi da hoton yaranta biyu like a bango ya tsumata.
“Rabuwar ita kadaice mafita, ita kadai ce maslaha a gurina, nesanta da Kareem shi ne burin da na dade ina binnewa a zuciyata, dakun mutuwar Momy da nake a baya duk saboda samun yanci ne...”
Ya zauna kan gadonta tana kallon hoton hawaye na sauko mata.
“Yanci irin na ya mace mai burin auren wanda take so, yanci na rayuwa a karkashin inuwar wani namijin dabam da zuciyata zata yi na'am da shi ba Kareem ba, Wallahi kullum da wannan bakinciki nake kwana da shi nake tashi. Momy ta hada wuta da ruwa ne ba tare da tunani ba, bama haduwa da juna, ba mu dace da juna ba, dan Allah ku yafe mini”
Ta kwanta saman gadon tana hawaye, tana jin kaunar yayanta domin babu ruwansu a cikin matsalarsu, sai dai kuma Kiyayyar Kareem ta fi soyayyar yaransa karfi a zuciyarta.
*** *** ***
Tuki yake da hannu daya a lokacin da wayarsa ta yi ringing. Sai da ya kalli mai kiran sannan ya daga ya sakata a speaker.
“Hello”
“Doctor Ka fito gida?”
“Eh ya aka yi?”
“Wani dan abu na aikata”
“Na me?”
Barrister ya sauke ajiyar zuciya ta ciki wayar sannan ya ce.
“Na saki Noor..!! Na san ba abu ne mai dadi ba, but ina ganin kamar hakan zai fi zame mana mafita, saboda akwai abubuwanta da ban gamsu da su ba, kuma ina ganin kamar ba zata iya canjawa ba”
Doctor ya tabe baki ya kalli ne mirror sannan yayi overtake yana tabe baki.
“Okay.. Daman aure rai ne da shi, na wasu ya kan dade na wasu kuma be dade ba, Allah yasa hakan shi ne mafita alheri, ya baka zaman lafiya da matarka, ita kuma Allah ya bata wanda ya fika ya dace da ita..”
Hafiz yayi shiru ya kasa amsa da Ameen kuma ya kasa sake wani furucin, all what he expected Kareem ya fada hakan da ka yi ka yi daidai or no baka yi daidai ba. Sai dai kam be ji haka daga gurin abokin shawararsa ba. Kareem ya kashe wayar jin Hafiz be ce komai ba kuma be yanke kiran ba. Tuki yake cikin natsuwa har ya ratso cikin unguwarsu Noor, a gaban gidansu ya faka ya bude motar ya fito rike da wayarsa. Nabil ya kira yana dagawa ya ce.
“Ranka ya dade”
“Kana gida?”
“Eh ina gida ranka ya dade”
“Fito ina waje”
Before Kareem yayi blink Nabil ya fito ya fito da saurinsa. At that time ne Kareem ya daga kai yana kallon kofar gidanta data kone kana ganin gidan zaka san an yi gobara.
“Oga Allah yasa ba wani laifi na yi ba”
Kareem ya mika masa hannu da suna gaisawa amman Nabil ya ki ya karba saboda yana jin kamar kuskuren gaisawa da mai gidansa a lokacin da yake karkashinsa, shi kuma yake samansa sosai.
“Ka yi laifi zan biyo ka har gida? Me yasa kullum tunaninka ka yi laifi ne ko dai akwai laifin da kake min ne a restaurant ban sani ba?”
Nabil ya shafa kansa yana dariya.
“Aa Wallahi oga, na ga yanzu Noor bata nan balle ace ita ta janyo min wani abun a gurinka”
Kareem be biye mishi da maganar ba sai ya tambaye shi yaushe aka yi gobara a gidan.
“An yi sati uku yanzu”
“Subhanallahi, Allah maida alheri na zo gurin mahaifinku ne yana ciki?”
“Eh yana ciki kasan safiya ce yanzu, be isa fita ba”
“Good ka yi masa sallama, amman kamin nan me yasa kullum nake samunka a gida baka karatu ne?”
“Na fara kuma abun ya zo da dan nauyi sai na aje sai nan gaba kuma”
Nabil ya fada yana sosa kansa cike da kunya.
“Allah ya taimaka, sallamo shi”
“Ameen ranka ya dade”
Nabil ya juya ya shiga cikin gidan, nan ma babu jimawa Baba ya fito yana gyaran hula ganin Kareem ya saka shi washe hakora ya mika masa hannu biyu suka gaisa.
“Baraba da zuwa, baka shigo ba kake zaune a waje”
“Ba sai na shiga ba, magana ce kawai na zo da ita zamu iya yi a waje ma Baba”
“Toh Allah yasa dai lafiya”
“Lafiya Kalau, Irin na amsu lafiya ba irin na masu matsala ba, Baba na zo da magana ne mai nauyi kuma daci sai ka jure”
“Kar ka ji komai fada min ko minene kai tsaye”
Kareem ya sauke ajiyar zuciya.
“Baba jiya, ko kuma ma na ce kamin jiyan Noor ta samu matsala da mijinta wanda amini ne a gurina, kusan ma ni ne dalilin auren domin sanadina ya san ta ni kuma na san ta sanadin danka Nabil”
“Haka ne, ai ta zo nan na korata bana son sauraren komai daga gareta, domin na fahimce take takenta so take ta kashe auren, yaushe aka yi auren ma? Fisabillilahi, a yau ma nake da niyar tafiyar gidan shi Hafizun na ji rashin mutuncin da take masa, domin komai aka ce Noor ta yi bana musu yarinya ce da bata da jin magana sam”
“Amman ka bincike me yasa ta zo gida?”
“Bana bukatar ji, ai ita mace baiwa ce namiji ko dukanta yake be kamata ta yi yaji ba ko ta zo gida kawo shedu idan na bata wannan kofar kamin ka ankara kashe auren zata yi”
“Zaman lafiya be tsawaita aure, tashin hankali be gajarta aure, ko ya kashe rai ne da shi ko ana zaune lafiya mutuwa yake, idan lokaci yayi, wani kuma ga tashin hankali amman auren ya ki mutuwa saboda lokacin rabuwar be yi ba, da dadi da ba dadi as long as auren yana raye za a zauna”
“Haka ne, amman Noor ba a nuna mata wannan, yarinya da bata da tunani babu natsuwa a tare da ita”
“Amman ko minene ya kamata ka saurari damuwarta, ka aura mata wanda bata so at her young age kuma ta yarda ta aureshi, yanxu kuma ta zo da matsala ya kamata ka aurareta, mace bata da gidan da ya wuce na uba a duniya idan aka cire gidan mijin, wani bangaren ma gidan uban ya kan fi na mijin, domin yanzu da ya korota gidan ubanta ta doso, da namiji ne shi zai yi korar ko kuma ya nemi wani gurin ya fake, irin haka yana saka rayuwar mace ta lalace”
“Wato duk abun da za a fada maka ba zaka gane ba, ita Noor dabam take ta sauran yaya, kuma ka duba yadda abokin ka yayi hidima da mu, ace wai Noor ta kwaso jiki ta zo gida ai be kamata ma na saurareta ba”
“Ina ganin ku kuka haifi Noor a hannunku ta girma ta yi wayo, amman ko ku din ba ku fi ni fahimtarta ba, ban sani ba ko dan ina kallonta a wani yanayi ne da ku ba a baka kuke kallonta ba”
“Ni fa na haifi noor na san halinta gaba da baya”
Kareem ya aje numfashi da karfi.
“Ko ma dai minene yanzu, Baba ina son ka karbi wannan kaddarar, dan Allah ka yi hakuri ya karbi Noor, ni kuma zan shiga na fita na ga na yi abun da ya dace”
“To wai sakinta yayi ne ko kuma me?”
“Sakinta yayi, ni kaina ban san abun da ya hada su ba, amman dai yanzu haka Noor din tana asibiti saboda buga mata abu da aka yi a kai ta ji ciwo sosai”
“Yayi daidai ai kara da yayi mata duka, daman Noor bata san arziki ba, wato ni zata watsawa kasa a ido ko? Aure ko wata daya be yi ba ta an sakota ta dawo? Oh Allah na gode maka da ka yi min wannan kyautar, yarinyar nan ban da bakinciki babu abun da take saka min tun da aka haife ta, yanzu ina murna na aurar da ita na huta ita ma ta huta, sai kuma yanzu na ji wani labarin na dabam? So take fita sallah cikin jaama'a ma ya gagareni?”
Kareem yayi shiru ba tare da fada masa dalilin dukan ba, ko fayyace masa cewar ba Hafiz ne yayi ba matarsa ce ta yi mata duka a rashin fahimta. Sai kawai ya dora da
“Hakuri zaka yi Baba, komai zai wuce”
Baba yayi baya baya ya jingina da ginin gidansa, gaba daya furucin saki da Kareem ya furta ya fi jefa Baba cikin damuwa, duk wani buri da hangen dafgen da Baba yake a auren Hafiz da Noor ta yi ya sha ruwa.
“To wai saki har nawa yayi mata ne?”
“Daya ne ina zaton ba zai wuce haka ba, ni dai abun da nake so daga gurinku shi ne hakuri ku karbeta, zan binka komai kuma da yardar Allah zata koma dakinta amman dole sai ka yi hakuri Baba”
Kareem ya fada ne kawai saboda ya samawa Noor matsuguni a gidansu ba wai dan yana da niyar yin wani abun akan auren ba. Be ji zai iya sake tuntubar Hafiz ma da maganar ba balle har yayi ruwa da tsaki Noor ta koma gurinsa.
“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un, wannan yarinya ba zata tana canja hali ba, to sai ta zo ta zauna ai ta ji idan zaman gidan dadi ne da shi, sakarya kawai marar hankali”
Now ta ji kamar ba zata iya tarar yakin ba, ba zata iya rumgumar wani dacin ba bayan wanda take ciki.
Takowa ta yi ta fito daga dakin ta shiga nata dakin, arba da ta yi da hoton yaranta biyu like a bango ya tsumata.
“Rabuwar ita kadaice mafita, ita kadai ce maslaha a gurina, nesanta da Kareem shi ne burin da na dade ina binnewa a zuciyata, dakun mutuwar Momy da nake a baya duk saboda samun yanci ne...”
Ya zauna kan gadonta tana kallon hoton hawaye na sauko mata.
“Yanci irin na ya mace mai burin auren wanda take so, yanci na rayuwa a karkashin inuwar wani namijin dabam da zuciyata zata yi na'am da shi ba Kareem ba, Wallahi kullum da wannan bakinciki nake kwana da shi nake tashi. Momy ta hada wuta da ruwa ne ba tare da tunani ba, bama haduwa da juna, ba mu dace da juna ba, dan Allah ku yafe mini”
Ta kwanta saman gadon tana hawaye, tana jin kaunar yayanta domin babu ruwansu a cikin matsalarsu, sai dai kuma Kiyayyar Kareem ta fi soyayyar yaransa karfi a zuciyarta.
*** *** ***
Tuki yake da hannu daya a lokacin da wayarsa ta yi ringing. Sai da ya kalli mai kiran sannan ya daga ya sakata a speaker.
“Hello”
“Doctor Ka fito gida?”
“Eh ya aka yi?”
“Wani dan abu na aikata”
“Na me?”
Barrister ya sauke ajiyar zuciya ta ciki wayar sannan ya ce.
“Na saki Noor..!! Na san ba abu ne mai dadi ba, but ina ganin kamar hakan zai fi zame mana mafita, saboda akwai abubuwanta da ban gamsu da su ba, kuma ina ganin kamar ba zata iya canjawa ba”
Doctor ya tabe baki ya kalli ne mirror sannan yayi overtake yana tabe baki.
“Okay.. Daman aure rai ne da shi, na wasu ya kan dade na wasu kuma be dade ba, Allah yasa hakan shi ne mafita alheri, ya baka zaman lafiya da matarka, ita kuma Allah ya bata wanda ya fika ya dace da ita..”
Hafiz yayi shiru ya kasa amsa da Ameen kuma ya kasa sake wani furucin, all what he expected Kareem ya fada hakan da ka yi ka yi daidai or no baka yi daidai ba. Sai dai kam be ji haka daga gurin abokin shawararsa ba. Kareem ya kashe wayar jin Hafiz be ce komai ba kuma be yanke kiran ba. Tuki yake cikin natsuwa har ya ratso cikin unguwarsu Noor, a gaban gidansu ya faka ya bude motar ya fito rike da wayarsa. Nabil ya kira yana dagawa ya ce.
“Ranka ya dade”
“Kana gida?”
“Eh ina gida ranka ya dade”
“Fito ina waje”
Before Kareem yayi blink Nabil ya fito ya fito da saurinsa. At that time ne Kareem ya daga kai yana kallon kofar gidanta data kone kana ganin gidan zaka san an yi gobara.
“Oga Allah yasa ba wani laifi na yi ba”
Kareem ya mika masa hannu da suna gaisawa amman Nabil ya ki ya karba saboda yana jin kamar kuskuren gaisawa da mai gidansa a lokacin da yake karkashinsa, shi kuma yake samansa sosai.
“Ka yi laifi zan biyo ka har gida? Me yasa kullum tunaninka ka yi laifi ne ko dai akwai laifin da kake min ne a restaurant ban sani ba?”
Nabil ya shafa kansa yana dariya.
“Aa Wallahi oga, na ga yanzu Noor bata nan balle ace ita ta janyo min wani abun a gurinka”
Kareem be biye mishi da maganar ba sai ya tambaye shi yaushe aka yi gobara a gidan.
“An yi sati uku yanzu”
“Subhanallahi, Allah maida alheri na zo gurin mahaifinku ne yana ciki?”
“Eh yana ciki kasan safiya ce yanzu, be isa fita ba”
“Good ka yi masa sallama, amman kamin nan me yasa kullum nake samunka a gida baka karatu ne?”
“Na fara kuma abun ya zo da dan nauyi sai na aje sai nan gaba kuma”
Nabil ya fada yana sosa kansa cike da kunya.
“Allah ya taimaka, sallamo shi”
“Ameen ranka ya dade”
Nabil ya juya ya shiga cikin gidan, nan ma babu jimawa Baba ya fito yana gyaran hula ganin Kareem ya saka shi washe hakora ya mika masa hannu biyu suka gaisa.
“Baraba da zuwa, baka shigo ba kake zaune a waje”
“Ba sai na shiga ba, magana ce kawai na zo da ita zamu iya yi a waje ma Baba”
“Toh Allah yasa dai lafiya”
“Lafiya Kalau, Irin na amsu lafiya ba irin na masu matsala ba, Baba na zo da magana ne mai nauyi kuma daci sai ka jure”
“Kar ka ji komai fada min ko minene kai tsaye”
Kareem ya sauke ajiyar zuciya.
“Baba jiya, ko kuma ma na ce kamin jiyan Noor ta samu matsala da mijinta wanda amini ne a gurina, kusan ma ni ne dalilin auren domin sanadina ya san ta ni kuma na san ta sanadin danka Nabil”
“Haka ne, ai ta zo nan na korata bana son sauraren komai daga gareta, domin na fahimce take takenta so take ta kashe auren, yaushe aka yi auren ma? Fisabillilahi, a yau ma nake da niyar tafiyar gidan shi Hafizun na ji rashin mutuncin da take masa, domin komai aka ce Noor ta yi bana musu yarinya ce da bata da jin magana sam”
“Amman ka bincike me yasa ta zo gida?”
“Bana bukatar ji, ai ita mace baiwa ce namiji ko dukanta yake be kamata ta yi yaji ba ko ta zo gida kawo shedu idan na bata wannan kofar kamin ka ankara kashe auren zata yi”
“Zaman lafiya be tsawaita aure, tashin hankali be gajarta aure, ko ya kashe rai ne da shi ko ana zaune lafiya mutuwa yake, idan lokaci yayi, wani kuma ga tashin hankali amman auren ya ki mutuwa saboda lokacin rabuwar be yi ba, da dadi da ba dadi as long as auren yana raye za a zauna”
“Haka ne, amman Noor ba a nuna mata wannan, yarinya da bata da tunani babu natsuwa a tare da ita”
“Amman ko minene ya kamata ka saurari damuwarta, ka aura mata wanda bata so at her young age kuma ta yarda ta aureshi, yanxu kuma ta zo da matsala ya kamata ka aurareta, mace bata da gidan da ya wuce na uba a duniya idan aka cire gidan mijin, wani bangaren ma gidan uban ya kan fi na mijin, domin yanzu da ya korota gidan ubanta ta doso, da namiji ne shi zai yi korar ko kuma ya nemi wani gurin ya fake, irin haka yana saka rayuwar mace ta lalace”
“Wato duk abun da za a fada maka ba zaka gane ba, ita Noor dabam take ta sauran yaya, kuma ka duba yadda abokin ka yayi hidima da mu, ace wai Noor ta kwaso jiki ta zo gida ai be kamata ma na saurareta ba”
“Ina ganin ku kuka haifi Noor a hannunku ta girma ta yi wayo, amman ko ku din ba ku fi ni fahimtarta ba, ban sani ba ko dan ina kallonta a wani yanayi ne da ku ba a baka kuke kallonta ba”
“Ni fa na haifi noor na san halinta gaba da baya”
Kareem ya aje numfashi da karfi.
“Ko ma dai minene yanzu, Baba ina son ka karbi wannan kaddarar, dan Allah ka yi hakuri ya karbi Noor, ni kuma zan shiga na fita na ga na yi abun da ya dace”
“To wai sakinta yayi ne ko kuma me?”
“Sakinta yayi, ni kaina ban san abun da ya hada su ba, amman dai yanzu haka Noor din tana asibiti saboda buga mata abu da aka yi a kai ta ji ciwo sosai”
“Yayi daidai ai kara da yayi mata duka, daman Noor bata san arziki ba, wato ni zata watsawa kasa a ido ko? Aure ko wata daya be yi ba ta an sakota ta dawo? Oh Allah na gode maka da ka yi min wannan kyautar, yarinyar nan ban da bakinciki babu abun da take saka min tun da aka haife ta, yanzu ina murna na aurar da ita na huta ita ma ta huta, sai kuma yanzu na ji wani labarin na dabam? So take fita sallah cikin jaama'a ma ya gagareni?”
Kareem yayi shiru ba tare da fada masa dalilin dukan ba, ko fayyace masa cewar ba Hafiz ne yayi ba matarsa ce ta yi mata duka a rashin fahimta. Sai kawai ya dora da
“Hakuri zaka yi Baba, komai zai wuce”
Baba yayi baya baya ya jingina da ginin gidansa, gaba daya furucin saki da Kareem ya furta ya fi jefa Baba cikin damuwa, duk wani buri da hangen dafgen da Baba yake a auren Hafiz da Noor ta yi ya sha ruwa.
“To wai saki har nawa yayi mata ne?”
“Daya ne ina zaton ba zai wuce haka ba, ni dai abun da nake so daga gurinku shi ne hakuri ku karbeta, zan binka komai kuma da yardar Allah zata koma dakinta amman dole sai ka yi hakuri Baba”
Kareem ya fada ne kawai saboda ya samawa Noor matsuguni a gidansu ba wai dan yana da niyar yin wani abun akan auren ba. Be ji zai iya sake tuntubar Hafiz ma da maganar ba balle har yayi ruwa da tsaki Noor ta koma gurinsa.
“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un, wannan yarinya ba zata tana canja hali ba, to sai ta zo ta zauna ai ta ji idan zaman gidan dadi ne da shi, sakarya kawai marar hankali”