Sashe 68
Taki Zaman Aure Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na ji ya fada domin yayi sallama be ji kowa ya amsa masa ba. Sai da na tabbatar ya shiga dakin, sannan na fito kitchen din.
Dakin da Hana take na shiga na nufi gurin da takardunta suke na bude jakarta na dauko littafi na cire paper na dauki pen, sannan na kalli kofar bandakinta da nake jiyo kukanta na munafurci daman na san haka zata yi ai, karshen munafuki jin kunya.
Na shiga da kuzarina, domin na gama yanke shawara Wallahi ko auren Abdull ne rayuwata yau kam na shiryawa mutuwa domin ba zan iya kara awa daya da aurensa ba. Zaune na same shi sanye da suit dinsa na aiki da be cire ba yana duba wayarsa da alama wani abun yake kallo. A lokacin da na kalli fuskarsa sai na ji ban taba tsanar kowa a duniya kamar yadda nake jin tsanarsa ba. Kusa da shi na karasa na aje masa takardar da biron.
Ya kalli takardar da biron da na aje masa.
“Miye wannan?”
“Me ka gani?”
Na tambaya ina kallonsa cike da tsana da kyama.
“Takardar da biro”
“So na nake ka rubuta min saki”
Ya kalleni.
“Are you okay?”
“Ka ji ni ai i mean it ka rubuta min saki na ce!!!”
Na karashe zance a tsawace. Ya aje wayar hannunsa ya mike tsaye.
“Saki? My soul kin san me kike fada kuwa? Ba a wasa da wannan kalmar fa”
Ya dafa ni sai na buge hannunsa ina tauna hakora ta cikin bakina.
“Wani abu kika sha yau?”
“Eh... Na sha bala'i da masifa da wutar da zan amayar maka a yanzu nan idan baka sake ni ba”
“Na sake ki kamar yaya me yake damunki?”
“Kai ne kai kake damuna Abdullahi, na tsane ka, damba marar tunani dan duniya wulakantacce, barikin ta wuce waje har sai ta shigo cikin gidana? Sai ka hurumina da yar'uwata?”
“Kina da hankali kuwa? Ni kike kira damba...”
Ya daga hannu zai mare ni, a nan Allah ya ba ni iko da karfin iya rike hannun da dukanin karfina.
“Maci amana, karka sake tsinanen hannunka ya kai ga halattaciyar fuskata ma ci amana ka bi yaya ka bi kanwarta, haihuwar hasara”
“Okay ta kwashe karya da gaskiya ta fada miki kin zo kina zargina da abun da ban aikata ba ko? Saboda tsaurin ido har ki kalleni kina kirana da suna kala kala ko? Ni fa mijinki Noor”
Na tofa masa yawu a fuska.
“Allah ya kiyaye Allah ya kiyaye yanzu kam, da can amman ban da yanzu”
“Okay rashin kunya zaki nuna min ko? To sai na ga idan akwai uban da ya isa ya saka na sake ki, kuma kika sake fada min wata maganar banza sai na ci ubanki yanzu nan”
“Ubana yayi maka yawa, kuma babu wanda zai saka kaka kai zaka sake ni dan kanka, wato kai da yake namiji mai karfin hali dan duniya har kana da bakin yakata ko? Taya zaka ba ni maganin bachi ka tafi ko wane dare ka kwanta da yar'uwata sai asuba ka dawo ku ci amanata a tare kuma ka ce ba zaka sake ni ba? Wallahi karya kake Abdullahi”
Ya nuna kansa yana murje ido kamar da gaske be aikata ba.
“Ni nake saka miki maganin bachi?”
“Aa ni nake sakawa kaina, wanda ka ba ni jiya ya zube ban sha ba, ina kallon lokacin da ka tashi daga dakin nan ka tafi dakin Hana, na labe na ji abun da kuke magana a kai, har ciki za ku zubar”
Na fashe da kuka domin ba ni da wani abun yi a yanzu kamar shi.
“Ba laifinka ba ne, laifin yar'uwata ne ita da ta ci amanata, dama kum jira wata kila gurin haihu zan mutu ai sai ka aureta ku zauna”
“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”
Ya sassauta muryarsa.
“Noor Wallahi aikin sheidan ne, kuskure ne aka samu, me Hana ta fada miki?”
“Ban saurareta ba, kamar yadda ba zan saurareka ba, saki kawai nake so ka sake ni”
“Ni ba zan sake ki ba Ina son ki Noor shedan ne Wallahi”
Kalmar ina son ki ta saka na ji kamar da wuka a kusa na daka masa a sautin zuciya. Ya matso kusa da ni
“Abu ne da zamu tsaya mu rufawa juna asiri, ita yar'uwarki ce ni kuma mijinki ne, kuma ga cikina a jikinki Noor, Wallahi na miki alkawari ba zan sake ba”
“Gobe zan tafi na bar muku gidan, ku cigaba da aikata abun da kuke har mahadi ya bayyana, ni dai ka sake ni”
“Ba zan sake ki ba Noor ni ba zan sake ki ba, ni ban taba aikata komai ba sai a wannan karon da Allah ya kawo tsautsayi”
“Karya kake, ba wannan ne karon farko ba Wallahi kawai dai ban gane ba sai yanzu, shiyasa tun kamin ka aure ni kake ta taba ni, da na yi magana ka ce gwada ni kake yi, ashe gwadawa kake ka gani idan ni yar iska ce na amince maka a waje, ka gama da ni ka tafi, da hakan be samu sai ka bijiro da maganar aure, da na samu ciki kuma sai na daina burge ka saboda ba auren Allah ba ne, auren sha'awa ka yi min. Sai kuma sha'awarka ta koma gurin kanwata jinina, ita kuma bata duba alaka ba ta yarda kuka taru kuka ci amanata”
Na dafe zuciyata ina bakincin da ban fahimci wannan red flag din ba tun farko, ga kuma Safeena ma ai izina ce.
Ya dafe kansa ya juya ya juyo ya fara safa da marwa kamin ya samu tsayawa gabana a rikece har da fashe min da kuka.
“Dan Allah ki kwantar da hankalinki mu yi magana ta fahimta, sakinki zai bata abubuwa ne kawai, ina zaki je da ciki? Abun nan aikin shaidan ne Noor zai iya fadawa kan kowa, zan tafi na bar miki gidan har hankalinki ya kwanta amman ni ba zan sake ki ba”
A take kukan ya yanke min.
“Ba zaka sake ni ba saboda kana tsoron kar a tambayi dalilin mutuwar na fadi cewar kai da yar'uwata kuka ci amanata?”
Yayi kamar be ji ba dauki wayarsa yana kuka zai fice dakin.
“Ba zaka sake ni ba, sai na hada maka cewar dan da Safeena ta haifa maka yanzu ba jininka ba ne, ďan falkanta ne, ex-boyfriend dinta? Sai na fada maka dalilin da ya saka Safeena ta daina daga maka hankali akan aurena? Sai na fada maka na san Safeena irin wanin da baka yi mata ba? Sai na fada maka a duk lokacin da ka bar Kano tana tarayya da Ex dinta ne har sai ka dawo? Sai na fada maka Safeena ta taba ji min ciwo a hannu saboda ta yi tunanin Ex dinta kuma falkamta so na yake, saboda kishinsa?”
Ya juyo ya kalleni kukan da yake ya tsaya.
“Kina cikin bachin rai ne, zaki iya fadar komai Noor na sani”
“Ina cikin bacin rai, amman ba cikin gushewar hankali ba, idan baka yarda ba ka dauki yaron ka gwada jininsa da naka mana, ka cancanci haka ai, daman shege sai dan iska, a da har mamakin dalilin Safeena nake na aikata haka, ashe ta yi daidaita kai din tsohon shege ne”
Ya daka min tsawa.
“Ya ishe ki haka yanzu kam ya ishe ki haka? Mace nawa take kama mijinta yana abun da be dace ba amman ta rufa masa asiri a zaune, balle ni da kaddara ce kuma ba ni kadai ba har da yar'uwarki, kusan ma ita ta ja ra'ayi a komai”
“Wallahi ko kai ne dan autan maza na gama zaman aure da kai Abdull, ko ka sake ni ko na daga na kira uwarka a yanzu na fada mata abun da ka aikata da kanwata kuma na tabbatar mata cewar ďan da Safeena take shayarwa a yanzu ba jikanta ba ne? Domin ba jininka ba ne, na yarda idan aka bincika aka tararda tsabanin haka a kai ni kotu, ko dai so kake na kira kanenka da mahaifiyata ma fada musu? Kwanciyar hankalinka ka sake ni, Ba zan fadawa kowa abun da kuka aikata ba ni na bar ku da Allah”
A fusace ya nufi takardar ya dauka yayi rubutu a kai ya jefa min a fuska.
“Ke ce da bakinciki ba ni ba...”
Ya nufi kofa.
“Allah ya raba ni da bakinciki tun da ya raba ni da kai”
Na fashe da kuka mai karfi. Na yi kuka kuka sosai kuka irin na macen da rauni ya mamayeta ta rasa makoma, saki nake so kuma na samu yanzu idan na koma gida me zan fadawa iyayenmu? Na fada cikina ina bakinciki da ban zaba masa uba na gari ba. A dakin na kwana, sai dai bachi be dauke ni ba, bayan ruwa bana shan komai ba, shi kuma tun da ya fita be dawo ba, har garin Allah ya waye.
Cikin kuka da bakinciki na yi sallah Asuba, na roki Allah ya sanyaya min zuciyata ya sanya min saka min kana'a domin har lokacin ban ji zan iya yi ma yar'uwata wata bakar addu'a ba, har gobe ita din jini na ce idan wani abun ya faru da ita kamar ya faru da ni ne. Ni dai na san na barta da Allah shi ya san abun da ya dace da ita kuma shi ya san sakamakon da zai yi min akanta.
Misalin shida da rabi na fara hada kayana cikin akwaiti sai da na yi nisa da hadawa sai kuma, sai kuma na ji bana bukatar kala ko daya domin Abdull ne ya siya, a yanzu kuma bana sha'awar duk wani abu mai alaka da shi. Cikinsa ma da yake jikina da ace zan iya da cire shi zan yi na aje masa a gidansa na yi tafiyata. Jaka kawai na nufa na dauka na hada yan kudadena na dauki wayata ita ma dan ta zame min dole a yanzu.
Dakin da Hana take na shiga na nufi gurin da takardunta suke na bude jakarta na dauko littafi na cire paper na dauki pen, sannan na kalli kofar bandakinta da nake jiyo kukanta na munafurci daman na san haka zata yi ai, karshen munafuki jin kunya.
Na shiga da kuzarina, domin na gama yanke shawara Wallahi ko auren Abdull ne rayuwata yau kam na shiryawa mutuwa domin ba zan iya kara awa daya da aurensa ba. Zaune na same shi sanye da suit dinsa na aiki da be cire ba yana duba wayarsa da alama wani abun yake kallo. A lokacin da na kalli fuskarsa sai na ji ban taba tsanar kowa a duniya kamar yadda nake jin tsanarsa ba. Kusa da shi na karasa na aje masa takardar da biron.
Ya kalli takardar da biron da na aje masa.
“Miye wannan?”
“Me ka gani?”
Na tambaya ina kallonsa cike da tsana da kyama.
“Takardar da biro”
“So na nake ka rubuta min saki”
Ya kalleni.
“Are you okay?”
“Ka ji ni ai i mean it ka rubuta min saki na ce!!!”
Na karashe zance a tsawace. Ya aje wayar hannunsa ya mike tsaye.
“Saki? My soul kin san me kike fada kuwa? Ba a wasa da wannan kalmar fa”
Ya dafa ni sai na buge hannunsa ina tauna hakora ta cikin bakina.
“Wani abu kika sha yau?”
“Eh... Na sha bala'i da masifa da wutar da zan amayar maka a yanzu nan idan baka sake ni ba”
“Na sake ki kamar yaya me yake damunki?”
“Kai ne kai kake damuna Abdullahi, na tsane ka, damba marar tunani dan duniya wulakantacce, barikin ta wuce waje har sai ta shigo cikin gidana? Sai ka hurumina da yar'uwata?”
“Kina da hankali kuwa? Ni kike kira damba...”
Ya daga hannu zai mare ni, a nan Allah ya ba ni iko da karfin iya rike hannun da dukanin karfina.
“Maci amana, karka sake tsinanen hannunka ya kai ga halattaciyar fuskata ma ci amana ka bi yaya ka bi kanwarta, haihuwar hasara”
“Okay ta kwashe karya da gaskiya ta fada miki kin zo kina zargina da abun da ban aikata ba ko? Saboda tsaurin ido har ki kalleni kina kirana da suna kala kala ko? Ni fa mijinki Noor”
Na tofa masa yawu a fuska.
“Allah ya kiyaye Allah ya kiyaye yanzu kam, da can amman ban da yanzu”
“Okay rashin kunya zaki nuna min ko? To sai na ga idan akwai uban da ya isa ya saka na sake ki, kuma kika sake fada min wata maganar banza sai na ci ubanki yanzu nan”
“Ubana yayi maka yawa, kuma babu wanda zai saka kaka kai zaka sake ni dan kanka, wato kai da yake namiji mai karfin hali dan duniya har kana da bakin yakata ko? Taya zaka ba ni maganin bachi ka tafi ko wane dare ka kwanta da yar'uwata sai asuba ka dawo ku ci amanata a tare kuma ka ce ba zaka sake ni ba? Wallahi karya kake Abdullahi”
Ya nuna kansa yana murje ido kamar da gaske be aikata ba.
“Ni nake saka miki maganin bachi?”
“Aa ni nake sakawa kaina, wanda ka ba ni jiya ya zube ban sha ba, ina kallon lokacin da ka tashi daga dakin nan ka tafi dakin Hana, na labe na ji abun da kuke magana a kai, har ciki za ku zubar”
Na fashe da kuka domin ba ni da wani abun yi a yanzu kamar shi.
“Ba laifinka ba ne, laifin yar'uwata ne ita da ta ci amanata, dama kum jira wata kila gurin haihu zan mutu ai sai ka aureta ku zauna”
“Innalillahi Wa'Inna Ilaihirraji'un”
Ya sassauta muryarsa.
“Noor Wallahi aikin sheidan ne, kuskure ne aka samu, me Hana ta fada miki?”
“Ban saurareta ba, kamar yadda ba zan saurareka ba, saki kawai nake so ka sake ni”
“Ni ba zan sake ki ba Ina son ki Noor shedan ne Wallahi”
Kalmar ina son ki ta saka na ji kamar da wuka a kusa na daka masa a sautin zuciya. Ya matso kusa da ni
“Abu ne da zamu tsaya mu rufawa juna asiri, ita yar'uwarki ce ni kuma mijinki ne, kuma ga cikina a jikinki Noor, Wallahi na miki alkawari ba zan sake ba”
“Gobe zan tafi na bar muku gidan, ku cigaba da aikata abun da kuke har mahadi ya bayyana, ni dai ka sake ni”
“Ba zan sake ki ba Noor ni ba zan sake ki ba, ni ban taba aikata komai ba sai a wannan karon da Allah ya kawo tsautsayi”
“Karya kake, ba wannan ne karon farko ba Wallahi kawai dai ban gane ba sai yanzu, shiyasa tun kamin ka aure ni kake ta taba ni, da na yi magana ka ce gwada ni kake yi, ashe gwadawa kake ka gani idan ni yar iska ce na amince maka a waje, ka gama da ni ka tafi, da hakan be samu sai ka bijiro da maganar aure, da na samu ciki kuma sai na daina burge ka saboda ba auren Allah ba ne, auren sha'awa ka yi min. Sai kuma sha'awarka ta koma gurin kanwata jinina, ita kuma bata duba alaka ba ta yarda kuka taru kuka ci amanata”
Na dafe zuciyata ina bakincin da ban fahimci wannan red flag din ba tun farko, ga kuma Safeena ma ai izina ce.
Ya dafe kansa ya juya ya juyo ya fara safa da marwa kamin ya samu tsayawa gabana a rikece har da fashe min da kuka.
“Dan Allah ki kwantar da hankalinki mu yi magana ta fahimta, sakinki zai bata abubuwa ne kawai, ina zaki je da ciki? Abun nan aikin shaidan ne Noor zai iya fadawa kan kowa, zan tafi na bar miki gidan har hankalinki ya kwanta amman ni ba zan sake ki ba”
A take kukan ya yanke min.
“Ba zaka sake ni ba saboda kana tsoron kar a tambayi dalilin mutuwar na fadi cewar kai da yar'uwata kuka ci amanata?”
Yayi kamar be ji ba dauki wayarsa yana kuka zai fice dakin.
“Ba zaka sake ni ba, sai na hada maka cewar dan da Safeena ta haifa maka yanzu ba jininka ba ne, ďan falkanta ne, ex-boyfriend dinta? Sai na fada maka dalilin da ya saka Safeena ta daina daga maka hankali akan aurena? Sai na fada maka na san Safeena irin wanin da baka yi mata ba? Sai na fada maka a duk lokacin da ka bar Kano tana tarayya da Ex dinta ne har sai ka dawo? Sai na fada maka Safeena ta taba ji min ciwo a hannu saboda ta yi tunanin Ex dinta kuma falkamta so na yake, saboda kishinsa?”
Ya juyo ya kalleni kukan da yake ya tsaya.
“Kina cikin bachin rai ne, zaki iya fadar komai Noor na sani”
“Ina cikin bacin rai, amman ba cikin gushewar hankali ba, idan baka yarda ba ka dauki yaron ka gwada jininsa da naka mana, ka cancanci haka ai, daman shege sai dan iska, a da har mamakin dalilin Safeena nake na aikata haka, ashe ta yi daidaita kai din tsohon shege ne”
Ya daka min tsawa.
“Ya ishe ki haka yanzu kam ya ishe ki haka? Mace nawa take kama mijinta yana abun da be dace ba amman ta rufa masa asiri a zaune, balle ni da kaddara ce kuma ba ni kadai ba har da yar'uwarki, kusan ma ita ta ja ra'ayi a komai”
“Wallahi ko kai ne dan autan maza na gama zaman aure da kai Abdull, ko ka sake ni ko na daga na kira uwarka a yanzu na fada mata abun da ka aikata da kanwata kuma na tabbatar mata cewar ďan da Safeena take shayarwa a yanzu ba jikanta ba ne? Domin ba jininka ba ne, na yarda idan aka bincika aka tararda tsabanin haka a kai ni kotu, ko dai so kake na kira kanenka da mahaifiyata ma fada musu? Kwanciyar hankalinka ka sake ni, Ba zan fadawa kowa abun da kuka aikata ba ni na bar ku da Allah”
A fusace ya nufi takardar ya dauka yayi rubutu a kai ya jefa min a fuska.
“Ke ce da bakinciki ba ni ba...”
Ya nufi kofa.
“Allah ya raba ni da bakinciki tun da ya raba ni da kai”
Na fashe da kuka mai karfi. Na yi kuka kuka sosai kuka irin na macen da rauni ya mamayeta ta rasa makoma, saki nake so kuma na samu yanzu idan na koma gida me zan fadawa iyayenmu? Na fada cikina ina bakinciki da ban zaba masa uba na gari ba. A dakin na kwana, sai dai bachi be dauke ni ba, bayan ruwa bana shan komai ba, shi kuma tun da ya fita be dawo ba, har garin Allah ya waye.
Cikin kuka da bakinciki na yi sallah Asuba, na roki Allah ya sanyaya min zuciyata ya sanya min saka min kana'a domin har lokacin ban ji zan iya yi ma yar'uwata wata bakar addu'a ba, har gobe ita din jini na ce idan wani abun ya faru da ita kamar ya faru da ni ne. Ni dai na san na barta da Allah shi ya san abun da ya dace da ita kuma shi ya san sakamakon da zai yi min akanta.
Misalin shida da rabi na fara hada kayana cikin akwaiti sai da na yi nisa da hadawa sai kuma, sai kuma na ji bana bukatar kala ko daya domin Abdull ne ya siya, a yanzu kuma bana sha'awar duk wani abu mai alaka da shi. Cikinsa ma da yake jikina da ace zan iya da cire shi zan yi na aje masa a gidansa na yi tafiyata. Jaka kawai na nufa na dauka na hada yan kudadena na dauki wayata ita ma dan ta zame min dole a yanzu.