Sashe 7
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yatsine fuska Asad yake yi ya mayar da idanun sa ya kulle Mama tace, "Aliyu bana son shirme zauna ka daina min shouting a kai na. Wannan halayen naka suna bani mamaki kamar ba jinin sarauta ba." Ba musu ya zauna yana jijjiga kai Mama ta kalli Asad tace, "Ina ruwan ka in ma dafa naman su kazo ka samu yana yi? Ba bayin sa bane?, yana da ikon yi musu duk abinda yake so babu abinda ya shafe ka a ciki, bana son shishshigi Asad dalilin da ya saka bakwa shiri kenan kai da shi."
Asad bai ce komai ba daman kuma itama tasan bazai ce ba tace, "Ku had'a kan ku dan Allah bana son wananan tashin hankalin a tsakanin ku, yadda kuke zaune lafiya da Hydar shima da Aliyun ku zauna lafiya."
Aliyu ya girgiza kai yace, "ki gafarce ni Mama, Ba'a nemi zaman lafiya ba matuk'ar aka bawa Asad mulkin garin nan, Ba'a nemi kwanciyar hankali ba ko kad'an." Mama ta kalle shi a gajiye da magana irin ta tace, "Wai kai Aliyu waye zai baka mulki ne?, baka kwana a gida sai sanda kaga dama, koda yaushe cikin yawon banza kake da shaye-shaye na banza da wofi, a haka za'a baka mulkin ragamar al'uma?. Ka ajjiye wannan tunanin a ranka ka taya d'an uwan ka neman sarauta domin indai yana raye kai baza kayi mulki ba sai shi."
Kallon mahaifiyar tasa yayi da jajayen idanun sa yace, "indai yana raye mahaifiyata tace?."
"Eh indai yana raye baza ka mulki garin nan ba, da ace babu shi ne babu kuma Hydar zan shiga na fita wajan ganin ka zama sarkin garin nan kodan cikar burina, amma kash! Asad ya fika duk wani 'karko da ake nema a wajan wanda za'a bawa mulki dalilin da ya saka mahaifin ku ya furta zai bar masa karagar kenan. Hydar ya fila qualities d'in mulkar garin nan tunda shi rashin lafiya ce kawai kuma sai lokaci zuwa lokaci take tashi kai fa?."
"In kin min izini zanje na kwanta" ya fad'a muryar sa har sark'ewa take sabida bak'in ciki.
"Mu tashi lafiya" ta furta bata kalle shi ba yace, "Godiya nake." Mik'ewa tsaye yayi yana kallon Asad da ba shi yake kallo ba ya lumshe idanun sa kalaman mahaifiyar sa na dawo masa cikin kansa a zuciyar sa sak'a yadda zaiyi da Asad tunda ta furta da dai baya raye ne sai ta san yadda zatayi tabbas zai zama baya rayen kuwa nan kusa, baice komai ba ya girgiza kai ya fita.
Asad ya kalli Maman nasu yace, "in anyi min izini zan tafi na kwanta nima." Da kai tayi masa alama da an bashi ya mik'e sannan ya duk'a yace, "Sai da safe" abinda yace kenan ya mik'e Hydar ma haka suka fita tare.
Tare suke tafiya Hydar yace, "Deaf bana son mulkin nan ya sub'uce daga hannun ka ya koma hannun Aliyu, babu abinda bro bazai iya ba indai a kan sarautar nan ne." Asad ya sauke numfashi kawai baice komai ya kalli Hydar har zaiyi magana sai kuma ya fasa cewa komai ya d'auke kansa.
Murmushi Hydar yayi yace, "ka koyi magana deaf domin nan da wasu kwanaki kad'an zaka zama shugaban wannan gari ba kuma za'ayi shugaba wanda baya magana ba."
"Hydar ya zanyi?!" Ya furta da wata irin murya da ya sanya Hydar kallon sa har lokacin tafiya suke yi yace,
"Kai kad'ai ka cancanta Deaf, in ba kai ba duk wanda aka bawa mulkin nan komai sai ya lalace, kayi hak'uri domin ya zamar maka dole." Bai bashi amsa ba daman shima yasan iyakacin maganar da zai samu kenan hakan ya saka shi jan bakin sa yayi shiru kawai yana kallon sa.
Yana son Asad sosai baya son ganin abinda zai cutar dashi kamar yadda shima yake son sa, yayi alqawarin taya shi yak'i da duk wani mak'iya da suka sako shi a gaba, zai taya shi nemawa kansa kariya a duk inda kariyar take. A haka suka k'arasa babban b'angaren su suka shiga daman sun san baza su samu Aliyu ba kowa ya wuce d'akin sa Hydar yana murmushi ya shiga nasa d'akin.
*☆☆☆*
"Rauda! Zo ki bani kud'in ciniki na, rainin hankali ne ma irin naki kin san ban karb'i kud'ina ba ina ke ina bacci?" Baba ya fad'a da k'arfi a k'ofar d'akin su.
Rauda da bacci ya d'auke ta ta jiyo amon muryar sa ba jimawa ta mik'e tana laluben k'aramar touch light d'in Umma ta d'auko ta kunna tana haska inda zata ga kud'in. Muryar Umma taji tace, "Suna cikin kayan ki kinyi bacci kin barsu shiyasa na b'oye miki."
"Wai baza ki kawo min bane?!" Ya sake fad'a cikin d'aga murya yana d'aga laluben d'akin.
"D'auko maka nake Baba" ta fad'a cikin muryar bacci tana dube ghana must go na kayan ta ta d'auko kud'in a bak'ar leda ta mik'e ta kawo masa ya karb'a ya kwance yana lissfawa, kallon ta yayi yace, "babu naira hamsin tana ina?."
"Fad'uwa tayi Baba."
"Kinci uwar ki keda fad'uwar, kaji min yarinya ni zaki kalla kice kin naira hamsin ta fad'i? Ina laifin ma biyar ta fad'i sai ki yarda har hamsin?."
"Kayi hak'uri Baba wallahi ban sani ba sai bayan na dawo dana irga naga babu."
"Daman ai kin saba, rik'e min canji ba wannan ya zama sabon ki dan kinga ina k'yale ki. Y'ar uwar ki cif ta kawo min kud'ina amma ke da yake bakya son tallah uwar ki ma bata so shine ake rik'e min canji dan nace na daina d'ora miki, to baki isa ba talla yanzu kika fara kuma wallahi sai kin biya ni hamsin d'ina."
Yana fad'a ya saki labulen ya tafi nasa d'akin yana mita. Umma ta kalle ta tace, "ya akayi kika yar masa da kud'i?." Idanun Rauda suke ciko da hawaye tace, "Banyi da niya ba Umma ban san ta fad'i ba wallahi."
"Da safe cikin cinikin alawar madarar da kike yi ki d'auki hamsin ki bashi in b haka ba kin shiga uku."
"To Umma."
"Kwanta sai da safe" komawa tayi ta kwanta tana share hawayen ta. Ko kad'an bata son wannan dabi'ar ta Baba baya d'aga k'afa akan kud'i ko waye kai.
Kamar kullum da asuba duk ya tashe su kowa ya fito sallah bayan an idar aka jira ya shigo kowa ya gaishe shi sannan aka koma aka kwanta. K'arfe bakwai Rauda ta tashi ta tashi Khairi da Khalil suka fara shirin tafiya makaranta ita kuma ta fara gyare-gyaren gidan.
Bata gama aikin ba ta shiga ciki wajan Umman su tace, "Umma gasarar Koko ta k'are gashi su Khalil zasu tafi makaranta."
Umma ta mik'e zaune tace, "bai baku kud'in awarar bane?."
"Bai bayar ba." Umma ta mik'e tace, "to bara naje naji yadda zamuyi dashi." Ta fad'a tana fitowa shima a lokacin Baba ya fito daga d'aki.
Ganin tana nufo shi ya saka yace, "ban kwana da ko sisi ba kar kizo min da maganar kud'i." Umma ta karyar da wuya tace, "ba batun kud'i bane gasara ta k'are ne gashi baka bada kud'in awara ba ga y'an makaranta suna shiri basu ci komai ba."
"Ki tafasa musu ruwa hamsin d'in da nake bin Rauda ku siyo ganyen shayi da sikari su sha su tafi."
"Bak'in shayi Malam? Kar ka manta fa in suka tafi sai azahar ta yaya zasu gane karatu basu k'oshi ba?."
"Kar su gane mana wani ma ai bai sha bak'in shayin ba, tun yaushe nake cewa ki dinga tura su gidan sarki suna karb'o sadakar taliya baki tab'a ba. Ita y'ar uwar ki ai gashi yanzu sun dafa sun ci har sun tafi sun bar naki suna kale."
Umma tace, "yanzu malam kana da kud'in da zaka bamu muci baza ka bayar ba har sai munje karb'o sadaka har gidan sarki? Ka duba nisan dake tsakanin mu mana."
"Ita wacce taje bata san ciwon kanta ba kenan? Da asuba Rahma take tafiya amma ke y'ar ki y'ar gwal ce baza taje ba sai ku zauna haka ni kinga tafiya ta" ya fad'a yana ficewa ya bar Umma a tsaye.
Ummulkhairi ta taso tace, "Umma barshi ba sai munci komai ba ni zan iya dawowa haka in kina da wani abun ki bawa Khalil kawai." Girgiza kai tayi tace, "A'a Ummulkhairi muje ina da naira d'ari biyu ku siyo awara kuci ku tafi." D'aki ta shiga ta d'auko musu Khalil ya siyo musu awara suka ci suka tafi makaranta.
Rauda bayan ta gama aikin gidan tayi wanka shiga wajan mahaifiyar tata ta same ta a zaune tayi tagumi tace, "Umma ki daina saka damuwa a ranki, indai batun abinci ne zan dinga zuwa ina karb'owa sai muje tare da Rahman mu dawo."
"A'a Rauda ban amince da fitar asuba d'in nan ba, ban kuma amince da ki nemo abinda zaki ci da kanki ba Allah bazai hanani abinda zan baku ba in ya hana mu. Kin san bana son rok'o ne ko yawan cewa a bani da y'an uwana duk wanda na tambaya sai ya bani, yanzu ma ina da shinkafa kwano guda da aka aiko min dashi har gida wanke ki dafa canjin awarar da suka kawo ki siyo mai na hamsin yaji na hamsin muci har dare." Da to ta amsa ta mik'e ta tayi abinda mahaifiyarta ta ta saka ta.
Gab da azahar Baba ya dawo ya kwab'e babbar riga ya shiga aikin dafa d'an wake ya gama nan da nan ya kwashe ya lissafa na nawa ne ya zuba masu ya fara kwala musu kira, ita da Rahma suka fito ya kalle su yace, "to gashi nan na naira dubu biyu ne ko waccen ku, wallahi Allah biyar d'ina baza tayi ciwon kai ba." Komawa Rauda tayi ta d'auko hijjabin da tayi sallah ta d'auki abincin ta fita itama Rahma ta fita ba wacce tace kanzil.
Asad bai ce komai ba daman kuma itama tasan bazai ce ba tace, "Ku had'a kan ku dan Allah bana son wananan tashin hankalin a tsakanin ku, yadda kuke zaune lafiya da Hydar shima da Aliyun ku zauna lafiya."
Aliyu ya girgiza kai yace, "ki gafarce ni Mama, Ba'a nemi zaman lafiya ba matuk'ar aka bawa Asad mulkin garin nan, Ba'a nemi kwanciyar hankali ba ko kad'an." Mama ta kalle shi a gajiye da magana irin ta tace, "Wai kai Aliyu waye zai baka mulki ne?, baka kwana a gida sai sanda kaga dama, koda yaushe cikin yawon banza kake da shaye-shaye na banza da wofi, a haka za'a baka mulkin ragamar al'uma?. Ka ajjiye wannan tunanin a ranka ka taya d'an uwan ka neman sarauta domin indai yana raye kai baza kayi mulki ba sai shi."
Kallon mahaifiyar tasa yayi da jajayen idanun sa yace, "indai yana raye mahaifiyata tace?."
"Eh indai yana raye baza ka mulki garin nan ba, da ace babu shi ne babu kuma Hydar zan shiga na fita wajan ganin ka zama sarkin garin nan kodan cikar burina, amma kash! Asad ya fika duk wani 'karko da ake nema a wajan wanda za'a bawa mulki dalilin da ya saka mahaifin ku ya furta zai bar masa karagar kenan. Hydar ya fila qualities d'in mulkar garin nan tunda shi rashin lafiya ce kawai kuma sai lokaci zuwa lokaci take tashi kai fa?."
"In kin min izini zanje na kwanta" ya fad'a muryar sa har sark'ewa take sabida bak'in ciki.
"Mu tashi lafiya" ta furta bata kalle shi ba yace, "Godiya nake." Mik'ewa tsaye yayi yana kallon Asad da ba shi yake kallo ba ya lumshe idanun sa kalaman mahaifiyar sa na dawo masa cikin kansa a zuciyar sa sak'a yadda zaiyi da Asad tunda ta furta da dai baya raye ne sai ta san yadda zatayi tabbas zai zama baya rayen kuwa nan kusa, baice komai ba ya girgiza kai ya fita.
Asad ya kalli Maman nasu yace, "in anyi min izini zan tafi na kwanta nima." Da kai tayi masa alama da an bashi ya mik'e sannan ya duk'a yace, "Sai da safe" abinda yace kenan ya mik'e Hydar ma haka suka fita tare.
Tare suke tafiya Hydar yace, "Deaf bana son mulkin nan ya sub'uce daga hannun ka ya koma hannun Aliyu, babu abinda bro bazai iya ba indai a kan sarautar nan ne." Asad ya sauke numfashi kawai baice komai ya kalli Hydar har zaiyi magana sai kuma ya fasa cewa komai ya d'auke kansa.
Murmushi Hydar yayi yace, "ka koyi magana deaf domin nan da wasu kwanaki kad'an zaka zama shugaban wannan gari ba kuma za'ayi shugaba wanda baya magana ba."
"Hydar ya zanyi?!" Ya furta da wata irin murya da ya sanya Hydar kallon sa har lokacin tafiya suke yi yace,
"Kai kad'ai ka cancanta Deaf, in ba kai ba duk wanda aka bawa mulkin nan komai sai ya lalace, kayi hak'uri domin ya zamar maka dole." Bai bashi amsa ba daman shima yasan iyakacin maganar da zai samu kenan hakan ya saka shi jan bakin sa yayi shiru kawai yana kallon sa.
Yana son Asad sosai baya son ganin abinda zai cutar dashi kamar yadda shima yake son sa, yayi alqawarin taya shi yak'i da duk wani mak'iya da suka sako shi a gaba, zai taya shi nemawa kansa kariya a duk inda kariyar take. A haka suka k'arasa babban b'angaren su suka shiga daman sun san baza su samu Aliyu ba kowa ya wuce d'akin sa Hydar yana murmushi ya shiga nasa d'akin.
*☆☆☆*
"Rauda! Zo ki bani kud'in ciniki na, rainin hankali ne ma irin naki kin san ban karb'i kud'ina ba ina ke ina bacci?" Baba ya fad'a da k'arfi a k'ofar d'akin su.
Rauda da bacci ya d'auke ta ta jiyo amon muryar sa ba jimawa ta mik'e tana laluben k'aramar touch light d'in Umma ta d'auko ta kunna tana haska inda zata ga kud'in. Muryar Umma taji tace, "Suna cikin kayan ki kinyi bacci kin barsu shiyasa na b'oye miki."
"Wai baza ki kawo min bane?!" Ya sake fad'a cikin d'aga murya yana d'aga laluben d'akin.
"D'auko maka nake Baba" ta fad'a cikin muryar bacci tana dube ghana must go na kayan ta ta d'auko kud'in a bak'ar leda ta mik'e ta kawo masa ya karb'a ya kwance yana lissfawa, kallon ta yayi yace, "babu naira hamsin tana ina?."
"Fad'uwa tayi Baba."
"Kinci uwar ki keda fad'uwar, kaji min yarinya ni zaki kalla kice kin naira hamsin ta fad'i? Ina laifin ma biyar ta fad'i sai ki yarda har hamsin?."
"Kayi hak'uri Baba wallahi ban sani ba sai bayan na dawo dana irga naga babu."
"Daman ai kin saba, rik'e min canji ba wannan ya zama sabon ki dan kinga ina k'yale ki. Y'ar uwar ki cif ta kawo min kud'ina amma ke da yake bakya son tallah uwar ki ma bata so shine ake rik'e min canji dan nace na daina d'ora miki, to baki isa ba talla yanzu kika fara kuma wallahi sai kin biya ni hamsin d'ina."
Yana fad'a ya saki labulen ya tafi nasa d'akin yana mita. Umma ta kalle ta tace, "ya akayi kika yar masa da kud'i?." Idanun Rauda suke ciko da hawaye tace, "Banyi da niya ba Umma ban san ta fad'i ba wallahi."
"Da safe cikin cinikin alawar madarar da kike yi ki d'auki hamsin ki bashi in b haka ba kin shiga uku."
"To Umma."
"Kwanta sai da safe" komawa tayi ta kwanta tana share hawayen ta. Ko kad'an bata son wannan dabi'ar ta Baba baya d'aga k'afa akan kud'i ko waye kai.
Kamar kullum da asuba duk ya tashe su kowa ya fito sallah bayan an idar aka jira ya shigo kowa ya gaishe shi sannan aka koma aka kwanta. K'arfe bakwai Rauda ta tashi ta tashi Khairi da Khalil suka fara shirin tafiya makaranta ita kuma ta fara gyare-gyaren gidan.
Bata gama aikin ba ta shiga ciki wajan Umman su tace, "Umma gasarar Koko ta k'are gashi su Khalil zasu tafi makaranta."
Umma ta mik'e zaune tace, "bai baku kud'in awarar bane?."
"Bai bayar ba." Umma ta mik'e tace, "to bara naje naji yadda zamuyi dashi." Ta fad'a tana fitowa shima a lokacin Baba ya fito daga d'aki.
Ganin tana nufo shi ya saka yace, "ban kwana da ko sisi ba kar kizo min da maganar kud'i." Umma ta karyar da wuya tace, "ba batun kud'i bane gasara ta k'are ne gashi baka bada kud'in awara ba ga y'an makaranta suna shiri basu ci komai ba."
"Ki tafasa musu ruwa hamsin d'in da nake bin Rauda ku siyo ganyen shayi da sikari su sha su tafi."
"Bak'in shayi Malam? Kar ka manta fa in suka tafi sai azahar ta yaya zasu gane karatu basu k'oshi ba?."
"Kar su gane mana wani ma ai bai sha bak'in shayin ba, tun yaushe nake cewa ki dinga tura su gidan sarki suna karb'o sadakar taliya baki tab'a ba. Ita y'ar uwar ki ai gashi yanzu sun dafa sun ci har sun tafi sun bar naki suna kale."
Umma tace, "yanzu malam kana da kud'in da zaka bamu muci baza ka bayar ba har sai munje karb'o sadaka har gidan sarki? Ka duba nisan dake tsakanin mu mana."
"Ita wacce taje bata san ciwon kanta ba kenan? Da asuba Rahma take tafiya amma ke y'ar ki y'ar gwal ce baza taje ba sai ku zauna haka ni kinga tafiya ta" ya fad'a yana ficewa ya bar Umma a tsaye.
Ummulkhairi ta taso tace, "Umma barshi ba sai munci komai ba ni zan iya dawowa haka in kina da wani abun ki bawa Khalil kawai." Girgiza kai tayi tace, "A'a Ummulkhairi muje ina da naira d'ari biyu ku siyo awara kuci ku tafi." D'aki ta shiga ta d'auko musu Khalil ya siyo musu awara suka ci suka tafi makaranta.
Rauda bayan ta gama aikin gidan tayi wanka shiga wajan mahaifiyar tata ta same ta a zaune tayi tagumi tace, "Umma ki daina saka damuwa a ranki, indai batun abinci ne zan dinga zuwa ina karb'owa sai muje tare da Rahman mu dawo."
"A'a Rauda ban amince da fitar asuba d'in nan ba, ban kuma amince da ki nemo abinda zaki ci da kanki ba Allah bazai hanani abinda zan baku ba in ya hana mu. Kin san bana son rok'o ne ko yawan cewa a bani da y'an uwana duk wanda na tambaya sai ya bani, yanzu ma ina da shinkafa kwano guda da aka aiko min dashi har gida wanke ki dafa canjin awarar da suka kawo ki siyo mai na hamsin yaji na hamsin muci har dare." Da to ta amsa ta mik'e ta tayi abinda mahaifiyarta ta ta saka ta.
Gab da azahar Baba ya dawo ya kwab'e babbar riga ya shiga aikin dafa d'an wake ya gama nan da nan ya kwashe ya lissafa na nawa ne ya zuba masu ya fara kwala musu kira, ita da Rahma suka fito ya kalle su yace, "to gashi nan na naira dubu biyu ne ko waccen ku, wallahi Allah biyar d'ina baza tayi ciwon kai ba." Komawa Rauda tayi ta d'auko hijjabin da tayi sallah ta d'auki abincin ta fita itama Rahma ta fita ba wacce tace kanzil.