Sashe 33
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata musa ba dan duk jikin ta yayi sanyi dan ta san wanda ya rasu d'in sosai suna gaisawa in sun had'u a gidan su tunda takan je ta gaishe da matar, mik'ewa tayi ta saka hijjabi mara tsayi sosai ta d'auki abin tafiyar ta ta saka takalmi ta fita daga gidan.
Tafiya take a hankali babu ruwan ta da mutane da suke kallon ta dan in ta biye musu sai ta kifa sabida kallo, kasancewar da y'ar tafiya tsakanin su dan sai ka shiga layikan manyan gidaje zaka je gidan ga kuma yanayin tafiyar ta ya saka ta jima a hanya.
Tana dosar layin taga manyan motoci da runfuna an kafa manya-manyan mutane a zaune ana ta fitowa da abinci kamar ba safiya ba.
Daga farkon layin babu mutane sai kayi nisa zaka zo wajan mutanen, tsayawa tayi daga baya tana kallon mutanen tace, "Anya zan k'arasa kuwa? Gwara na koma anjima Khairi ta rako ni." Ganin kamar ana kallo ta sai ta b'uya bayan wata farar mota tana cigaba da yanke hukunci a zuciyar ta wata zuciyar tana taje wata tana ta bari sai anjima.
"Gaskiya komawa zanyi bazan iya wuce mazan nan ni kad'ai ba" ta fad'a tana gyara zaman sandinan ta zata bar wajan.
"Takawar ka lafiya d'an sarki jikan sarki, takawar ka lafiya yarima mai jiran gado, taka a sannu sikari bakai farin banza ba, inuwar kowa kake, dawisu sarkin ado, wallahi in kana wajan ba'a kowa sai kai kad'ai, d'aya kake tamkar da dubu." kirarin da ta jiyo kenan daga bayan ta kafin ta farga har an zo inda take duk sai ta rud'e ganin wanda take jin tsoro masu bulalai a hannun su. Tsawa d'aya daga cikin dogaran da suke take masa baya yayi mata yace, "gafara y'ar talakawa!" Ya fad'a da k'arfin gaske.
Duk sai ta kuma gigicewa tama rasa wacce hanya zata bi zuciyar ta na rawa dan bata k'aunar ganin su ko kad'an gashi bata son tsawa.
"Baza ki matsa bane?!" Aka sake fad'a mata kafin ta dawo hankalin ta. Aliyu face d'in ta yake k'arewa kallo ganin yadda ta rud'e ya kuma tabbatar itace fa ba k'arya idanun sa sukayi masa ba. "You!" Ya furta cike da mamaki yana k'are mata kallo tun daga sama har k'asa kafin ya cize bakin sa yana kallon motar sa wacce yafi so duk duniya tana jikin ta a tsaye har da dafawa.
Sai a sannan ta dawo nutsuwar ta ta danne tsoron da take ciki tayi niyar barin wajan yace, "ke mahaukaciyar banza, ki kiyayi idanu na su sake tozali da k'aramar mummnar fuskar ki. Duk sanda na sake tozali da bak'ar fuskar ki wallahi sai na canja miki kamannin" ya fad'a a kausasahe yana nuna ta da yatsa.
A fusace ta juyo ta zuba masa banzar harara tace, "indai har ni mahaukaciya ce tabbas kai kakana ne a hauka domin a wajan ka na gani na koya, kaine mahaukaci bani ba a zahirance ana ganin yanayin ka an san na mahaukata ne. Baka isa kayi min komai ba kuma wallahi nafi k'arfi wanda ya fika ma balle kai iskar titi" ta fad'a cikin salon rashin kunya tana hararar sa cikin tsana da b'acin rai.
Kafin kace kwabo dogarin bayan ta ya zuba mata bulala a baya ta runtse idanu domin bulalar ta shige ta sosai ta hana idanun ta kuka amma tana jin zugin ta a gadon bayan ta, kallon ta kawai yake da mamaki ya rasa abinda zai mata ya wuce daga b'acin ran da ta jefa zuciyar sa a ciki hakan ya saka shi yin cak yana kallon ta. D'aga hannu yayi zai d'auke ta da mari ganin hakan ya saka ta runtse idanu yaji an rik'e hannun nasa daga baya bayyanar wanda ya rik'e hannun nasa ya sake b'ata masa rai yana kallon sa yace, "Aliyu why?."
Jin shiru ba'a mare ta ba ya saka ta bud'e idanu tana kallon su, gaban ta yayi mummnar fad'uwa ganin sun zamar mata guda biyu hatta kayan jikin su iri d'aya komai nasu sak kwabo da kwabo baka banbance su. Murza idanun ta tayi ta sake kallon su a lokacin da Aliyu ya fizge hannun sa yana fad'in, "look Asad babu abinda ya shafe ka babu wanda ya isa ya hanani ganin waye uban yarinyar nan a kaf duniyar nan, babu wanda ya isa ya hana ni sakawa a sake b'alla mata k'afa."
Asad ya kalle ta itama shi take kallo idanun ta a bud'e yace, "Jeki." Kasa motsawa tayi jin sanyin muryar sa har cikin kwanyar ta ta kasa koda motsi sai kifta idanu da take yi. "Kee y'ar talakawa baki ji abinda yarima yace ba ne!" Aka sake mata tsawar da ta firgita ta har sandar ta guda d'aya ta fad'i.
"Kar ka sake!" Ya fad'a yana d'agawa wanda yayi tsawar tsayan sa tare da had'e fuskar sa. "Tuba nake ranka ya dad'e, Allah ya wuci zuciyar ka" ya fad'a yana zubewa a k'asa dan bai tab'a jin Asad yayi tsawa haka ba tunda suke. Asad ya sake kallon ta baice komai na kamar ta san me yake nufi ta duk'a zata d'auki sandar ta ya kalli dogarin sai ya zabura ya d'auka mik'a mata yana fad'in, "Wuce ki tafi baiwar Allah, Allah ya baki lafiya" ya fad'a a sanyaye yana bata hanya. Da yake babu mutane a wajan da suke masu zaman makokin suna can nesa ba hango su ake ba hakan ya saka babu wanda ya lura da abinda yake faruwa a wajan.
A sanyaye take takawa jikin ta kamar an mata dukan tsiya tana tafiya tana waiwayon su taga d'aya daga cikin su yana ta masifa d'ayan kuma yama bar wajan da alama wanda yake k'okarin dukan nata ne yake fad'a, kallon gaban ta tayi ta cigaba da tafiya gaban ta na fad'uwa matuk'a zata iya rantsewa da Allah bata tab'a ganin y'an biyu masu kama da juna kamar su ba.
K'arar mota taji a baya ta Aliyu ne ya wuce a guje ta sauke numfashi tana bin motar da kallo gaban ta na cigaba da fad'uwa tsoro duk ya mamaye mata zuciya. Tunani take son yi amma ta fi to ta samu waje tukunna ta zauna sai tafi yin tunanin dakyau.
Tafiya take a kan hanyar babu kowa kamar yadda ta biyo tana tafe a hankali tana tunani, zafi bayan ta yake yi mata inda suka dake ta da bulala ta runtse idanun ta sosai har lokacin tana ji zafi sosai.
Asad yana hangon ta yana tawowa a bayan ta a mota a hankali ya rasa me yake d'aukar sa akan yarinyar ya san tabbas tana bashi tausayi amma bayan tausayi yana jin wani abu amma ya kasa fassara meye. Yana ganin ta kamar yarinyar cikin mafarkin sa abinda ya saka bai tabbatar ba sabida har lokacin fuskar ta gabad'aya bata tab'a bayyanar masa a mafarkin nasa ba.
Yana so ya k'arasa ya taimake ta ya kai ta gida amma kuma yana jin zai iya hakan gwara kawai ya k'yale ta.
Waje yaga ta samu ta zauna a kan wani dutse dake kan hanyar tana sauke numfashi alamun ta gaji, tsayawa yayi a motar yana kallon ta zuciyar sa na angiza shi akan yaje ya taimaka mata abar a taimakawa ce. Taka motar yayi yazo kusa da ita ya sauke glass ya kalle ta itama ta kalle shi suka had'a idanu duk sai ta dabarbarce kamar mara gaskiya ta fara kallon gefen ta kamar wacce take neman wani abun da ta ajjiye a wajan. Wani abu take ji mai sanyi yana shiga duk ilahirin jikinta wanda ya kasance bak'o a gare ta shiyasa duk ta dabarbarce jin bak'on yanayi a tare da ita har tana sauke ajiyar zuciya ga bugun da k'irjin ta yake yi.
*Akwai k'ura fan's.*⛹♀️⛹♀️🤸♀️🤣
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*016*
Yarda take jin gaban ta yana fad'uwa shima haka yake ji bai mata magana ba kuma bai d'aga glass d'in motar sama ba balle ya bar wajan yana tsaye har lokacin ko motsi bayayi. kanta ta sunkuyar k'irjin ta na bugawa duf, duf, duf, kamar wacce tayi gudu mai nisan zango tana raba idanu a k'asa tana ji kamar ta tashi ta gudu daga wajan. Ya bud'e baki zai yi magana sai kuma ya fasa ya d'aga glass d'in motar ya ja motar ya bar wajan a guje.
Nannauyar ajiyar zuciya tayi har da dafe k'irji jin ya tafi ta bi motar da kallo har lokacin k'irjin ta bugawa yake yi tace, "Ni Rauda na shiga uku, na d'auko abinda yafi k'arfi na" ta fad'a tana haki har lokacin tana kallon inda motar ta bi.
"Ke kuma zaman me kike a nan?" Aka fad'a daga gefen ta ta kalli inda taji maganart aga Habiba da Walida sai taji dad'i a ranta tana k'okarin mik'ewa suka zo suka kama ta ta mik'e tsaye.
"Bari kawai gidan gaiswar can zan je fa har na shiga layin naga maza shine zan koma gida an jima Khairi ta rako ni." Habiba tace, "Mu ma can zamu je ai yanzu, muje to." Ba musu suka jera suna tafiya a hankali sabida yanayin tafiyar ta. Waiwaye suka ga tana yi suka juya suma suka babu abinda take kallo Walida tace, "Wai me kike nema ne?."
Bata amsa ba suka cigaba da tafiya har suka shiga cikin gidan rasuwar.
Ba jima suka fito bayan sun yi mata gaisuwa sunyi nisa da gidan Walida tace, "Oh yanzu in kin ga an cika a rasuwa to gidan mai kud'i ne an san za'a ci a sha, in iyayen mu suka rasu ko wani namu babu wanda zaki gani amma nan da yake akwai kud'i kalli motoci da maza dan Allah."
Habiba tace, "Ai yanzu daman in kin ga gidan rasuwa ya cika to tabbas akwai wani babban mai kud'i a gidan, ki duba irin abincin dake fitowa dashi fa kamar gidan biki ga kaji ga naman rago ga kuma ruwa da lemo kamar bikin gidan gwamna. Har da gwamna fa akayi jana'iza d'azu."
Tafiya take a hankali babu ruwan ta da mutane da suke kallon ta dan in ta biye musu sai ta kifa sabida kallo, kasancewar da y'ar tafiya tsakanin su dan sai ka shiga layikan manyan gidaje zaka je gidan ga kuma yanayin tafiyar ta ya saka ta jima a hanya.
Tana dosar layin taga manyan motoci da runfuna an kafa manya-manyan mutane a zaune ana ta fitowa da abinci kamar ba safiya ba.
Daga farkon layin babu mutane sai kayi nisa zaka zo wajan mutanen, tsayawa tayi daga baya tana kallon mutanen tace, "Anya zan k'arasa kuwa? Gwara na koma anjima Khairi ta rako ni." Ganin kamar ana kallo ta sai ta b'uya bayan wata farar mota tana cigaba da yanke hukunci a zuciyar ta wata zuciyar tana taje wata tana ta bari sai anjima.
"Gaskiya komawa zanyi bazan iya wuce mazan nan ni kad'ai ba" ta fad'a tana gyara zaman sandinan ta zata bar wajan.
"Takawar ka lafiya d'an sarki jikan sarki, takawar ka lafiya yarima mai jiran gado, taka a sannu sikari bakai farin banza ba, inuwar kowa kake, dawisu sarkin ado, wallahi in kana wajan ba'a kowa sai kai kad'ai, d'aya kake tamkar da dubu." kirarin da ta jiyo kenan daga bayan ta kafin ta farga har an zo inda take duk sai ta rud'e ganin wanda take jin tsoro masu bulalai a hannun su. Tsawa d'aya daga cikin dogaran da suke take masa baya yayi mata yace, "gafara y'ar talakawa!" Ya fad'a da k'arfin gaske.
Duk sai ta kuma gigicewa tama rasa wacce hanya zata bi zuciyar ta na rawa dan bata k'aunar ganin su ko kad'an gashi bata son tsawa.
"Baza ki matsa bane?!" Aka sake fad'a mata kafin ta dawo hankalin ta. Aliyu face d'in ta yake k'arewa kallo ganin yadda ta rud'e ya kuma tabbatar itace fa ba k'arya idanun sa sukayi masa ba. "You!" Ya furta cike da mamaki yana k'are mata kallo tun daga sama har k'asa kafin ya cize bakin sa yana kallon motar sa wacce yafi so duk duniya tana jikin ta a tsaye har da dafawa.
Sai a sannan ta dawo nutsuwar ta ta danne tsoron da take ciki tayi niyar barin wajan yace, "ke mahaukaciyar banza, ki kiyayi idanu na su sake tozali da k'aramar mummnar fuskar ki. Duk sanda na sake tozali da bak'ar fuskar ki wallahi sai na canja miki kamannin" ya fad'a a kausasahe yana nuna ta da yatsa.
A fusace ta juyo ta zuba masa banzar harara tace, "indai har ni mahaukaciya ce tabbas kai kakana ne a hauka domin a wajan ka na gani na koya, kaine mahaukaci bani ba a zahirance ana ganin yanayin ka an san na mahaukata ne. Baka isa kayi min komai ba kuma wallahi nafi k'arfi wanda ya fika ma balle kai iskar titi" ta fad'a cikin salon rashin kunya tana hararar sa cikin tsana da b'acin rai.
Kafin kace kwabo dogarin bayan ta ya zuba mata bulala a baya ta runtse idanu domin bulalar ta shige ta sosai ta hana idanun ta kuka amma tana jin zugin ta a gadon bayan ta, kallon ta kawai yake da mamaki ya rasa abinda zai mata ya wuce daga b'acin ran da ta jefa zuciyar sa a ciki hakan ya saka shi yin cak yana kallon ta. D'aga hannu yayi zai d'auke ta da mari ganin hakan ya saka ta runtse idanu yaji an rik'e hannun nasa daga baya bayyanar wanda ya rik'e hannun nasa ya sake b'ata masa rai yana kallon sa yace, "Aliyu why?."
Jin shiru ba'a mare ta ba ya saka ta bud'e idanu tana kallon su, gaban ta yayi mummnar fad'uwa ganin sun zamar mata guda biyu hatta kayan jikin su iri d'aya komai nasu sak kwabo da kwabo baka banbance su. Murza idanun ta tayi ta sake kallon su a lokacin da Aliyu ya fizge hannun sa yana fad'in, "look Asad babu abinda ya shafe ka babu wanda ya isa ya hanani ganin waye uban yarinyar nan a kaf duniyar nan, babu wanda ya isa ya hana ni sakawa a sake b'alla mata k'afa."
Asad ya kalle ta itama shi take kallo idanun ta a bud'e yace, "Jeki." Kasa motsawa tayi jin sanyin muryar sa har cikin kwanyar ta ta kasa koda motsi sai kifta idanu da take yi. "Kee y'ar talakawa baki ji abinda yarima yace ba ne!" Aka sake mata tsawar da ta firgita ta har sandar ta guda d'aya ta fad'i.
"Kar ka sake!" Ya fad'a yana d'agawa wanda yayi tsawar tsayan sa tare da had'e fuskar sa. "Tuba nake ranka ya dad'e, Allah ya wuci zuciyar ka" ya fad'a yana zubewa a k'asa dan bai tab'a jin Asad yayi tsawa haka ba tunda suke. Asad ya sake kallon ta baice komai na kamar ta san me yake nufi ta duk'a zata d'auki sandar ta ya kalli dogarin sai ya zabura ya d'auka mik'a mata yana fad'in, "Wuce ki tafi baiwar Allah, Allah ya baki lafiya" ya fad'a a sanyaye yana bata hanya. Da yake babu mutane a wajan da suke masu zaman makokin suna can nesa ba hango su ake ba hakan ya saka babu wanda ya lura da abinda yake faruwa a wajan.
A sanyaye take takawa jikin ta kamar an mata dukan tsiya tana tafiya tana waiwayon su taga d'aya daga cikin su yana ta masifa d'ayan kuma yama bar wajan da alama wanda yake k'okarin dukan nata ne yake fad'a, kallon gaban ta tayi ta cigaba da tafiya gaban ta na fad'uwa matuk'a zata iya rantsewa da Allah bata tab'a ganin y'an biyu masu kama da juna kamar su ba.
K'arar mota taji a baya ta Aliyu ne ya wuce a guje ta sauke numfashi tana bin motar da kallo gaban ta na cigaba da fad'uwa tsoro duk ya mamaye mata zuciya. Tunani take son yi amma ta fi to ta samu waje tukunna ta zauna sai tafi yin tunanin dakyau.
Tafiya take a kan hanyar babu kowa kamar yadda ta biyo tana tafe a hankali tana tunani, zafi bayan ta yake yi mata inda suka dake ta da bulala ta runtse idanun ta sosai har lokacin tana ji zafi sosai.
Asad yana hangon ta yana tawowa a bayan ta a mota a hankali ya rasa me yake d'aukar sa akan yarinyar ya san tabbas tana bashi tausayi amma bayan tausayi yana jin wani abu amma ya kasa fassara meye. Yana ganin ta kamar yarinyar cikin mafarkin sa abinda ya saka bai tabbatar ba sabida har lokacin fuskar ta gabad'aya bata tab'a bayyanar masa a mafarkin nasa ba.
Yana so ya k'arasa ya taimake ta ya kai ta gida amma kuma yana jin zai iya hakan gwara kawai ya k'yale ta.
Waje yaga ta samu ta zauna a kan wani dutse dake kan hanyar tana sauke numfashi alamun ta gaji, tsayawa yayi a motar yana kallon ta zuciyar sa na angiza shi akan yaje ya taimaka mata abar a taimakawa ce. Taka motar yayi yazo kusa da ita ya sauke glass ya kalle ta itama ta kalle shi suka had'a idanu duk sai ta dabarbarce kamar mara gaskiya ta fara kallon gefen ta kamar wacce take neman wani abun da ta ajjiye a wajan. Wani abu take ji mai sanyi yana shiga duk ilahirin jikinta wanda ya kasance bak'o a gare ta shiyasa duk ta dabarbarce jin bak'on yanayi a tare da ita har tana sauke ajiyar zuciya ga bugun da k'irjin ta yake yi.
*Akwai k'ura fan's.*⛹♀️⛹♀️🤸♀️🤣
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*016*
Yarda take jin gaban ta yana fad'uwa shima haka yake ji bai mata magana ba kuma bai d'aga glass d'in motar sama ba balle ya bar wajan yana tsaye har lokacin ko motsi bayayi. kanta ta sunkuyar k'irjin ta na bugawa duf, duf, duf, kamar wacce tayi gudu mai nisan zango tana raba idanu a k'asa tana ji kamar ta tashi ta gudu daga wajan. Ya bud'e baki zai yi magana sai kuma ya fasa ya d'aga glass d'in motar ya ja motar ya bar wajan a guje.
Nannauyar ajiyar zuciya tayi har da dafe k'irji jin ya tafi ta bi motar da kallo har lokacin k'irjin ta bugawa yake yi tace, "Ni Rauda na shiga uku, na d'auko abinda yafi k'arfi na" ta fad'a tana haki har lokacin tana kallon inda motar ta bi.
"Ke kuma zaman me kike a nan?" Aka fad'a daga gefen ta ta kalli inda taji maganart aga Habiba da Walida sai taji dad'i a ranta tana k'okarin mik'ewa suka zo suka kama ta ta mik'e tsaye.
"Bari kawai gidan gaiswar can zan je fa har na shiga layin naga maza shine zan koma gida an jima Khairi ta rako ni." Habiba tace, "Mu ma can zamu je ai yanzu, muje to." Ba musu suka jera suna tafiya a hankali sabida yanayin tafiyar ta. Waiwaye suka ga tana yi suka juya suma suka babu abinda take kallo Walida tace, "Wai me kike nema ne?."
Bata amsa ba suka cigaba da tafiya har suka shiga cikin gidan rasuwar.
Ba jima suka fito bayan sun yi mata gaisuwa sunyi nisa da gidan Walida tace, "Oh yanzu in kin ga an cika a rasuwa to gidan mai kud'i ne an san za'a ci a sha, in iyayen mu suka rasu ko wani namu babu wanda zaki gani amma nan da yake akwai kud'i kalli motoci da maza dan Allah."
Habiba tace, "Ai yanzu daman in kin ga gidan rasuwa ya cika to tabbas akwai wani babban mai kud'i a gidan, ki duba irin abincin dake fitowa dashi fa kamar gidan biki ga kaji ga naman rago ga kuma ruwa da lemo kamar bikin gidan gwamna. Har da gwamna fa akayi jana'iza d'azu."