Sashe 24
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A wannan lokacin aka had'a magungunan Rauda da komai nasu aka saka Rauda a ambulance Umma ma ta shiga aka wuce da ita gida. Kafin suje Inna ta gyara d'akin Umma an yiwa Rauda shinfid'a aka shigo da ita a akan gadon aka zaunar da ita aka basu maganin ta suka koma.
Umma ta cire mayafi ta ajjiye tace, "Daman na gaji da zaman asibitin nan, zaman asibiti sai dole." Rauda tayi shiru bata ce komai ba haka kawai take jin haushin wanda ya kad'e ta a ganin ta bai d'auki lafiyar ta da mahimmaci ba tunda ita talaka ce.
Ummulkhairi da Khalil sai dawowa sukayi suka ga su Umma a gida suka dinga murya Umma ta dawo.
K'arfe biyu na rana Baba ya diro gidan ganin k'ofar Umma a bud'e ya saka shi ya lek'a ya gansu a zaune Rauda tace, "Baba sannu da dawowa." Kallon su yake da mamaki kafin yace, "Me kuma ya dawo daku?." Umma tace, "Kud'in wanda ya kad'e tane ya k'are a asibitin kuma bashi da lafiya shiyasa aka dawo damu gida." Baba yaja dogon tsaki yace, "Kai amma ban so hakan ta faru ba, yanzu shikenan bazan kuma ganin sa ya bani wani abun ba? Abin takaici wallahi."
Rauda tabi mahaifin nata da kallo da mamaki kafin ta d'auke kanta Allah ya sani abinda yake yi yana bata takaici kawai dan babu yadda zatayi ne uba uba ne. Juyawa yayi ya fita yana fad'in, "To Rahma a fito." Ba musu Rahma ta fito da hijjabi ya nuna mata kular yace, "gashi nan na dubu uku ne ayi aje a dawo." Da to ta amsa ta d'auki kular ta fita ranta a b'ace.
Inna ta fito daga d'akin ta ta kalle shi tace, "Tsakani da Allah malam nima da nake goya maka baya na gaji da wannan tallan da kake d'orawa yaran nan, ka duba halin da Rauda take ciki ta dalilin talla ni na d'auka zaka saduda sabida hakan amma ko gezau bakai ba."
Kama k'ugu yayi yace, "To uwata kama kunne na zakiyi ki fad'i maganar nafi fahimtar ki sosai." Inna ta d'auke kanta gefe yace, "in ban d'ora musu tallan ba a gida kike so su zauna naita kallon su su ba aure ba ba kuma samari ba?, meye amfanin su in basu yi tallan ba?."
"Abinda kake sakawa suna yi ba shine zai kawo musu miji ba, aure kuma ai lokaci ne in yazo kamar ba'a zauna ba."
"To bazan daina ba, tallah yanzu suka fara siyar da abinci ba ki d'auka yanzu aka fara wallahi sai sunyi. Inda Allah ya bani manyan y'ay'a maza ya za'ayi na saurare su?, haihuwar y'ay'a mata a farko ma ai asara ce."
Umma da take d'aki tace, "Haba malam, da kanka kake furta wannan maganar?, abinda Allah ya baka ne fa kake cewa asara?."
"Asara mana inda wad'anda na aurar suke gidan mazajen su ne y'ay'ana maza da yanzu sune suke taimaka min ko d'awainiyar ku suka d'auke min ai na huta amma duka mata ne kuma suka auri talakawa ba uwar abinda nake mora, su kuma wannan da suke zaune ba miji sai na zuba musu idanu haka kawai ina ciyar dasu a banza bana k'aruwa?."
"Daman hakkin ciyarwa a kanka yake ba kan su ba" Inna ta fad'a tana kallon sa. Yace, "wannan kuma ku kuka jiyo tallah dai yanzu na fara in kunji haushi bakwa so suyi ku dinga ciyar da kan ku kuga zan basu tallah ko bazan basu ba" yana fad'ar hakan ya fita Inna tace, "nidai na gaji da wannan dabi'ar wallahi." Umma bata kuma cewa komai ba balle kuma Rauda da take zaune.
Ba jimawa Yaya Ummi tazo ta fara shiga d'akin Inna ta gaishe ta sannan ta shiga d'akin Umma tana fad'in, "Allah ya taimaka banje can ba kika min waya Umma." Ta fad'a tana zama Umma tace, "Shiyasa na sanar dake ai dan nasan tsaf zaki iya wucewa." Gaisawa sukayi ta kalli Rauda tace, "Sannu Rauda, kin ajjiye k'iba kinyi haske da yake babu inda kike zuwa." Murmushi kawai tayi bata ce komai ba.
"Ni gwara ma da kuka dawo gidan wallahi k'afar taki ai tayi kyau da yake asibitin kud'i ne kamar ba karaya ba."
Umma tace, "haka nace nima wallahi, ai yayi k'ok'ari yaro."
Ledar da ta shigo da ita ta bud'e ta mik'a mata tace, "karb'i kazar hausa ce kici ance ana so masu karaya suci kaza." Karb'a Rauda tayi tace, "Na gode Yaya Ummi, Umma kici." Umma tace, "ki ci k'oshi tukunna, naji dad'i ma dasu Khalil sun tafi islamiyya." Ba musu ta fara ci suna hira sama-sama kawai sai ganin Baba sukayi kamar an cillo sa.
Kafin suce wani abun ya saka hannu a kwanon hannun Rauda ya d'auki k'atuwar b'angare daga cikin kazar ya saka a baki yana fad'in, "Daman sai dana aiyana wani abun kika kawo kika k'unso a leda to Allah yayi da rabona, yaushe rabon da a gamu da kaza?" ya fad'a yana taunawa tare da lumshe idanun sa. Umma takaici kamar me haka take ji amma ya zatayi haka tayi tagumi tayi shiru suma haka ba wanda yace uppan ya cinye ta hannun sa ya kuma d'aukar wata yana ci.
Yace, "Ke Mamana yaushe mijin naki yayi kud'in siyo miki kaza har kika bayar?." Yaya Ummi tace, "ba shine ya siyo ba bashi na karb'o a mak'ota na na dafa mata ganin mai karaya ce, ina yaga halin da zai siyo min kaza Baba?."
Baba yana b'alla k'ashi yace, "yauwa koda naji" ya fad'a yana fita ya sha ruwa ya dauraye hannun sa ya fita. Umma tace, "Allah ya kyauta." Da amin suka amsa kafin Rauda tace, "Amma Yaya meyasa zaki karb'i bashi?."
"Ke k'arya nake ba bashi na karb'a ba wasu y'an kud'i Abban su Islam ya samu ya siyo mana guda uku yace na kawo miki guda d'aya. Kin san halin Baba ina fad'a masa hakan gobe a gidana zaiyi sallama yace masa bashi da kud'in cefane."
Dariya Rauda tayi tace, "kinyi farar dabara." Umma ma dariya tayi bata ce komai ba Yaya Ummi tace, "ke ai kece a ruwa kika auri wannan yaron Anas ai kun shiga uku da rok'on Baba wallahi." D'aure fuska tayi tace, "nifa bashi zan aura ba Allah zai kawo min miji na."
"Allah ya kawo k'anwa ta burina naga anyi auren ki. Allah ya kawo wanda ya fishing mu sha biki." Da amin suka amsa ta cigaba da cin kazar kafin ta ragewa Umma.
*☆☆☆*
A zaune ya same ta kamar koda yaushe ya k'arasa ya zauna a kan carpet ta kalle shi tace, "tun yaushe nace kaje gidan su Jidda?." Yayi shiru bai amsa ba ta kuma cewa, "ba magana nake maka ba?." Asad yace, "tun kwanaki."
"Sabida ban isa dakai ba ya saka baka je ba kenan ko?." Kai ya girgiza alamun a'a yace, "Tuba nake."
"To me ya hana ka zuwa?."
"Na manta ne."
"Yanzu na tuna maka ai saura ka kuma cemin ka manta. Kunyi waya da mahaifin ka?."
Kai ya d'aga tace, "yaushe zai dawo?."
"Jibi" ya bata amsa a tak'aice yana kallon k'asa. Zatayi magana Aliyu ya shigo cikin k'ananu kaya mara sa tsayi a jikin sa ya mayar da gashin fuskar sa bak'i kamar na Asad daman shine yake banbanta su sai suttura kuma. Shima k'asa ya zauna Mama ta kalle shi tace, "Lafiya na ganka haka?." Ya cize bakin sa har zai magana sai kuma yace, "babu komai."
"Kai dai ka sani" ta fad'a tana kallon Asad kafin tace, "na gama dakai zaka iya tafiya." Ba musu ya mik'e yace, "Ki tashi lafiya" ya fad'a yana fita. Aliyu ya kalle ta yace, "Allah ya taimaki Mamana maganar me naji kuna yi dashi?." Mama tace, "to wanda ya haife ni bani umarni sai na fad'a maka." "Allah ya wuci zuciyar ki, tuba nake. Ki tashi lafiya" ya mik'e yana girgiza kansa ya fita ta bishi da kallo cikin takaici.
Asad yana fita mota ya hau ya tafi company dan akwai abubuwan da dole sai yaje da babu abinda zai kai shi, yana zama a office yaji kansa yayi mugun sarawa ya dafe kan da duka hannu biyu ya kulle idanun sa, "Prince lafiya?" Hafiz ya fad'a yana shigowa. D'ago kai Asad yayi ya kalli Hafiz da ya zauna ya girgiza kai kafin yace, "kaina."
"Sorry."
"Ina files d'in nan?." Hafiz ya mik'e ya kawo masa yana dubawa Hafiz yace, "akwai abinda yake damun ka deaf, tell me please." Baice komai ba ya koma ya jingina da kujera yana sauke ajiyar zuciya amma baice komai ba.
Hafiz yace, "i don't know why yanzu baka sanar dani damuwar ka." Asad yace, "no ba haka bane, babu ne" ya fad'a yana mik'ewa tsaye ya d'auki key da wayar sa yace, "in ka gama ka same ni gida."
"Okay, akwai meeting da kamfanin k'asar Dubai yarjejeniyar suke so a k'ara musu tsahon lokaci."
Asad yace, "Kuyi komai" yana fad'a ya fita Hafiz ya bishi da kallon tausayi gabad'aya ya canja kamar ba shi ba.
Bai koma gida ba yawo yayi tayi a gari bai koma gida ba sai magriba, yana shiga apartment d'in su yaga giftawar mutum kamar iska alamun rashin gaskiya ya dawo da baya ya ganta ta juya baya tana waya ya k'arasa kusa da ita ya tsaya yaji ana cewa, "na saka tun wancan lokacin har yanzu kuma yana cikin d'akin nasa." Juyo da ita taji anyi ta zaro idanu waje shima nasa idanun ya wara ganin wacece ya Bud'e baki yace "Suhaima!."
*Ba'a fara komai ba ku shirya kawai.*
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*012.*
Umma ta cire mayafi ta ajjiye tace, "Daman na gaji da zaman asibitin nan, zaman asibiti sai dole." Rauda tayi shiru bata ce komai ba haka kawai take jin haushin wanda ya kad'e ta a ganin ta bai d'auki lafiyar ta da mahimmaci ba tunda ita talaka ce.
Ummulkhairi da Khalil sai dawowa sukayi suka ga su Umma a gida suka dinga murya Umma ta dawo.
K'arfe biyu na rana Baba ya diro gidan ganin k'ofar Umma a bud'e ya saka shi ya lek'a ya gansu a zaune Rauda tace, "Baba sannu da dawowa." Kallon su yake da mamaki kafin yace, "Me kuma ya dawo daku?." Umma tace, "Kud'in wanda ya kad'e tane ya k'are a asibitin kuma bashi da lafiya shiyasa aka dawo damu gida." Baba yaja dogon tsaki yace, "Kai amma ban so hakan ta faru ba, yanzu shikenan bazan kuma ganin sa ya bani wani abun ba? Abin takaici wallahi."
Rauda tabi mahaifin nata da kallo da mamaki kafin ta d'auke kanta Allah ya sani abinda yake yi yana bata takaici kawai dan babu yadda zatayi ne uba uba ne. Juyawa yayi ya fita yana fad'in, "To Rahma a fito." Ba musu Rahma ta fito da hijjabi ya nuna mata kular yace, "gashi nan na dubu uku ne ayi aje a dawo." Da to ta amsa ta d'auki kular ta fita ranta a b'ace.
Inna ta fito daga d'akin ta ta kalle shi tace, "Tsakani da Allah malam nima da nake goya maka baya na gaji da wannan tallan da kake d'orawa yaran nan, ka duba halin da Rauda take ciki ta dalilin talla ni na d'auka zaka saduda sabida hakan amma ko gezau bakai ba."
Kama k'ugu yayi yace, "To uwata kama kunne na zakiyi ki fad'i maganar nafi fahimtar ki sosai." Inna ta d'auke kanta gefe yace, "in ban d'ora musu tallan ba a gida kike so su zauna naita kallon su su ba aure ba ba kuma samari ba?, meye amfanin su in basu yi tallan ba?."
"Abinda kake sakawa suna yi ba shine zai kawo musu miji ba, aure kuma ai lokaci ne in yazo kamar ba'a zauna ba."
"To bazan daina ba, tallah yanzu suka fara siyar da abinci ba ki d'auka yanzu aka fara wallahi sai sunyi. Inda Allah ya bani manyan y'ay'a maza ya za'ayi na saurare su?, haihuwar y'ay'a mata a farko ma ai asara ce."
Umma da take d'aki tace, "Haba malam, da kanka kake furta wannan maganar?, abinda Allah ya baka ne fa kake cewa asara?."
"Asara mana inda wad'anda na aurar suke gidan mazajen su ne y'ay'ana maza da yanzu sune suke taimaka min ko d'awainiyar ku suka d'auke min ai na huta amma duka mata ne kuma suka auri talakawa ba uwar abinda nake mora, su kuma wannan da suke zaune ba miji sai na zuba musu idanu haka kawai ina ciyar dasu a banza bana k'aruwa?."
"Daman hakkin ciyarwa a kanka yake ba kan su ba" Inna ta fad'a tana kallon sa. Yace, "wannan kuma ku kuka jiyo tallah dai yanzu na fara in kunji haushi bakwa so suyi ku dinga ciyar da kan ku kuga zan basu tallah ko bazan basu ba" yana fad'ar hakan ya fita Inna tace, "nidai na gaji da wannan dabi'ar wallahi." Umma bata kuma cewa komai ba balle kuma Rauda da take zaune.
Ba jimawa Yaya Ummi tazo ta fara shiga d'akin Inna ta gaishe ta sannan ta shiga d'akin Umma tana fad'in, "Allah ya taimaka banje can ba kika min waya Umma." Ta fad'a tana zama Umma tace, "Shiyasa na sanar dake ai dan nasan tsaf zaki iya wucewa." Gaisawa sukayi ta kalli Rauda tace, "Sannu Rauda, kin ajjiye k'iba kinyi haske da yake babu inda kike zuwa." Murmushi kawai tayi bata ce komai ba.
"Ni gwara ma da kuka dawo gidan wallahi k'afar taki ai tayi kyau da yake asibitin kud'i ne kamar ba karaya ba."
Umma tace, "haka nace nima wallahi, ai yayi k'ok'ari yaro."
Ledar da ta shigo da ita ta bud'e ta mik'a mata tace, "karb'i kazar hausa ce kici ance ana so masu karaya suci kaza." Karb'a Rauda tayi tace, "Na gode Yaya Ummi, Umma kici." Umma tace, "ki ci k'oshi tukunna, naji dad'i ma dasu Khalil sun tafi islamiyya." Ba musu ta fara ci suna hira sama-sama kawai sai ganin Baba sukayi kamar an cillo sa.
Kafin suce wani abun ya saka hannu a kwanon hannun Rauda ya d'auki k'atuwar b'angare daga cikin kazar ya saka a baki yana fad'in, "Daman sai dana aiyana wani abun kika kawo kika k'unso a leda to Allah yayi da rabona, yaushe rabon da a gamu da kaza?" ya fad'a yana taunawa tare da lumshe idanun sa. Umma takaici kamar me haka take ji amma ya zatayi haka tayi tagumi tayi shiru suma haka ba wanda yace uppan ya cinye ta hannun sa ya kuma d'aukar wata yana ci.
Yace, "Ke Mamana yaushe mijin naki yayi kud'in siyo miki kaza har kika bayar?." Yaya Ummi tace, "ba shine ya siyo ba bashi na karb'o a mak'ota na na dafa mata ganin mai karaya ce, ina yaga halin da zai siyo min kaza Baba?."
Baba yana b'alla k'ashi yace, "yauwa koda naji" ya fad'a yana fita ya sha ruwa ya dauraye hannun sa ya fita. Umma tace, "Allah ya kyauta." Da amin suka amsa kafin Rauda tace, "Amma Yaya meyasa zaki karb'i bashi?."
"Ke k'arya nake ba bashi na karb'a ba wasu y'an kud'i Abban su Islam ya samu ya siyo mana guda uku yace na kawo miki guda d'aya. Kin san halin Baba ina fad'a masa hakan gobe a gidana zaiyi sallama yace masa bashi da kud'in cefane."
Dariya Rauda tayi tace, "kinyi farar dabara." Umma ma dariya tayi bata ce komai ba Yaya Ummi tace, "ke ai kece a ruwa kika auri wannan yaron Anas ai kun shiga uku da rok'on Baba wallahi." D'aure fuska tayi tace, "nifa bashi zan aura ba Allah zai kawo min miji na."
"Allah ya kawo k'anwa ta burina naga anyi auren ki. Allah ya kawo wanda ya fishing mu sha biki." Da amin suka amsa ta cigaba da cin kazar kafin ta ragewa Umma.
*☆☆☆*
A zaune ya same ta kamar koda yaushe ya k'arasa ya zauna a kan carpet ta kalle shi tace, "tun yaushe nace kaje gidan su Jidda?." Yayi shiru bai amsa ba ta kuma cewa, "ba magana nake maka ba?." Asad yace, "tun kwanaki."
"Sabida ban isa dakai ba ya saka baka je ba kenan ko?." Kai ya girgiza alamun a'a yace, "Tuba nake."
"To me ya hana ka zuwa?."
"Na manta ne."
"Yanzu na tuna maka ai saura ka kuma cemin ka manta. Kunyi waya da mahaifin ka?."
Kai ya d'aga tace, "yaushe zai dawo?."
"Jibi" ya bata amsa a tak'aice yana kallon k'asa. Zatayi magana Aliyu ya shigo cikin k'ananu kaya mara sa tsayi a jikin sa ya mayar da gashin fuskar sa bak'i kamar na Asad daman shine yake banbanta su sai suttura kuma. Shima k'asa ya zauna Mama ta kalle shi tace, "Lafiya na ganka haka?." Ya cize bakin sa har zai magana sai kuma yace, "babu komai."
"Kai dai ka sani" ta fad'a tana kallon Asad kafin tace, "na gama dakai zaka iya tafiya." Ba musu ya mik'e yace, "Ki tashi lafiya" ya fad'a yana fita. Aliyu ya kalle ta yace, "Allah ya taimaki Mamana maganar me naji kuna yi dashi?." Mama tace, "to wanda ya haife ni bani umarni sai na fad'a maka." "Allah ya wuci zuciyar ki, tuba nake. Ki tashi lafiya" ya mik'e yana girgiza kansa ya fita ta bishi da kallo cikin takaici.
Asad yana fita mota ya hau ya tafi company dan akwai abubuwan da dole sai yaje da babu abinda zai kai shi, yana zama a office yaji kansa yayi mugun sarawa ya dafe kan da duka hannu biyu ya kulle idanun sa, "Prince lafiya?" Hafiz ya fad'a yana shigowa. D'ago kai Asad yayi ya kalli Hafiz da ya zauna ya girgiza kai kafin yace, "kaina."
"Sorry."
"Ina files d'in nan?." Hafiz ya mik'e ya kawo masa yana dubawa Hafiz yace, "akwai abinda yake damun ka deaf, tell me please." Baice komai ba ya koma ya jingina da kujera yana sauke ajiyar zuciya amma baice komai ba.
Hafiz yace, "i don't know why yanzu baka sanar dani damuwar ka." Asad yace, "no ba haka bane, babu ne" ya fad'a yana mik'ewa tsaye ya d'auki key da wayar sa yace, "in ka gama ka same ni gida."
"Okay, akwai meeting da kamfanin k'asar Dubai yarjejeniyar suke so a k'ara musu tsahon lokaci."
Asad yace, "Kuyi komai" yana fad'a ya fita Hafiz ya bishi da kallon tausayi gabad'aya ya canja kamar ba shi ba.
Bai koma gida ba yawo yayi tayi a gari bai koma gida ba sai magriba, yana shiga apartment d'in su yaga giftawar mutum kamar iska alamun rashin gaskiya ya dawo da baya ya ganta ta juya baya tana waya ya k'arasa kusa da ita ya tsaya yaji ana cewa, "na saka tun wancan lokacin har yanzu kuma yana cikin d'akin nasa." Juyo da ita taji anyi ta zaro idanu waje shima nasa idanun ya wara ganin wacece ya Bud'e baki yace "Suhaima!."
*Ba'a fara komai ba ku shirya kawai.*
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*012.*