Sashe 10
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rauda kuwa bayan sallar azahar ta dawo unguwar su tana gab da shiga layin su ta had'u da k'awayen ta guda biyu Walida da Habiba suna fitowa ta tsaya tana kallon su tace, "ku kuma ina zuwa da rana haka?." Habiba tace, "Rauda manyan gari ke daga ina kike?."
"Gidan Yaya Ummi naje."
"Gidan sarki zamu je zan raka Habiba karb'o sak'o" Walida ta bata amsa tana kallon ta.
"Sai kun dawo Allah ya kiyaye." Habiba tayi y'ar dariya tace, "banza matsoraciya, kizo muje."
"Ni y'ar gidan baban mu, rufa min asiri babu inda zani."
Walida tace, "ke kuwa kizo muje mana yanzu fa zamu dawo." Ta rausayar da kai tace, "kin san ni tsoron doki nake kuma wannan dogaran bulalar hannu su na bani tsoro wallahi."
Habiba tace, "to ina ruwan ki da doki muda ba turken su zamu je ba?, dogarai kuma ai ba ciki zamu shiga bafa k'ark'arin mu wajan Gwaggo ta sai mu dawo." Rauda tace, "kedai Habiba dan kin saba dasu ne kina zuwa ni kam tsoro nake ji."
Jan hannun ta Walida tayi tace, "Dallah can muje an fad'a miki baza mu shiga ciki ba ko banza kya kashe kwarkwatar idanun ki dan nasan baki tab'a shiga ba."
Haka suka rankaya tafi suna hira Habiba tace, "Wallahi Rauda ke kam matsoraciya ce meye abin tsoro a doki da dogarai?." Dariya tayi kad'an tace, "to abinda baka saba gani ba mana Habiba ai dole naji tsoro, nifa ban tab'a shiga cikin gidan ba tunda nake, zaki ga ko hawan sallah ake bana lek'owa sabida tsoron doki kar yayo kaina."
"Shiyasa muka ce kizo muje ai" Walida ta bata amsa suna cigaba da tafiya. Sun yi tafiya mai d'an nisa kafin suka iso babban gate d'in farko na gidan sarki.
Ganin Rauda zata bayar dasu jiki har ya fara rawa ya saka ta suka rik'o ta suka shiga ciki, gate d'in farko suka fara wucewa na cikin masarautar suna ta tafiya domin da nisa kafin kaje gate na biyu, sun wuce gate na biyu suka zo wajan dokuna zasu wuce Rauda ta tsaya cak a wajan idanun ta na kawo ruwa tana girgiza musu kai, "Habiba tace, "kizo mu wuce Rauda babu abinda zasu yi miki."
Kai take girgizawa tana kallo dokunan tace, "bazan iya ba nidai kuje, bazan iya zuwa ba." Walida ta kalli Habiba Habiba tace, "to ki jira mu a nan zamu je yanzu mu dawo, kar ki motsa." Kai kawai ta d'aga sukayi gaba suna waiwayon ta suka shiga gate na biyu.
Doki d'aya ta gani kamar zai yo kanta ta zabura ta bi wata k'ofa da ta gani a bud'e a guje hawaye yana sakko mata daga idanun ta dan ta tsorata sosai bata son ganin doki ko kad'an hakan ya saka ta gigice har bata ganin abinda yake gabanta hankalin ta ya tafi wajan ganin ta nemi mafaka da zata b'uya. Ba zato babu tsammani tayi karo da mutum kafin ta dawo daidai tasan waye ta bashi hak'uri taji an shararawa fuskar ta mari.........
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023.
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*005.*
Yadda ta gigice idanun ta ya firfito abin tausayi ne jikinta ya tsananta rawa haka hawayen idanun ta suka cigaba da zuba ta kasa koda d'ago kanta balle ma tasan wanda yayi mata kyakykyawan mari haka. A haukace Aliyu yake k'are mata kallo ransa a mugun a b'ace har wuci yake sabida b'acin rai yana binta da banza kallo yace, "Kuna ina!" Ya fad'a cikin murya mai amo har sai da Rauda tayi baya tana rutse idanun ta sabida yadda taji sautin har cikin zuciyar ta.
A guje dogarai guda biyu suka shigo suka zube a k'asa ya bisu da kallon wulaƙanci yace, "wacece wannan?" Ya fad'a yana nuna musu Rauda da take tsaye idanun ta a rufe. Kallon ta sukayi wani daga cikin su yace, "ke y'ar talakawa durk'usa mana!." Jikin Rauda na rawa ta zube guiwa a k'asa jikin ta na rawa sosai duk tsoro ya gama kama mata zuciya. Kallon sa sukayi suka ce, "Allah ya ja zamanin Yarima ban mu santa ba."
Aliyu ya kuma fusata yace, "kenan daman barin wajan kuke babu kowa duk wanda yazo ya shigo sanda ya ga dama?." Su kansu jikin su rawa yake domin tabbas zai iya sakawa a canja musu wajan zama hakan ya saka a tsorace d'aya yace, "tuba muke ranka ya dad'e, Allah ya wuci zuciyar ka, mun amsa kiran Gimbiya ne."
Tunda suka ce gimbiya yasan Mama suke nufi hakan ya saka shi jan dogon tsaki yace, "ku d'auke ta kuje a hukunta ta tunda bata da bakin bada hak'uri" yana fad'a ya juya ya fita daga wajan a fusace.
Har lokacin jikin Rauda rawa yake yi suka mik'e d'aya daga cikin su ya kalle ta yace, "tashi y'ar talakawa yau kin d'ebo ruwan dafa kan ki." Jikin Rauda na rawa ta mik'e har lokacin kuka take ta kasa cewa komai, ba wai tsoron sa take ji ba a'a tsoron doki da kuma masu bulalan nan shine yake sake hargitsa ta. Fitowa sukayi daga wajan daidai nan Habiba da Walida sun fito da alama neman ta suke yi ganin hakan ya saka tawo wajan da sauri Habiba tace, "Allah ya ja zamanin sarkin k'ofa."
"Habiba kin san tane?" Ya fad'a yana kallon ta.
"Na san ta Yallab'ai, k'awa tace rakiya tayi min tana jin tsoron dokuna shiyasa bamu wuce ciki muka ce ta jira mu."
"Ta yiwa yarima Aliyu laifi yana tafiya ta bangaje shi kin kuma san tunda yace ayi mata hukunci babu wanda ya isa ya hana sai mutum biyu kuma basa nan."
Habiba cikin girmamawa ta kuma cewa, "Wallahi Yallab'ai bata tab'a zuwa gidan nan ba yanzun ma nice na jawo ta dan Allah ayi hak'uri a sassauta mata."
"Habiba ba daga ni bane daga shi ne ke kin san halin sa." Zata kuma magana suka hango shi ya tawo lokaci d'aya suka dare hanya yana zuwa zai wuce Habiba tace, "Allah ya ja zamanin yarima mai jiran gado, Allah yayi maka sarkin katagum, Allah yasa ka gaji mai martaba, kaine sarki na goma sha hud'u da izinin Allah. Ranka ya dad'e muna rok'on alfarma, k'awata ce bata tab'a zuwa gidan nan ba sai yau bata san hanyar da zata bi ba, na tabbata kuskure tayi ta shiga inda kake, ina ita ina yarima katagum?, ina ita ina sarkin mu?, ina ita ina shugaban mu baki d'aya?. Ayi mata afuwa ranka ya dad'e" ta fad'a da girmamawa bayan ta zube a k'asa tana tab'a Rauda da har lokacin jikin ta yake bala'in rawa.
"Allah ya wuci zuciyar ka" abinda Rauda ta iya fad'a kenan murya na rawa jikin ta ma na rawa tsoron ta d'aya kar ya saka a kaita wajan doki. Kirarin da Habiba tayi masa ya shige shi hakan ya saka shi ya motsa yatsun sa biyu alamun su tafi kafin yaji ma mai zasu ce ya wuce ciki a abin sa. Wanda yake kusa da sarkin k'ofa ya kalle su yace, "Kinyi sa'a yarinya, maza ku tashi ku tafi kafin ya fito ya canja shawara."
Ai kamar jira suke suka mik'e a guje suka yi hanyar fita Rauda na kuka sosai lokacin Hydar ya fito yaga gift giftwar su fusksr Rauda kawai ya gani tana hawaye daga nan kuma sai suka wuce. D'an lekawa yayi yana kallon su a ransa yana tambayar ko wacece take kuka oho.
Tafiya suke har lokacin Rauda kuka take yi Walida tace, "mune muka ja miki Kiyi hak'uri dan Allah." Habiba tace, "badan mun tilasta ki ba da yanzu babu abinda ya faru, kiyi hak'uri dan Allah ki daina wannan kukan kinga a kan hanya muke fa sai aita kallon ki."
Rauda kuwa ba kukan marin da yayi mata take ba kawai ita a tsorace take ne gani take kamar dokunan zasu biyo ta su kamata. Habiba tace, "kiyi hak'uri haka halin yarima Aliyu yake, bashi da kirki ko kad'an bai d'auki talaka a bakin komai ba ya mayar dasu kamar k'asar da zai taka ya wuce, yadda baya tausayin k'asa yake taka ta da zafin nama haka baya tausayin talaka. Kowa a gidan nan tsoron yi mata laifi yake domin duk tsufan ka koda furfurar ka tana jan k'asa wallahi sai ya saka an maka hukunci. A haka kuma shine zai zama sarkin garin namu."
Walida tace, "mun shiga uku Habiba, akace d'an uwan sa ne."
"Tabd'ijam naki wasa ne Walida, to yadda yake son mulki babu wanda ya isa ya hana shi mulkar garin nan, ke baki ga kirarin da nayi masa bane ya saka ya k'yale Rauda?, ai wallahi da yadda ya furta hukuncin nan sai ya hukunta ta. D'an uwan shine simple babu ruwan sa wallahi kika gan shi baza kice jinin sarauta bane sabida babu abinda ya dame shi, illar kawai shi bashi da lafiyar kwakwalwar in ciwon sa ya tashi sai yayi sati uku a sume."
"Allah sarki abin tausayi, aka ce kuma y'an uku ne."
"Eh uku ne ban tab'a ganin na ukun ba gaskiya kasancewar shi ba mai hayaniya bane ba, ace sai ya kwana ya wuni baice kanzil ba shiyasa ma baya fitowa sabida baya son gaisuwa. Ke kona ganshi bazan banbance su ba."
Walida tace, "tofa lallai."
"Bari kedai, kuma kinga yadda kika ga Aliyun nan haka babar su take ke tama fi Aliyu izza da k'asaita da saka tsinin takalmi ta murtsuke talaka. yar sarki ce kuma jikar sarki ce gata matar sarki, burin ta d'aya tak d'anta yayi sarki kuma zasu yi tunda sune kawai manya y'ay'an mai martaba maza a gidan."
"In sha Allah baza suyi ba, wannan ya zama sarki ai mun shiga uku, taliyar da muke karb'owa kullum ma sai ya saka an daina bamu."
Habiba tace, "kedai ki tsuke baki kawai dan wallahi in kinga yaran nan basu yi mulkin katagum ba sai dai in Allah ne ya nuna ikon sa, dan matar nan da kike gani sai addu'a kawai."
"Allah muka ce ai muma."
Habiba ta kalli Rauda da tayi shiru da alama har lokacin a tsorace take tace, "kiyi hak'uri Rauda dan Allah."
"Gidan Yaya Ummi naje."
"Gidan sarki zamu je zan raka Habiba karb'o sak'o" Walida ta bata amsa tana kallon ta.
"Sai kun dawo Allah ya kiyaye." Habiba tayi y'ar dariya tace, "banza matsoraciya, kizo muje."
"Ni y'ar gidan baban mu, rufa min asiri babu inda zani."
Walida tace, "ke kuwa kizo muje mana yanzu fa zamu dawo." Ta rausayar da kai tace, "kin san ni tsoron doki nake kuma wannan dogaran bulalar hannu su na bani tsoro wallahi."
Habiba tace, "to ina ruwan ki da doki muda ba turken su zamu je ba?, dogarai kuma ai ba ciki zamu shiga bafa k'ark'arin mu wajan Gwaggo ta sai mu dawo." Rauda tace, "kedai Habiba dan kin saba dasu ne kina zuwa ni kam tsoro nake ji."
Jan hannun ta Walida tayi tace, "Dallah can muje an fad'a miki baza mu shiga ciki ba ko banza kya kashe kwarkwatar idanun ki dan nasan baki tab'a shiga ba."
Haka suka rankaya tafi suna hira Habiba tace, "Wallahi Rauda ke kam matsoraciya ce meye abin tsoro a doki da dogarai?." Dariya tayi kad'an tace, "to abinda baka saba gani ba mana Habiba ai dole naji tsoro, nifa ban tab'a shiga cikin gidan ba tunda nake, zaki ga ko hawan sallah ake bana lek'owa sabida tsoron doki kar yayo kaina."
"Shiyasa muka ce kizo muje ai" Walida ta bata amsa suna cigaba da tafiya. Sun yi tafiya mai d'an nisa kafin suka iso babban gate d'in farko na gidan sarki.
Ganin Rauda zata bayar dasu jiki har ya fara rawa ya saka ta suka rik'o ta suka shiga ciki, gate d'in farko suka fara wucewa na cikin masarautar suna ta tafiya domin da nisa kafin kaje gate na biyu, sun wuce gate na biyu suka zo wajan dokuna zasu wuce Rauda ta tsaya cak a wajan idanun ta na kawo ruwa tana girgiza musu kai, "Habiba tace, "kizo mu wuce Rauda babu abinda zasu yi miki."
Kai take girgizawa tana kallo dokunan tace, "bazan iya ba nidai kuje, bazan iya zuwa ba." Walida ta kalli Habiba Habiba tace, "to ki jira mu a nan zamu je yanzu mu dawo, kar ki motsa." Kai kawai ta d'aga sukayi gaba suna waiwayon ta suka shiga gate na biyu.
Doki d'aya ta gani kamar zai yo kanta ta zabura ta bi wata k'ofa da ta gani a bud'e a guje hawaye yana sakko mata daga idanun ta dan ta tsorata sosai bata son ganin doki ko kad'an hakan ya saka ta gigice har bata ganin abinda yake gabanta hankalin ta ya tafi wajan ganin ta nemi mafaka da zata b'uya. Ba zato babu tsammani tayi karo da mutum kafin ta dawo daidai tasan waye ta bashi hak'uri taji an shararawa fuskar ta mari.........
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023.
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*005.*
Yadda ta gigice idanun ta ya firfito abin tausayi ne jikinta ya tsananta rawa haka hawayen idanun ta suka cigaba da zuba ta kasa koda d'ago kanta balle ma tasan wanda yayi mata kyakykyawan mari haka. A haukace Aliyu yake k'are mata kallo ransa a mugun a b'ace har wuci yake sabida b'acin rai yana binta da banza kallo yace, "Kuna ina!" Ya fad'a cikin murya mai amo har sai da Rauda tayi baya tana rutse idanun ta sabida yadda taji sautin har cikin zuciyar ta.
A guje dogarai guda biyu suka shigo suka zube a k'asa ya bisu da kallon wulaƙanci yace, "wacece wannan?" Ya fad'a yana nuna musu Rauda da take tsaye idanun ta a rufe. Kallon ta sukayi wani daga cikin su yace, "ke y'ar talakawa durk'usa mana!." Jikin Rauda na rawa ta zube guiwa a k'asa jikin ta na rawa sosai duk tsoro ya gama kama mata zuciya. Kallon sa sukayi suka ce, "Allah ya ja zamanin Yarima ban mu santa ba."
Aliyu ya kuma fusata yace, "kenan daman barin wajan kuke babu kowa duk wanda yazo ya shigo sanda ya ga dama?." Su kansu jikin su rawa yake domin tabbas zai iya sakawa a canja musu wajan zama hakan ya saka a tsorace d'aya yace, "tuba muke ranka ya dad'e, Allah ya wuci zuciyar ka, mun amsa kiran Gimbiya ne."
Tunda suka ce gimbiya yasan Mama suke nufi hakan ya saka shi jan dogon tsaki yace, "ku d'auke ta kuje a hukunta ta tunda bata da bakin bada hak'uri" yana fad'a ya juya ya fita daga wajan a fusace.
Har lokacin jikin Rauda rawa yake yi suka mik'e d'aya daga cikin su ya kalle ta yace, "tashi y'ar talakawa yau kin d'ebo ruwan dafa kan ki." Jikin Rauda na rawa ta mik'e har lokacin kuka take ta kasa cewa komai, ba wai tsoron sa take ji ba a'a tsoron doki da kuma masu bulalan nan shine yake sake hargitsa ta. Fitowa sukayi daga wajan daidai nan Habiba da Walida sun fito da alama neman ta suke yi ganin hakan ya saka tawo wajan da sauri Habiba tace, "Allah ya ja zamanin sarkin k'ofa."
"Habiba kin san tane?" Ya fad'a yana kallon ta.
"Na san ta Yallab'ai, k'awa tace rakiya tayi min tana jin tsoron dokuna shiyasa bamu wuce ciki muka ce ta jira mu."
"Ta yiwa yarima Aliyu laifi yana tafiya ta bangaje shi kin kuma san tunda yace ayi mata hukunci babu wanda ya isa ya hana sai mutum biyu kuma basa nan."
Habiba cikin girmamawa ta kuma cewa, "Wallahi Yallab'ai bata tab'a zuwa gidan nan ba yanzun ma nice na jawo ta dan Allah ayi hak'uri a sassauta mata."
"Habiba ba daga ni bane daga shi ne ke kin san halin sa." Zata kuma magana suka hango shi ya tawo lokaci d'aya suka dare hanya yana zuwa zai wuce Habiba tace, "Allah ya ja zamanin yarima mai jiran gado, Allah yayi maka sarkin katagum, Allah yasa ka gaji mai martaba, kaine sarki na goma sha hud'u da izinin Allah. Ranka ya dad'e muna rok'on alfarma, k'awata ce bata tab'a zuwa gidan nan ba sai yau bata san hanyar da zata bi ba, na tabbata kuskure tayi ta shiga inda kake, ina ita ina yarima katagum?, ina ita ina sarkin mu?, ina ita ina shugaban mu baki d'aya?. Ayi mata afuwa ranka ya dad'e" ta fad'a da girmamawa bayan ta zube a k'asa tana tab'a Rauda da har lokacin jikin ta yake bala'in rawa.
"Allah ya wuci zuciyar ka" abinda Rauda ta iya fad'a kenan murya na rawa jikin ta ma na rawa tsoron ta d'aya kar ya saka a kaita wajan doki. Kirarin da Habiba tayi masa ya shige shi hakan ya saka shi ya motsa yatsun sa biyu alamun su tafi kafin yaji ma mai zasu ce ya wuce ciki a abin sa. Wanda yake kusa da sarkin k'ofa ya kalle su yace, "Kinyi sa'a yarinya, maza ku tashi ku tafi kafin ya fito ya canja shawara."
Ai kamar jira suke suka mik'e a guje suka yi hanyar fita Rauda na kuka sosai lokacin Hydar ya fito yaga gift giftwar su fusksr Rauda kawai ya gani tana hawaye daga nan kuma sai suka wuce. D'an lekawa yayi yana kallon su a ransa yana tambayar ko wacece take kuka oho.
Tafiya suke har lokacin Rauda kuka take yi Walida tace, "mune muka ja miki Kiyi hak'uri dan Allah." Habiba tace, "badan mun tilasta ki ba da yanzu babu abinda ya faru, kiyi hak'uri dan Allah ki daina wannan kukan kinga a kan hanya muke fa sai aita kallon ki."
Rauda kuwa ba kukan marin da yayi mata take ba kawai ita a tsorace take ne gani take kamar dokunan zasu biyo ta su kamata. Habiba tace, "kiyi hak'uri haka halin yarima Aliyu yake, bashi da kirki ko kad'an bai d'auki talaka a bakin komai ba ya mayar dasu kamar k'asar da zai taka ya wuce, yadda baya tausayin k'asa yake taka ta da zafin nama haka baya tausayin talaka. Kowa a gidan nan tsoron yi mata laifi yake domin duk tsufan ka koda furfurar ka tana jan k'asa wallahi sai ya saka an maka hukunci. A haka kuma shine zai zama sarkin garin namu."
Walida tace, "mun shiga uku Habiba, akace d'an uwan sa ne."
"Tabd'ijam naki wasa ne Walida, to yadda yake son mulki babu wanda ya isa ya hana shi mulkar garin nan, ke baki ga kirarin da nayi masa bane ya saka ya k'yale Rauda?, ai wallahi da yadda ya furta hukuncin nan sai ya hukunta ta. D'an uwan shine simple babu ruwan sa wallahi kika gan shi baza kice jinin sarauta bane sabida babu abinda ya dame shi, illar kawai shi bashi da lafiyar kwakwalwar in ciwon sa ya tashi sai yayi sati uku a sume."
"Allah sarki abin tausayi, aka ce kuma y'an uku ne."
"Eh uku ne ban tab'a ganin na ukun ba gaskiya kasancewar shi ba mai hayaniya bane ba, ace sai ya kwana ya wuni baice kanzil ba shiyasa ma baya fitowa sabida baya son gaisuwa. Ke kona ganshi bazan banbance su ba."
Walida tace, "tofa lallai."
"Bari kedai, kuma kinga yadda kika ga Aliyun nan haka babar su take ke tama fi Aliyu izza da k'asaita da saka tsinin takalmi ta murtsuke talaka. yar sarki ce kuma jikar sarki ce gata matar sarki, burin ta d'aya tak d'anta yayi sarki kuma zasu yi tunda sune kawai manya y'ay'an mai martaba maza a gidan."
"In sha Allah baza suyi ba, wannan ya zama sarki ai mun shiga uku, taliyar da muke karb'owa kullum ma sai ya saka an daina bamu."
Habiba tace, "kedai ki tsuke baki kawai dan wallahi in kinga yaran nan basu yi mulkin katagum ba sai dai in Allah ne ya nuna ikon sa, dan matar nan da kike gani sai addu'a kawai."
"Allah muka ce ai muma."
Habiba ta kalli Rauda da tayi shiru da alama har lokacin a tsorace take tace, "kiyi hak'uri Rauda dan Allah."