Sashe 42
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mai martaba yayi murmushi mai kyau yace, "Shiyasa albarka take baibaiye dakai a koda yaushe, indai nace kar ayi ko tace kar ayi baza kayi koda a bayan idanun mu. Amma tauye ka da take yi yayi yawa nan gaba indai aka kuma zuwa irin wannan gab'ar bazan bari ta tauye ka sai kayi abinda kake so." Shima murmushi Asad d'in yayi yana kallon mahaifin nasa.
"Ya batun yarinyar da take nema maka?." Take fuskar sa ta koma yadda take a d'azu yace, "bata dace dani ba Abba, na sanar da Mama tace ba haka ba ita ta zab'a min, amma na karb'a."
"Da zarar ka samo wacce kake so ko wacece a fad'in duniya ka sanar dani Asad, zan shige maka gaba wajan ganin ka mallake ta ko waye mahaifinta a garin nan ko a k'asar nan."
D'ago idanu yayi suna had'a ido da Abban nasa kwarjini ya saka ya sauke kai k'asa ba tare da ya shirya ba yaji bakin sa yace, "Ko y'ar talakawa ce?."
Mai martaba ya tashi sosai yace, "Ko y'ar wace Asad; shi talaka ba mutum bane? Ko y'ar shugaban k'asa ce indai ba y'ar gidan sarauta bace y'ar talaka ce a gidan sarauta. Indai da tarbiya da ilimin addini zance ya k'are. Inda za'a samu matsala in aka bincika aka gano wata dabi'a a tare da ita ko tare da dangin ta, kasan gida irin wannan baya d'auko irin wannan yaran."
Jin abinda mai margaba yace sai kuma ya rud'e amma bai nuna hakan ba shima mai martaba ya lura bai san yayi maganar ba sai ya murmusa kawai baice komai ba.
"Ina neman izinin tafiya" ya fad'a kai a k'asa. Mai martaba yace, "Dan kada a fad'a min wacece sirikar tawa ya saka zaka gudu?, to Allah ya tashe mu lafiya." Murmushi sosai Asad yayi har hakoran sa suka bayyana yana son zama da mahaifin sa shine yake damuwa da damuwar sa sab'anin Mama da kanta kawai ta sani. Mik'ewa yayi ya fita yana jin sanyi a zuciyar sa.
_Na bayyana a zahiri na a gare ka yau Asad, kayi gaggawar kawo ni rayuwar ka kafin su hallaka, Asad kana da tarin mak'iya na jikin ka sune mak'iyan ka, zanzo gare ka Asad amma akwai tarin qalubale a gaban mu, sai ka jure sai kuma ka daure._ a firgice ya tashi zaune ya dafe kansa abinda ta fad'a masa yana dawo masa cikin kansa, tabbas Rauda ce domin fuskar ta yau ta bayyana sosai a gare shi, itace domin ya ganta ido da ido sosai ta fito tarr itace.
"Meyasa take taimako na tun a mafarki?." Ya tambayi kansa gabad'aya a rud'e yake hankalin sa kuma a matuk'ar tashe.
Agogo ya kalla yaga karfe biyu na dare ya tashi ya shiga band'aki ya d'auro alwala ya fito ya tayar da sallah. Ya jima yana sallah har k'arfe hud'u kafin ya koma lazimi yana zaune har lokacin k'irjin sa bugawa yake yi bai dawo daidai ba. Ana kiran sallah ya tashi ya fita zuwa masallacin cikin gida.
Safiyar asabar yaji gabad'aya babu abinda yake so ya gani ya kuma saka a idanun sa face fuskar Rauda, ya kasa kai komai bakin sa Rauda kawai yake son gani, k'okarin daurewa yake amma abin yaci tura zuciyar sa sake azalzala masa take yi a kan haka dak'yar ya iya zama a gidan bai fita yaje gidan su ba.
Koda ya fita daga gidan Company ya wuce ya tarar da Hafiz suna ta had'a kayan wanda sukayi order za'a kai ya wuce office gabad'aya jikin sa babu k'wari. Bai bar company ba sai yamma wajan cin abinci yaje yaci ya gito ya shiga mota ya nufi unguwar su Rauda kan sa tsaye.
A k'ofar gidan ya tsaya yana kallon gidan nasu amma ya rasa me ya kawo shi sai kallon gidan yake kawai amma ya rasa dalilin da ya kawo shi, hango ta yayi a tsaye da sandinan ta tana dariya ita da wata babbar mace mai shigen maka da ita da alama Yayar tace.
K'arewa mata kallo yake cikin hijjabi mara tsaho fuskar ta a washe da kyakykyawan murmushi a kan fuskar ta, lumshe idanun sa yayi gaban sa na fad'uwa sosai yana kallon ta domin ta k'ara yi masa kyau ga annuri da take fitarwa. Numfashi ya sauke mai nauyi bai daina kallon ta ba bai kuma sauke glass ba har matar da suke tsaye ta bar k'ofar gidan ita kuma koma cikin gidan.
Sai da ta bar wajan ya lumshe ido ya dafe saitin zuciyar sa da take bugawa da sauri ya bud'e ido daidai lokacin da wayar sa ta sake cika masa kunne da ihu, sai da ya dawo hankalin sa ya dawo nutsuwar sa duk da zuciyar sa na bugawa, kallon wayar yayi yaga sunan Mama bai yi k'asa a guiwa ba ya d'auka ya saka a kunne, "Asad ka dawo gida Hydar ya farka!" ta furta daga can b'angaren baice komai ba ya yanke wayar ya tashi motar sa zuwa gida.
_tirkashi fan's mai Asad yake nufi da Rauda ne?._
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*020.*
Lokacin da Asad ya shiga falon Mama ya tarar da Hydar a zaune ya rame sosai yayi haske jikin sa babu k'arfi sai idanu da yake bin mutane dashi, a nutse ya tako ya zauna kusa dashi ya kalli Mama da take zaune itama a gefen sa sai Suhaima da take tsaye yace, "Sannu Hydar, ya kake ji?."
Maganar sa bata fita sosai yace, "da sauk'i."
"Asad ka taimaka masa yayi wanka ya sai yaci abinci." Asad ya kalli Hydar yace, "Zaka iya tashi?." Kai ya d'aga alamun eh ya rik'e shi suka tashi zuwa d'akin da yake kwance. A nan yayi wanka aka kawo masa kaya ya saka yayi sallah ya fara cin abinci. Suna zaune zagaye dashi ya gama cin abincin ya sha magani kana ya kalli Asad yace, "Akwai yarinyar dana buge deaf a tambaya min Dr Yasir tana ina."
Ran Mama ya b'aci jin da abinda ya fad'a tace, "na saka an sallame ta." Hydar ya kalli Mama ya dafe kansa yace, "meyasa Mama? Yarinyar tana buk'atar taimako sai an mata aiki fa."
Mama tace, "kuma indai nice na haife ka dole ka bar maganar ta ba, bana son sake jin zancen wata wacce ka buge a bakin ka ya wuce ka manta da babin ta." Zaiyi magana Asad ya d'an ja rigar sa sai yayi shiru ya saukar da kansa k'asa baice komai ba. Tsaki Mama tayi tace, "kana farkawa ka rasa da abinda zaka tashi sai maganar wata banza y'ar talakawa, kenan daman da ita ka kwanta a ranka da yake baka da hankali, na tsani yarinyar tsana mai muni." Babu wanda ya ce komai ba sukayi shiru zuwa lokacin magariba ta kawo kai.
Tare suka fita da Hydar sai a sannan jama'ar masarautar suka san da farkawar sa aka dinga gaishe shi zai amsa duk da ba wani k'arfi ne dashi ba.
Bayan an idar da sallah suka je wajan mai martaba daga nan suka dawo apartment d'insu. Aliyu baya nan Hydar ya zauna a falo jin jiri yana d'aukar sa yana sauke numfashi yace, "Deaf ban san inda zan ga yarinyar ba, basu da kud'in da za'a yi mata aiki in wani abun ya same ta Allah sai ya saka mata."
"Relax" abinda Asad yace kenan daga nan bai kuma cewa komai ba.
"Deaf ina cikin damuwa tunda na tashi itace tazo raina, ta yaya zan ganta ina so na ganta wallahi."
Wani irin kallo Asad yayi masa jin abinda yace nan take sai gaban sa yayi mugun fad'uwa amma bai nuna masa ba bai kuma yi masa magana ba.
Hydar ya yi shiru amma zuciyar sa gabad'aya tana ga tunanin inda zai ganta gabad'aya hankalin sa yana kanta gashi bai san inda zai nemo ta ba abin duk ya dame shi.
Washe gari Asad tare da Hydar suka fita zuwa company dan ya samu k'arfin jikin sa suna tare har yamma, a yamman aka kawo masa passports d'insu Rauda an buga musu visa ticket ya rage a siya, bayan tafiyar wanda ya kawo passports Hydar ya kalle shi yace, "Passports d'in su waye?." Bai bashi amsa ba sai da ya gama abinda yake yi ya tashi suka shiga mota suka bar company.
Gidan su Rauda ya wuce Hydar bai san gidan ba yaga dai sun tsaya a k'ofar gidan ya kalli Asad yace, "Ina ne nan?."
Bai magana ba ya sauke glass d'in motar nan ya hango Khalil yana ta wasa ya yafito shi da hannu ba musu ya k'araso Asad ya kalle shi yace, "Abban ka yana nan?." Khalil yace, "Eh yana nan."
"Jeka kace ana sallama dashi" yana fad'a ya ja bakin sa yayi shiru Khalil ya shiga cikin gidan.
Hydar yace, "Asad ban gane ina muka zo ba fa." Kallon sa yayi baice masa komai ba a lokacin Baba ya fito ganin haka ya saka Asad ya fito daga motar shima Hydar ganin ya fita shima ya fito lokacin Baba ya k'araso, hango Asad sai ya washe baki ya k'araso da sauri yana zuwa yace, "Barka da zuwa ranka ya dad'e." Murmushin k'arfin hali Asad yayi suka gaisa da Baban Hydar ma ya gaishe shi kafin Asad yace, "Shine Hydar wanda ya buge ta jiya ya farka daga rashin lafiya" ya fad'a yana nuna masa Hydar.
Baba ya washe bakiyace, "Allahu Akbar! Naso na gane fuskar sa yadda ya rame ya saka ban gane shi ba, sannu Hydar ya jikin ka?." Fad'ar hakan nan take sai Hydar ya gane shi shima yace, "Alhamdulillah, ya jikin ta?."
"To jiki da sauk'i dai za'a ce."
"Zan iya ganin ta?" Hydar ya fad'a yana kallon Baba.
"Ya batun yarinyar da take nema maka?." Take fuskar sa ta koma yadda take a d'azu yace, "bata dace dani ba Abba, na sanar da Mama tace ba haka ba ita ta zab'a min, amma na karb'a."
"Da zarar ka samo wacce kake so ko wacece a fad'in duniya ka sanar dani Asad, zan shige maka gaba wajan ganin ka mallake ta ko waye mahaifinta a garin nan ko a k'asar nan."
D'ago idanu yayi suna had'a ido da Abban nasa kwarjini ya saka ya sauke kai k'asa ba tare da ya shirya ba yaji bakin sa yace, "Ko y'ar talakawa ce?."
Mai martaba ya tashi sosai yace, "Ko y'ar wace Asad; shi talaka ba mutum bane? Ko y'ar shugaban k'asa ce indai ba y'ar gidan sarauta bace y'ar talaka ce a gidan sarauta. Indai da tarbiya da ilimin addini zance ya k'are. Inda za'a samu matsala in aka bincika aka gano wata dabi'a a tare da ita ko tare da dangin ta, kasan gida irin wannan baya d'auko irin wannan yaran."
Jin abinda mai margaba yace sai kuma ya rud'e amma bai nuna hakan ba shima mai martaba ya lura bai san yayi maganar ba sai ya murmusa kawai baice komai ba.
"Ina neman izinin tafiya" ya fad'a kai a k'asa. Mai martaba yace, "Dan kada a fad'a min wacece sirikar tawa ya saka zaka gudu?, to Allah ya tashe mu lafiya." Murmushi sosai Asad yayi har hakoran sa suka bayyana yana son zama da mahaifin sa shine yake damuwa da damuwar sa sab'anin Mama da kanta kawai ta sani. Mik'ewa yayi ya fita yana jin sanyi a zuciyar sa.
_Na bayyana a zahiri na a gare ka yau Asad, kayi gaggawar kawo ni rayuwar ka kafin su hallaka, Asad kana da tarin mak'iya na jikin ka sune mak'iyan ka, zanzo gare ka Asad amma akwai tarin qalubale a gaban mu, sai ka jure sai kuma ka daure._ a firgice ya tashi zaune ya dafe kansa abinda ta fad'a masa yana dawo masa cikin kansa, tabbas Rauda ce domin fuskar ta yau ta bayyana sosai a gare shi, itace domin ya ganta ido da ido sosai ta fito tarr itace.
"Meyasa take taimako na tun a mafarki?." Ya tambayi kansa gabad'aya a rud'e yake hankalin sa kuma a matuk'ar tashe.
Agogo ya kalla yaga karfe biyu na dare ya tashi ya shiga band'aki ya d'auro alwala ya fito ya tayar da sallah. Ya jima yana sallah har k'arfe hud'u kafin ya koma lazimi yana zaune har lokacin k'irjin sa bugawa yake yi bai dawo daidai ba. Ana kiran sallah ya tashi ya fita zuwa masallacin cikin gida.
Safiyar asabar yaji gabad'aya babu abinda yake so ya gani ya kuma saka a idanun sa face fuskar Rauda, ya kasa kai komai bakin sa Rauda kawai yake son gani, k'okarin daurewa yake amma abin yaci tura zuciyar sa sake azalzala masa take yi a kan haka dak'yar ya iya zama a gidan bai fita yaje gidan su ba.
Koda ya fita daga gidan Company ya wuce ya tarar da Hafiz suna ta had'a kayan wanda sukayi order za'a kai ya wuce office gabad'aya jikin sa babu k'wari. Bai bar company ba sai yamma wajan cin abinci yaje yaci ya gito ya shiga mota ya nufi unguwar su Rauda kan sa tsaye.
A k'ofar gidan ya tsaya yana kallon gidan nasu amma ya rasa me ya kawo shi sai kallon gidan yake kawai amma ya rasa dalilin da ya kawo shi, hango ta yayi a tsaye da sandinan ta tana dariya ita da wata babbar mace mai shigen maka da ita da alama Yayar tace.
K'arewa mata kallo yake cikin hijjabi mara tsaho fuskar ta a washe da kyakykyawan murmushi a kan fuskar ta, lumshe idanun sa yayi gaban sa na fad'uwa sosai yana kallon ta domin ta k'ara yi masa kyau ga annuri da take fitarwa. Numfashi ya sauke mai nauyi bai daina kallon ta ba bai kuma sauke glass ba har matar da suke tsaye ta bar k'ofar gidan ita kuma koma cikin gidan.
Sai da ta bar wajan ya lumshe ido ya dafe saitin zuciyar sa da take bugawa da sauri ya bud'e ido daidai lokacin da wayar sa ta sake cika masa kunne da ihu, sai da ya dawo hankalin sa ya dawo nutsuwar sa duk da zuciyar sa na bugawa, kallon wayar yayi yaga sunan Mama bai yi k'asa a guiwa ba ya d'auka ya saka a kunne, "Asad ka dawo gida Hydar ya farka!" ta furta daga can b'angaren baice komai ba ya yanke wayar ya tashi motar sa zuwa gida.
_tirkashi fan's mai Asad yake nufi da Rauda ne?._
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*020.*
Lokacin da Asad ya shiga falon Mama ya tarar da Hydar a zaune ya rame sosai yayi haske jikin sa babu k'arfi sai idanu da yake bin mutane dashi, a nutse ya tako ya zauna kusa dashi ya kalli Mama da take zaune itama a gefen sa sai Suhaima da take tsaye yace, "Sannu Hydar, ya kake ji?."
Maganar sa bata fita sosai yace, "da sauk'i."
"Asad ka taimaka masa yayi wanka ya sai yaci abinci." Asad ya kalli Hydar yace, "Zaka iya tashi?." Kai ya d'aga alamun eh ya rik'e shi suka tashi zuwa d'akin da yake kwance. A nan yayi wanka aka kawo masa kaya ya saka yayi sallah ya fara cin abinci. Suna zaune zagaye dashi ya gama cin abincin ya sha magani kana ya kalli Asad yace, "Akwai yarinyar dana buge deaf a tambaya min Dr Yasir tana ina."
Ran Mama ya b'aci jin da abinda ya fad'a tace, "na saka an sallame ta." Hydar ya kalli Mama ya dafe kansa yace, "meyasa Mama? Yarinyar tana buk'atar taimako sai an mata aiki fa."
Mama tace, "kuma indai nice na haife ka dole ka bar maganar ta ba, bana son sake jin zancen wata wacce ka buge a bakin ka ya wuce ka manta da babin ta." Zaiyi magana Asad ya d'an ja rigar sa sai yayi shiru ya saukar da kansa k'asa baice komai ba. Tsaki Mama tayi tace, "kana farkawa ka rasa da abinda zaka tashi sai maganar wata banza y'ar talakawa, kenan daman da ita ka kwanta a ranka da yake baka da hankali, na tsani yarinyar tsana mai muni." Babu wanda ya ce komai ba sukayi shiru zuwa lokacin magariba ta kawo kai.
Tare suka fita da Hydar sai a sannan jama'ar masarautar suka san da farkawar sa aka dinga gaishe shi zai amsa duk da ba wani k'arfi ne dashi ba.
Bayan an idar da sallah suka je wajan mai martaba daga nan suka dawo apartment d'insu. Aliyu baya nan Hydar ya zauna a falo jin jiri yana d'aukar sa yana sauke numfashi yace, "Deaf ban san inda zan ga yarinyar ba, basu da kud'in da za'a yi mata aiki in wani abun ya same ta Allah sai ya saka mata."
"Relax" abinda Asad yace kenan daga nan bai kuma cewa komai ba.
"Deaf ina cikin damuwa tunda na tashi itace tazo raina, ta yaya zan ganta ina so na ganta wallahi."
Wani irin kallo Asad yayi masa jin abinda yace nan take sai gaban sa yayi mugun fad'uwa amma bai nuna masa ba bai kuma yi masa magana ba.
Hydar ya yi shiru amma zuciyar sa gabad'aya tana ga tunanin inda zai ganta gabad'aya hankalin sa yana kanta gashi bai san inda zai nemo ta ba abin duk ya dame shi.
Washe gari Asad tare da Hydar suka fita zuwa company dan ya samu k'arfin jikin sa suna tare har yamma, a yamman aka kawo masa passports d'insu Rauda an buga musu visa ticket ya rage a siya, bayan tafiyar wanda ya kawo passports Hydar ya kalle shi yace, "Passports d'in su waye?." Bai bashi amsa ba sai da ya gama abinda yake yi ya tashi suka shiga mota suka bar company.
Gidan su Rauda ya wuce Hydar bai san gidan ba yaga dai sun tsaya a k'ofar gidan ya kalli Asad yace, "Ina ne nan?."
Bai magana ba ya sauke glass d'in motar nan ya hango Khalil yana ta wasa ya yafito shi da hannu ba musu ya k'araso Asad ya kalle shi yace, "Abban ka yana nan?." Khalil yace, "Eh yana nan."
"Jeka kace ana sallama dashi" yana fad'a ya ja bakin sa yayi shiru Khalil ya shiga cikin gidan.
Hydar yace, "Asad ban gane ina muka zo ba fa." Kallon sa yayi baice masa komai ba a lokacin Baba ya fito ganin haka ya saka Asad ya fito daga motar shima Hydar ganin ya fita shima ya fito lokacin Baba ya k'araso, hango Asad sai ya washe baki ya k'araso da sauri yana zuwa yace, "Barka da zuwa ranka ya dad'e." Murmushin k'arfin hali Asad yayi suka gaisa da Baban Hydar ma ya gaishe shi kafin Asad yace, "Shine Hydar wanda ya buge ta jiya ya farka daga rashin lafiya" ya fad'a yana nuna masa Hydar.
Baba ya washe bakiyace, "Allahu Akbar! Naso na gane fuskar sa yadda ya rame ya saka ban gane shi ba, sannu Hydar ya jikin ka?." Fad'ar hakan nan take sai Hydar ya gane shi shima yace, "Alhamdulillah, ya jikin ta?."
"To jiki da sauk'i dai za'a ce."
"Zan iya ganin ta?" Hydar ya fad'a yana kallon Baba.