Sashe 49
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Dole ki kawar da kai gefe ai domin abinda kika aikata kin san ba abu bane mai kyau, da ace yarinyar nan bata furta ta hak'ura ba wallahil azim ko wanne hukuncin da take so ayi miki sai an miki sai dai hakan ya zama silar bugawar zuciyar ki sabida bak'in ciki. Yarinyar da Hydar ya buge har ta samu matsala a k'afar ta ki saka a kore ta daga asibiti kawai sabida banza ra'ayin ki..? Ke kullum a idanun ki talaka da mai kud'i suna da banbanci, dan ta kasance talaka wannan Allah ne ya k'addara amma d'anki ne yayi silar nakasar ta amma ke ko yaushe tunanin ki daban yake dana kowa. kin kyauta ai abinda kika aikata yayi miki kyau" ya fad'a yana mik'ewa dole ta mik'e Asad ma ya mik'e tsaye.
Ya sake kallon ta yace, "Ko nan gaba kika sake aikata wannan kuskuren Rabi'a sai na saka anyi miki hukuncin da baki tab'a tunani ba, sai na nuna miki talaka daidai yake dake a duniya tunda ke mutum ce shima mutum ne. Ki kuma ji tsoron ranar da zaki je neman alfarma a wajan talaka" ya fad'a da zallar b'acin raina tare dashi.
Tare suka fita da Asad yana kallon irin kallon da take masa take gaban sa ya cigaba da fad'uwa har suka koma b'angaren mai martaba Asad baya tare da nutsuwar sa nutsuwar sa. Ganin hakan ya saka yace, "Kada ka damu Asad zan tsaya maka a wannan karon sai naga ka samu abinda kake so koda ita d'in bata so, bazata cigaba da tauye maka hakki ina kallo ba a wannan karon alqawari nayi maka."
Kamar zaiyi kuka ya kalle shi yace, "Abba amma zatayi fushi dani kuma ni ban saka Hydar ya fad'a maka abinda yake faruwa ba, at least ban tabbatar da abinda nake ji akan yarinyar ba, a janye maganar Abba." Mai martaba ya dafa kafad'ar sa yace, "kana sonta, Asad na tabbatar da kana sonta. itace mace ta farko da saka kanka a cikin lamuran ta, kuma fuskar ta kake gani a mafarkin ka Asad. Akwai tarin alkhairi a zaman ka da ita nayi istikhara akan hakan Allah ya nuna min kaima yana da kyau kayi. Ka bawa zuciyar ka abinda take so kar ka cutar da kanka a wannan lokacin kamar yadda ka saba yi a baya, ka daure ka zama namiji ka Jajirce kar barazanar babar ka ta baka tsoro ka tsaya a akan ra'ayin ka. Shigowar ta rayuwar ka itace zata canja komai Asad, ka rubuta ka ajjiye koda bana raye hakan zata kasance amma dole ka jure, ka ajjiye wannan raguwar zuciyar taka ka zama namiji kamar kowa dan Allah" mai martaba yana gama fad'a yana kallon sa.
Asad kansa yana sunkuye mai martaba ya kuma cewa, "Yau ba gobe ba ina so kaje gidan su yarinyar ka fara yak'in neman amincewatar, tana da ilimin addini babu abinda ban sani ba a kanta. Tana da tarbiyya mai kyau duk da ta kasance kuna da banbanci ta b'angaren matsayi amma itace daidai da kai tunda kana sonta. Ilimin ta da tarbiyyar ta shine ya saka na sake baka goyan baya d'ari bisa dari ta ko wacce fuska bata da aibu haka dangin ta. Ka nemi amincewar ta umarni nake baka Asad." Yana gama fad'ar hakan ya shige ciki ya bar Asad da sanyi jiki dole ya jawo k'afar sa ya nufo b'angaren Mama k'irjin sa na bugawa.
Zagaye take hankalin ta a tashe ita kad'ai fuskar ta har ta fad'a sabida tashin hankalin da k'unar zuciyar da take ciki, jin motsin da taji ya saka ta juyo ta kalle shi ya sunkuyar da kansa k'asa baice komai ba ta gyara tsayuwa ta fuskance shi tace, "Asad kayi gaggawar samun mahaifin ka ka fad'a masa kai ba son yarinyar nan kake ba, ka janye maganar nan tun kafin nayi maka baki Asad" ta fad'a tana nuna shi.
Asad ya sauke numfashi amma baice komai ba ta kuma cewa, "in ma asiri tayi maka zan warware shi amma baza ta tab'a zama mallakin ka ba ko bayan raina, babu kai babu ita tsakanin ka da ita taimako ne bayan shi babu maganar aure Asad!."
Yadda ta d'aga murya ya saka shi runtse idanu zai iya cewa lokaci na farko kenan da Mama ta d'aga murya dan kowa yasan bata d'aga murya in tana magana a ganin ta fad'uwa ne a gare ta ya bud'e a hankali kana yace, "Ina sonta Mama!."
Tassss shine sautin abinda ya sauka a kuncin sa daidai lokacin da kalmar mama ta gama fitowa daga bakin sa. Rai a b'ace take kallon sa tana nuna shi da yatsa da yake tsaye har lokacin tace, "K'arya kake Asad! Baka isa ba ba kuma zaka isa ba. Meye a wajan ta da zaka so ta?, me take dashi?, bak'a, gurguwa, y'ar talakawa, y'ar tallan abinci a kan titi me zaka nema a wajan ta wanda Jidda bata shi?. Meyasa baka son Jidda sai ita?."
Yayi shiru zuciyar sa na zafi rana ta farko kenan da Mama ta d'aga hannu ta mare shi duk sai yaji duniyar tana yi masa zafi komai yana fice masa daga ransa.
"Asad Jidda itace daidai kai mahaifin ta ambassador ne, na zab'e ta sabida ita kanta a k'asan ka take talakar kace dalilin da ya saka ban nemo jinin sarauta irin ka ba dan bana son matar da zaka aura ya zama tana had'a kanta da matsayin ka. Ita ta dace da rayuwar ka ba waccan banzar ba, ka tuna kai d'an sarki ne, wanda ya haifi mahaifin ka sarki ne, wanda ya haifi mahaifiyar ka sarki ne, wanda ya haifi mahaifin mahaifiyar ka sarki ne, kaine kuma sarki mai jiran gado me zakayi da y'ar talaka mara ilimi da wayewa!?."
Ta bugi kujera ta cigaba da fadin, "Kask'anci ne a gare ni da dangi na gabad'aya matuk'ar ka auri yarinyar nan, baza ka aure ta ba indai ina da rai ka ajjiye wannan batun indai kana son farin cikina, in kuma ka dage akan kud'irin ka ka tabbatar min da y'ar talakawa ta fini a wajan ka." ta fad'a tana nuna shi da yatsa idanun ta a waje sabida bala'i da bak'in ciki.
Muryar sa a tausashe kamar ko yaushe yace, "K'addara ce ta had'a ni da ita Mama ba soyayya ba, kece mahaifiyata wacce ta haife ni ta raine ni na tsahon shekaru da dama har gobe take kan bani tarbiyya. Ta yaya zan had'a matsayin ta da nata wacce na tsince ta a sama?, ta yaya zan fifita wata a kanta?. Ki amince min Mama ki yarje min kaddarar da ta had'a ni da ita na d'auke ta tamkar jarabawa ce wacce Allah ya k'addaro min, ki bani dama na amshe ta hannu biyu-biyu na rubuta nayi nasara. Agajin ki nake nema akan komai a wannan gab'ar ma yarjewar ki nake nema. ki duba yanayin da abin yazo ban shirya zuwan sa ba balle nayi rigakafi tun kafin lokacin, K'aunar ta nake ba sonta nake ba, ki amince min a wannan lokacin na gayyato ta zuwa rayuwata" ya k'arasa fad'a yana runtse idanun sa dan shi kansa ji yake kawai maganar na fitowa daga zuciyar sa zuwa kan harshen sa.
K'are masa kallo take cike da dunbin mamaki jin doguwar maganar da ya tsaya yana yi mata akan wata mahaukaciyar yarinya da bata wuce mai bawa doki abinci a gidan su ba, ba k'aramin hasala ta sake yi ba tace, "baka isa ba Asad! wallahil azim baka isa ba, dole a wannan karon ma kaso abinda nake so in ba haka ba zaka jawowa yarinyar bala'i da masifar da baza ta iya fidda kanta ba; zan iya sakawa a kashe ta kuma na kashe banza da wofi kai ka sani, ina tabbatar maka matuk'ar ka bari abinda mai martaba ya fad'a ya tabbata wallahi sai kayi dana sani!."
Idanun sa sunyi jahh sosai sabida tashin hankalin da zuciyar sa take ciki, zai iya rantse da Allah bai tab'a tsintar kansa a yanayi mara dad'i kamar wannan lokacin hatta yanayin fuskar sa ya koma ja. K'asa tayi da murya ta juya masa baya tace, "Yau ni kake fad'awa doguwar magana akan wata banzar mahaukaciyar yarinya ko Asad?, baka tab'a min irin wannan maganar mai tsaho ba sai yau sabida ta fini a wajan ka, ina cewa ga abinda nake so kana cewa kai ba shi kake so ba sabida ita ko Asad....?" ta k'arasa maganar a sanyaye sai kuma ta ta zauna akan kujera tana hawaye.
Ganin hakan hankalin Asad ya tashi ya bita ya zauna a k'asan carpet yace, "Allah ya wuci zuciyar mahaifiyata, ina rok'on mahaifiyata akan tayi hak'uri ta daina zubar da hawaye akan Asad" ya fad'a a sanyaye yana dafa guiwar k'afar ta kamar shima zaiyi kuka.
"Asad kar ka aure ta, bana sonta wallahi na tsane ta kar ka aure ta Asad" ta fad'a tana rik'e hannun sa gam hawaye na zuba a idanun ta.
Kamar zaiyi kukan yake ji zuciyar sa tayi rauni matuk'a tana cigaba da bugawa rana ta farko da Maman sa take kuka a kansa hakan ya saka yace, "Zan iya hak'ura da komai akan Mamana duk k'aunar da nake masa, Allah ya wuci zuciyar ki."
Hydar dake tsaye a bayan su ya shigo yana fad'in, "A karo na farko meyasa Mahaifiyata baza ta amince da ta amince da abinda Asad yake so ba....? ya bar aikin sa da yake buri tun yana yaro sabida Maman sa, ya bar damammaki da yawa a rayuwar sa sabida Mahaifiyar sa abinda Mama take so shi yake yi. Baya son Jidda amma ya amince da ita duk sabida Mama tana so yau kad'ai Mama ya nuna yana son Rauda meyasa mahaifiyar mu bazata amince masa ta bashi goyan baya ba?. Meye aibun ta kawai dan ta kasance ta fito daga jinin talakawa shikenan ba abar so bace ba?. Dan Allah dan annabi ranki ya dad'e a yiwa Asad adalci a karon farko a barshi ya aure ta tunda yana sonta" ya fad'a a sanyaye yana durk'usawa a gaban Mama cikin girmamawa.
Ya sake kallon ta yace, "Ko nan gaba kika sake aikata wannan kuskuren Rabi'a sai na saka anyi miki hukuncin da baki tab'a tunani ba, sai na nuna miki talaka daidai yake dake a duniya tunda ke mutum ce shima mutum ne. Ki kuma ji tsoron ranar da zaki je neman alfarma a wajan talaka" ya fad'a da zallar b'acin raina tare dashi.
Tare suka fita da Asad yana kallon irin kallon da take masa take gaban sa ya cigaba da fad'uwa har suka koma b'angaren mai martaba Asad baya tare da nutsuwar sa nutsuwar sa. Ganin hakan ya saka yace, "Kada ka damu Asad zan tsaya maka a wannan karon sai naga ka samu abinda kake so koda ita d'in bata so, bazata cigaba da tauye maka hakki ina kallo ba a wannan karon alqawari nayi maka."
Kamar zaiyi kuka ya kalle shi yace, "Abba amma zatayi fushi dani kuma ni ban saka Hydar ya fad'a maka abinda yake faruwa ba, at least ban tabbatar da abinda nake ji akan yarinyar ba, a janye maganar Abba." Mai martaba ya dafa kafad'ar sa yace, "kana sonta, Asad na tabbatar da kana sonta. itace mace ta farko da saka kanka a cikin lamuran ta, kuma fuskar ta kake gani a mafarkin ka Asad. Akwai tarin alkhairi a zaman ka da ita nayi istikhara akan hakan Allah ya nuna min kaima yana da kyau kayi. Ka bawa zuciyar ka abinda take so kar ka cutar da kanka a wannan lokacin kamar yadda ka saba yi a baya, ka daure ka zama namiji ka Jajirce kar barazanar babar ka ta baka tsoro ka tsaya a akan ra'ayin ka. Shigowar ta rayuwar ka itace zata canja komai Asad, ka rubuta ka ajjiye koda bana raye hakan zata kasance amma dole ka jure, ka ajjiye wannan raguwar zuciyar taka ka zama namiji kamar kowa dan Allah" mai martaba yana gama fad'a yana kallon sa.
Asad kansa yana sunkuye mai martaba ya kuma cewa, "Yau ba gobe ba ina so kaje gidan su yarinyar ka fara yak'in neman amincewatar, tana da ilimin addini babu abinda ban sani ba a kanta. Tana da tarbiyya mai kyau duk da ta kasance kuna da banbanci ta b'angaren matsayi amma itace daidai da kai tunda kana sonta. Ilimin ta da tarbiyyar ta shine ya saka na sake baka goyan baya d'ari bisa dari ta ko wacce fuska bata da aibu haka dangin ta. Ka nemi amincewar ta umarni nake baka Asad." Yana gama fad'ar hakan ya shige ciki ya bar Asad da sanyi jiki dole ya jawo k'afar sa ya nufo b'angaren Mama k'irjin sa na bugawa.
Zagaye take hankalin ta a tashe ita kad'ai fuskar ta har ta fad'a sabida tashin hankalin da k'unar zuciyar da take ciki, jin motsin da taji ya saka ta juyo ta kalle shi ya sunkuyar da kansa k'asa baice komai ba ta gyara tsayuwa ta fuskance shi tace, "Asad kayi gaggawar samun mahaifin ka ka fad'a masa kai ba son yarinyar nan kake ba, ka janye maganar nan tun kafin nayi maka baki Asad" ta fad'a tana nuna shi.
Asad ya sauke numfashi amma baice komai ba ta kuma cewa, "in ma asiri tayi maka zan warware shi amma baza ta tab'a zama mallakin ka ba ko bayan raina, babu kai babu ita tsakanin ka da ita taimako ne bayan shi babu maganar aure Asad!."
Yadda ta d'aga murya ya saka shi runtse idanu zai iya cewa lokaci na farko kenan da Mama ta d'aga murya dan kowa yasan bata d'aga murya in tana magana a ganin ta fad'uwa ne a gare ta ya bud'e a hankali kana yace, "Ina sonta Mama!."
Tassss shine sautin abinda ya sauka a kuncin sa daidai lokacin da kalmar mama ta gama fitowa daga bakin sa. Rai a b'ace take kallon sa tana nuna shi da yatsa da yake tsaye har lokacin tace, "K'arya kake Asad! Baka isa ba ba kuma zaka isa ba. Meye a wajan ta da zaka so ta?, me take dashi?, bak'a, gurguwa, y'ar talakawa, y'ar tallan abinci a kan titi me zaka nema a wajan ta wanda Jidda bata shi?. Meyasa baka son Jidda sai ita?."
Yayi shiru zuciyar sa na zafi rana ta farko kenan da Mama ta d'aga hannu ta mare shi duk sai yaji duniyar tana yi masa zafi komai yana fice masa daga ransa.
"Asad Jidda itace daidai kai mahaifin ta ambassador ne, na zab'e ta sabida ita kanta a k'asan ka take talakar kace dalilin da ya saka ban nemo jinin sarauta irin ka ba dan bana son matar da zaka aura ya zama tana had'a kanta da matsayin ka. Ita ta dace da rayuwar ka ba waccan banzar ba, ka tuna kai d'an sarki ne, wanda ya haifi mahaifin ka sarki ne, wanda ya haifi mahaifiyar ka sarki ne, wanda ya haifi mahaifin mahaifiyar ka sarki ne, kaine kuma sarki mai jiran gado me zakayi da y'ar talaka mara ilimi da wayewa!?."
Ta bugi kujera ta cigaba da fadin, "Kask'anci ne a gare ni da dangi na gabad'aya matuk'ar ka auri yarinyar nan, baza ka aure ta ba indai ina da rai ka ajjiye wannan batun indai kana son farin cikina, in kuma ka dage akan kud'irin ka ka tabbatar min da y'ar talakawa ta fini a wajan ka." ta fad'a tana nuna shi da yatsa idanun ta a waje sabida bala'i da bak'in ciki.
Muryar sa a tausashe kamar ko yaushe yace, "K'addara ce ta had'a ni da ita Mama ba soyayya ba, kece mahaifiyata wacce ta haife ni ta raine ni na tsahon shekaru da dama har gobe take kan bani tarbiyya. Ta yaya zan had'a matsayin ta da nata wacce na tsince ta a sama?, ta yaya zan fifita wata a kanta?. Ki amince min Mama ki yarje min kaddarar da ta had'a ni da ita na d'auke ta tamkar jarabawa ce wacce Allah ya k'addaro min, ki bani dama na amshe ta hannu biyu-biyu na rubuta nayi nasara. Agajin ki nake nema akan komai a wannan gab'ar ma yarjewar ki nake nema. ki duba yanayin da abin yazo ban shirya zuwan sa ba balle nayi rigakafi tun kafin lokacin, K'aunar ta nake ba sonta nake ba, ki amince min a wannan lokacin na gayyato ta zuwa rayuwata" ya k'arasa fad'a yana runtse idanun sa dan shi kansa ji yake kawai maganar na fitowa daga zuciyar sa zuwa kan harshen sa.
K'are masa kallo take cike da dunbin mamaki jin doguwar maganar da ya tsaya yana yi mata akan wata mahaukaciyar yarinya da bata wuce mai bawa doki abinci a gidan su ba, ba k'aramin hasala ta sake yi ba tace, "baka isa ba Asad! wallahil azim baka isa ba, dole a wannan karon ma kaso abinda nake so in ba haka ba zaka jawowa yarinyar bala'i da masifar da baza ta iya fidda kanta ba; zan iya sakawa a kashe ta kuma na kashe banza da wofi kai ka sani, ina tabbatar maka matuk'ar ka bari abinda mai martaba ya fad'a ya tabbata wallahi sai kayi dana sani!."
Idanun sa sunyi jahh sosai sabida tashin hankalin da zuciyar sa take ciki, zai iya rantse da Allah bai tab'a tsintar kansa a yanayi mara dad'i kamar wannan lokacin hatta yanayin fuskar sa ya koma ja. K'asa tayi da murya ta juya masa baya tace, "Yau ni kake fad'awa doguwar magana akan wata banzar mahaukaciyar yarinya ko Asad?, baka tab'a min irin wannan maganar mai tsaho ba sai yau sabida ta fini a wajan ka, ina cewa ga abinda nake so kana cewa kai ba shi kake so ba sabida ita ko Asad....?" ta k'arasa maganar a sanyaye sai kuma ta ta zauna akan kujera tana hawaye.
Ganin hakan hankalin Asad ya tashi ya bita ya zauna a k'asan carpet yace, "Allah ya wuci zuciyar mahaifiyata, ina rok'on mahaifiyata akan tayi hak'uri ta daina zubar da hawaye akan Asad" ya fad'a a sanyaye yana dafa guiwar k'afar ta kamar shima zaiyi kuka.
"Asad kar ka aure ta, bana sonta wallahi na tsane ta kar ka aure ta Asad" ta fad'a tana rik'e hannun sa gam hawaye na zuba a idanun ta.
Kamar zaiyi kukan yake ji zuciyar sa tayi rauni matuk'a tana cigaba da bugawa rana ta farko da Maman sa take kuka a kansa hakan ya saka yace, "Zan iya hak'ura da komai akan Mamana duk k'aunar da nake masa, Allah ya wuci zuciyar ki."
Hydar dake tsaye a bayan su ya shigo yana fad'in, "A karo na farko meyasa Mahaifiyata baza ta amince da ta amince da abinda Asad yake so ba....? ya bar aikin sa da yake buri tun yana yaro sabida Maman sa, ya bar damammaki da yawa a rayuwar sa sabida Mahaifiyar sa abinda Mama take so shi yake yi. Baya son Jidda amma ya amince da ita duk sabida Mama tana so yau kad'ai Mama ya nuna yana son Rauda meyasa mahaifiyar mu bazata amince masa ta bashi goyan baya ba?. Meye aibun ta kawai dan ta kasance ta fito daga jinin talakawa shikenan ba abar so bace ba?. Dan Allah dan annabi ranki ya dad'e a yiwa Asad adalci a karon farko a barshi ya aure ta tunda yana sonta" ya fad'a a sanyaye yana durk'usawa a gaban Mama cikin girmamawa.