Sashe 23
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai kuma ya mik'e tsaye yana fad'in, "ya kamata na nemo wannan yarinyar" Sai kuma yaja ya tsaya ya kama k'ugu ya fad'a kan kujera ya zauna yana furta, "Oh Asad!" Ya dafe kansa yayi shiru yana sauke numfashi a hankali tunanin yake barin ransa ya runtse idanun sa yana goge fuskar ta mafarki da wacce aka zana masa a hankali suke barin idanun sa yana ajiyar zuciya.
Ya jima a haka sosai har magariba tayi a nan yayi sallah kafin ya mik'e ya d'auki key da wayar ya fita ya shiga mota ya fita daga gidan.
Baiyi gida ba babban company sa ya wuce ya tarar da Hafiz yana ta kai kawo har lokacin ganin sa ya shigo ya saka shi bin bayan sa zuwa office suna zama Hafiz yake cewa, "Asad what happened?." Bai bashi amsa ba yayi shiru ya jawo laptop d'in dake kan table d'in gaban sa yana dannawa. Ganin hakan sai Hafiz ya bar shi ya fita bai jima sosai ba ya fita daga office d'in yaja motar ya fita gabad'aya.
Gida ya wuce kai tsaye wajan Mama ya shiga kasancewar magariba ce bai same ta ba Suhaima take sanar dashi tana d'aki ya shiga wajan Hydar yana nan kamar yadda yake koda yaushe ko hannun sa baya motsawa yayi masa addu'a ya zauna a kan kujera yana kallon sa. A nan ya kwashe lokaci da yawa har i'sha tayi ya fita yayi sallah ya sake dawowa a nan ya ga Mama a wajan Hydar ya k'araso gaban ta ya tsuguna da girmamawa yace, "Barka da dare Mama."
"Ina kaje yau?" Ta tambaye shi ba tare da ta amsa ba. Kallon ta yayi sai kuma ya d'auke idanun sa wannan tun yana ganin wani abu kan tambayar nan da Mama take masa ta ina kaje, ina zaka, me zakayi in ka fita, wa ka tambaya har ya daina ma domin ya saba.
"Naje Abuja" ya bata amsa a tak'aice. Bata ce komai ba tayi jim kafin tace, "yaushe zaka je wajan Jidda kasan dai ita zaka aura ko?." Kallon Maman yayi baice komai ba tace, "in baka ce ba nasan ai ka jini, nan da lokaci kad'an za'a d'aura muku aure ta." Kai ya girgiza kafin yace, "Mamaa......" Sai kuma yayi shirun jin hakan sai tace, "kar kace min baka sonta ko baku dace ba, itace zab'ina ya zamar maka dole ka sota." Kai ya jinjina alamun gamsuwa kafin ya mik'e jikin sa a sab'ule ya fita.
Sallama akayi aka shigo falon ana fad'in, "y'ar sarki, jikar sarki, matar sarki, babar sarki kuma k'anwar sarkin garin Kano in sha Allah." Jin muryar tasan wacece k'anwar mai martaba kenan Rabi'a kaf cikin dangin mai martaba tasu ce tazo d'aya suna shiri sosai ta juya ta kalle ta ta fad'ad'a murmushi tace, "babbar bak'uwa." Murmushi tayi mai sauti itama ta k'araso tana fad'in, "Zaman kujera ya gagare ni ni Rabi in dai har gimbiya na zaune a kai." Kan Mama ya sake fashewa izzar ta ta ninku ta saki murmushin k'asaita tace, "keda kika b'uya ko ganin ki ba'a yi."
"Yanzun ma dole ce ta saka na taso nazo domin naji abubuwa suna ta faruwa marasa dad'in ji." Mama ta sauke numfashi tace, "bari kawai Rabi'a komai yana neman lalace min lokacin da ban shirya ba."
"Shiyasa nazo ai naji ya akayi hakan take faruwa."
"Sharrin Hajiya ne, itace ta bama Asad guba a ganye yaci." Murmushi Tayi tace, "Zata aikata ai, in kince badaqalar da suke yi da waziri kare bazai ci ba. Waziri yayana ne amma bazan b'oye miki ba baya son ki baya son me son ki, kinga dashi da galadima dama kawai suke jira a kan ki su kawar da y'ay'an ki sabida a lalata maki goben ki."
"Na sani takwara, na sani. Duk abinda suke yi a kan idanuna suke yin sa. Nan Suhail fa ya kira Suhaima yana bata wani abu wai ta bawa Asad na tsarin jiki ne, kiji rainin wayo da y'ar uwar sa yake son yin amfani yaga bayan sa." Tace, "shiyasa dana tashi tawowa na biya wajan malamin nan na karb'o garin magani da rubutu, kinga lamarin Aliyu ma wallahi saka masa hannu akayi haka Hydar ma. Asad ya gagare su ne kawai sabida ibadar sa amma shima zasu iya nasara a kansa nan gaba tunda ya kasance mai rauni ta wani fannin."
Mama tace, "ta b'angaren yarda da mutane Asad yana da rauri, ta b'angaren magana Asad yana da rauni. Amma fa wani abun kwantan b'auna yake yi kallon kowa yake kawai bar shi da rashin maganar sa. Amma wani lokacin in yayi wani abun sai ki d'auka Aliyu ne." Mama Rabi tace, "na sani, namijin duniya kenan kallon su yake yi ta wani b'angaren na san da hakan. Ga rubutun da maganin ko wanne da bayanin sa akwai na Asad akwai na Hydar dana Aliyu harda Suhaima."
Mama ta ja ledar kusa da ita tana dubawa tace, "ai yanzu ma zan tashi na shafawa Hydar nasa dan wancan lokacin rubutun da kika kawo aka shafa masa yayi amfani sosai."
"Mai martaba baya aiko da nasa?." Mama tace, "Da kansa yake zuwa ya bashi kin san gidan ya yake baya barin kowa yazo da kansa yake zuwa, shi da Asad kuma kin san ai ba'a jin sirrin su."
"Haka ne. Wai kuwa Rukayya da Sa'adatu sun zo duba Hydar kuwa?." Mama ta tabe baki tace, "Sun zo."
"Ki dai kula da Sa'adatu zata iya goga masa wani abun a hannu ko a k'afa wallahi." Murmushi tayi tace, "na sani fa rasss nake kallonta." Mik'ewa tayi tace, "ranki ya dad'e ki shafa masa zan shiga ciki na dawo." Kai ta girgiza kawai ita kuma ta fita.
*Bayan Kwana biyu.*
Babu abinda ya ragu ta b'angaren harin da ake kawowa Asad bai kuma fasa addu'a ba mafarkin da yake kullum k'aruwa yake, tunda aka zana masa fuskar ta kuma sai ya koma ganin fuskar a mafarkin amma yak'i bari mafarkin yin tasiri a zuciyar sa yana k'ok'arin mantawa dashi koda yaushe. Fuskar ta ta zama masa tamkar hoto a idanun sa da ya kulle sai ya hango ta hakan ya saka yake jin wani iri a zuciyar sa.
Hydar na kwance har lokacin amma an samu cigaba dan zuwa lokacin yana motsawa alamun ya kusa farfad'owa kenan.
A zaune take a babban d'akin ta wanda aka k'awata shi da kayan gado na alfarma waya na hannun ta, kamar wacce aka tunawa ta danna number Dr ta kira shi bata jima tana ringing ba ya d'auka yana fad'in, "Allah ya ja da ran Mama."
"Ka sallami yarinyar nan kuwa ko tana nan?" Bata amsa gaisuwar ba abinda ta fara tambaya kenan. D'an dabarbarcewa yayi kana yace, "Na sallame ta Mama."
"In ka min k'arya na gano gaskiya kai kasan sauran."
"Ba k'arya nake ba tun lokacin na sallame ta."
"Ka kyauta. In Hydar ya farfad'o kasan sometimes yakan manta wasu abubuwan na baya sai daga baya ya tuna in ya manta batun ta koda zai tambaye ka bana so ka sanar dashi kace komai bai faru ba ka gane ko?."
Kamar yana gaban ta ya girgiza kai alamun to kafin yace, "zanyi in sha Allah." Bata kuma cewa komai ba ta yanke wayar yabi wayar da kallo yana sauke numfashi. "Wannan mata masifaffiya ce, ta yaya zan iya sallamar Rauda bayan har yanzu bata ji sauk'i ba?. In kuma na barta ta gano na shiga uku." Tsaki yaja ya mik'e ya tafi d'akin da Raudan take ya same ta a zaune tana karatun alkur'ani a bayyane. kallon ta yake da birgewa domin da wuya yazo ya same ta haka kawai bata karatu ko lazumi.
Sallama yayi ta katse karatun ta kalle shi tace, "Dr shigo mana." Umma da bacci ya fara d'aukar ta ta mik'e zaune ya k'araso ya tsaya yana kallon k'afar tata yace, "Ya k'afar?."
"K'afa da sauk'i yanzu bata min ciwo ai sai dai gajiya da zama." Ya sauke numfashi yace, "Rauda kud'in wanda ya kawo ki asibitin nan ya k'are kuma shima yana kwance babu lafiya tun zuwan sa na k'arshe nan shine na rasa yadda zanyi." Gaban Umma ya fad'i itama Raudan haka ta rufe alkur'anin tace, "To sai mu koma gida."
"Eh ko kuma ku biya kud'in."
Umma da take gefe tace, "mu biya me likita? Ina muka ga wannan halin?, gwara dai mu koma tunda Allah yayi k'afar tayi kyau."
Jikin sa sai yayi sanyi ya sauke numfashi yace, "to in kun shirya zan saka a kai ku a mota sabida k'afar tata kafin kuje ku saka a gyara mata inda zata zauna, zan baku magungunan da zata dinga sha da abubuwan da ya kamata ta cigaba da ci in sun k'are a kuma siya. Kuyi hak'uri dan Allah na rasa yadda zanyi ne."
"Haba likita meye na bada hak'uri? Ai kayi k'ok'ari ko kaine ka buge ta ai sai haka."
Rauda ta tab'e baki tace, "Daman su y'ay'an masu kud'in nan babu abinda suka sani sai kansu, yanzu inda girmamawa ai yaci ace wani nasa yazo ya cigaba da d'aukar nauyi na tunda sune silar komai. Tunda bashi da lafiya an bar maganar daman ba gata ne dani ba sun yiwa banza. Allah wadaran wasu masu kud'in" Rauda ta fad'a a fusace.
Dr yace, "Wallahi Hydar bashi da wannan halin baki ga yadda ya tsaya akan ki ba rashin lafiya ce dashi in ta tashi sai ya kwashe sati uku a sume bai farfad'o ba, yanzu zancen da nake miki tun da yazo nan ciwon ya same sa bai tashi ba har yanzu."
Umma tace, "kai ka biye mata ai likita ai ko iya haka aka tsaya yayi k'ok'ari sosai, wanda in sun buge ka suke guduwa fa su kuma ace musu me?."
"Umma maganar da ta fad'a gaskiya ce ya kamata ace wani nasa ya tsaya, amma da zaku san waye shi ku kuma san abubuwan da suke faruwa da ku kan ku kun tausaya masa shida y'an uwan nasa."
"Allah ya kyauta" Umma ta fad'a.
Ya jima a haka sosai har magariba tayi a nan yayi sallah kafin ya mik'e ya d'auki key da wayar ya fita ya shiga mota ya fita daga gidan.
Baiyi gida ba babban company sa ya wuce ya tarar da Hafiz yana ta kai kawo har lokacin ganin sa ya shigo ya saka shi bin bayan sa zuwa office suna zama Hafiz yake cewa, "Asad what happened?." Bai bashi amsa ba yayi shiru ya jawo laptop d'in dake kan table d'in gaban sa yana dannawa. Ganin hakan sai Hafiz ya bar shi ya fita bai jima sosai ba ya fita daga office d'in yaja motar ya fita gabad'aya.
Gida ya wuce kai tsaye wajan Mama ya shiga kasancewar magariba ce bai same ta ba Suhaima take sanar dashi tana d'aki ya shiga wajan Hydar yana nan kamar yadda yake koda yaushe ko hannun sa baya motsawa yayi masa addu'a ya zauna a kan kujera yana kallon sa. A nan ya kwashe lokaci da yawa har i'sha tayi ya fita yayi sallah ya sake dawowa a nan ya ga Mama a wajan Hydar ya k'araso gaban ta ya tsuguna da girmamawa yace, "Barka da dare Mama."
"Ina kaje yau?" Ta tambaye shi ba tare da ta amsa ba. Kallon ta yayi sai kuma ya d'auke idanun sa wannan tun yana ganin wani abu kan tambayar nan da Mama take masa ta ina kaje, ina zaka, me zakayi in ka fita, wa ka tambaya har ya daina ma domin ya saba.
"Naje Abuja" ya bata amsa a tak'aice. Bata ce komai ba tayi jim kafin tace, "yaushe zaka je wajan Jidda kasan dai ita zaka aura ko?." Kallon Maman yayi baice komai ba tace, "in baka ce ba nasan ai ka jini, nan da lokaci kad'an za'a d'aura muku aure ta." Kai ya girgiza kafin yace, "Mamaa......" Sai kuma yayi shirun jin hakan sai tace, "kar kace min baka sonta ko baku dace ba, itace zab'ina ya zamar maka dole ka sota." Kai ya jinjina alamun gamsuwa kafin ya mik'e jikin sa a sab'ule ya fita.
Sallama akayi aka shigo falon ana fad'in, "y'ar sarki, jikar sarki, matar sarki, babar sarki kuma k'anwar sarkin garin Kano in sha Allah." Jin muryar tasan wacece k'anwar mai martaba kenan Rabi'a kaf cikin dangin mai martaba tasu ce tazo d'aya suna shiri sosai ta juya ta kalle ta ta fad'ad'a murmushi tace, "babbar bak'uwa." Murmushi tayi mai sauti itama ta k'araso tana fad'in, "Zaman kujera ya gagare ni ni Rabi in dai har gimbiya na zaune a kai." Kan Mama ya sake fashewa izzar ta ta ninku ta saki murmushin k'asaita tace, "keda kika b'uya ko ganin ki ba'a yi."
"Yanzun ma dole ce ta saka na taso nazo domin naji abubuwa suna ta faruwa marasa dad'in ji." Mama ta sauke numfashi tace, "bari kawai Rabi'a komai yana neman lalace min lokacin da ban shirya ba."
"Shiyasa nazo ai naji ya akayi hakan take faruwa."
"Sharrin Hajiya ne, itace ta bama Asad guba a ganye yaci." Murmushi Tayi tace, "Zata aikata ai, in kince badaqalar da suke yi da waziri kare bazai ci ba. Waziri yayana ne amma bazan b'oye miki ba baya son ki baya son me son ki, kinga dashi da galadima dama kawai suke jira a kan ki su kawar da y'ay'an ki sabida a lalata maki goben ki."
"Na sani takwara, na sani. Duk abinda suke yi a kan idanuna suke yin sa. Nan Suhail fa ya kira Suhaima yana bata wani abu wai ta bawa Asad na tsarin jiki ne, kiji rainin wayo da y'ar uwar sa yake son yin amfani yaga bayan sa." Tace, "shiyasa dana tashi tawowa na biya wajan malamin nan na karb'o garin magani da rubutu, kinga lamarin Aliyu ma wallahi saka masa hannu akayi haka Hydar ma. Asad ya gagare su ne kawai sabida ibadar sa amma shima zasu iya nasara a kansa nan gaba tunda ya kasance mai rauni ta wani fannin."
Mama tace, "ta b'angaren yarda da mutane Asad yana da rauri, ta b'angaren magana Asad yana da rauni. Amma fa wani abun kwantan b'auna yake yi kallon kowa yake kawai bar shi da rashin maganar sa. Amma wani lokacin in yayi wani abun sai ki d'auka Aliyu ne." Mama Rabi tace, "na sani, namijin duniya kenan kallon su yake yi ta wani b'angaren na san da hakan. Ga rubutun da maganin ko wanne da bayanin sa akwai na Asad akwai na Hydar dana Aliyu harda Suhaima."
Mama ta ja ledar kusa da ita tana dubawa tace, "ai yanzu ma zan tashi na shafawa Hydar nasa dan wancan lokacin rubutun da kika kawo aka shafa masa yayi amfani sosai."
"Mai martaba baya aiko da nasa?." Mama tace, "Da kansa yake zuwa ya bashi kin san gidan ya yake baya barin kowa yazo da kansa yake zuwa, shi da Asad kuma kin san ai ba'a jin sirrin su."
"Haka ne. Wai kuwa Rukayya da Sa'adatu sun zo duba Hydar kuwa?." Mama ta tabe baki tace, "Sun zo."
"Ki dai kula da Sa'adatu zata iya goga masa wani abun a hannu ko a k'afa wallahi." Murmushi tayi tace, "na sani fa rasss nake kallonta." Mik'ewa tayi tace, "ranki ya dad'e ki shafa masa zan shiga ciki na dawo." Kai ta girgiza kawai ita kuma ta fita.
*Bayan Kwana biyu.*
Babu abinda ya ragu ta b'angaren harin da ake kawowa Asad bai kuma fasa addu'a ba mafarkin da yake kullum k'aruwa yake, tunda aka zana masa fuskar ta kuma sai ya koma ganin fuskar a mafarkin amma yak'i bari mafarkin yin tasiri a zuciyar sa yana k'ok'arin mantawa dashi koda yaushe. Fuskar ta ta zama masa tamkar hoto a idanun sa da ya kulle sai ya hango ta hakan ya saka yake jin wani iri a zuciyar sa.
Hydar na kwance har lokacin amma an samu cigaba dan zuwa lokacin yana motsawa alamun ya kusa farfad'owa kenan.
A zaune take a babban d'akin ta wanda aka k'awata shi da kayan gado na alfarma waya na hannun ta, kamar wacce aka tunawa ta danna number Dr ta kira shi bata jima tana ringing ba ya d'auka yana fad'in, "Allah ya ja da ran Mama."
"Ka sallami yarinyar nan kuwa ko tana nan?" Bata amsa gaisuwar ba abinda ta fara tambaya kenan. D'an dabarbarcewa yayi kana yace, "Na sallame ta Mama."
"In ka min k'arya na gano gaskiya kai kasan sauran."
"Ba k'arya nake ba tun lokacin na sallame ta."
"Ka kyauta. In Hydar ya farfad'o kasan sometimes yakan manta wasu abubuwan na baya sai daga baya ya tuna in ya manta batun ta koda zai tambaye ka bana so ka sanar dashi kace komai bai faru ba ka gane ko?."
Kamar yana gaban ta ya girgiza kai alamun to kafin yace, "zanyi in sha Allah." Bata kuma cewa komai ba ta yanke wayar yabi wayar da kallo yana sauke numfashi. "Wannan mata masifaffiya ce, ta yaya zan iya sallamar Rauda bayan har yanzu bata ji sauk'i ba?. In kuma na barta ta gano na shiga uku." Tsaki yaja ya mik'e ya tafi d'akin da Raudan take ya same ta a zaune tana karatun alkur'ani a bayyane. kallon ta yake da birgewa domin da wuya yazo ya same ta haka kawai bata karatu ko lazumi.
Sallama yayi ta katse karatun ta kalle shi tace, "Dr shigo mana." Umma da bacci ya fara d'aukar ta ta mik'e zaune ya k'araso ya tsaya yana kallon k'afar tata yace, "Ya k'afar?."
"K'afa da sauk'i yanzu bata min ciwo ai sai dai gajiya da zama." Ya sauke numfashi yace, "Rauda kud'in wanda ya kawo ki asibitin nan ya k'are kuma shima yana kwance babu lafiya tun zuwan sa na k'arshe nan shine na rasa yadda zanyi." Gaban Umma ya fad'i itama Raudan haka ta rufe alkur'anin tace, "To sai mu koma gida."
"Eh ko kuma ku biya kud'in."
Umma da take gefe tace, "mu biya me likita? Ina muka ga wannan halin?, gwara dai mu koma tunda Allah yayi k'afar tayi kyau."
Jikin sa sai yayi sanyi ya sauke numfashi yace, "to in kun shirya zan saka a kai ku a mota sabida k'afar tata kafin kuje ku saka a gyara mata inda zata zauna, zan baku magungunan da zata dinga sha da abubuwan da ya kamata ta cigaba da ci in sun k'are a kuma siya. Kuyi hak'uri dan Allah na rasa yadda zanyi ne."
"Haba likita meye na bada hak'uri? Ai kayi k'ok'ari ko kaine ka buge ta ai sai haka."
Rauda ta tab'e baki tace, "Daman su y'ay'an masu kud'in nan babu abinda suka sani sai kansu, yanzu inda girmamawa ai yaci ace wani nasa yazo ya cigaba da d'aukar nauyi na tunda sune silar komai. Tunda bashi da lafiya an bar maganar daman ba gata ne dani ba sun yiwa banza. Allah wadaran wasu masu kud'in" Rauda ta fad'a a fusace.
Dr yace, "Wallahi Hydar bashi da wannan halin baki ga yadda ya tsaya akan ki ba rashin lafiya ce dashi in ta tashi sai ya kwashe sati uku a sume bai farfad'o ba, yanzu zancen da nake miki tun da yazo nan ciwon ya same sa bai tashi ba har yanzu."
Umma tace, "kai ka biye mata ai likita ai ko iya haka aka tsaya yayi k'ok'ari sosai, wanda in sun buge ka suke guduwa fa su kuma ace musu me?."
"Umma maganar da ta fad'a gaskiya ce ya kamata ace wani nasa ya tsaya, amma da zaku san waye shi ku kuma san abubuwan da suke faruwa da ku kan ku kun tausaya masa shida y'an uwan nasa."
"Allah ya kyauta" Umma ta fad'a.