Sashe 20
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Asad ya girgiza kai mai martaba yace, "ka cigaba da addu'a duk abinda ya tunkaro ka ka fuskance shi ka daina cin abincin kowa sai wanda Maman ka ta baka itace kad'ai ce baza ta cutar da kai ba dan itace ta haife ka bayan ita kar ka amince da kowa hatta y'anuwan ka na jini ban d'auke kowa a cikin su ba sai kuma wanda zuciyar ka ta amince dasu."
"In sha Allah Takawa zanyi abinda aka umarce ni" ya fad'a da girmamawa kamar ko yaushe kansa yana kallon k'asa.
Mai martaba yace, "Allah ya bada iko. Kak'i kayi aure wata k'ila matar taka ce garkuwa a gare ka Allah yake nuna maka tun yanzu, ka daure ka nemo mata kayi aure a kwanakin Asad."
"In sha Allah zanyi" ya bashi amsa yana murmushi.
Murmushin shima yake yana kallon sa, kaf y'ay'an sa babu wanda yake so kamar Asad a baya yaso Aliyu amma a yanzu halayen sa sam sun saka ya fita a ransa amma Asad shine a kan gaba a kaf cikin yaran sa. Shi kad'ai ne zai zauna dashi yayi doguwar hira haka shima Asad d'in shi kad'ai yake iya fad'awa damuwar sa hakan ya saka in suka zauna waje d'aya sai su shafe awa d'aya mai martaba bai ga kowa ba sai shi kawai.
Bai wani jima sosai ba ya fito yana takawa a hankali kasancewar yamma tayi iska na kad'a shi yana kallon kowa na aikin sa ana ta gaishe sa yana d'aga hannu ko ya d'aga kai. Wajan Mama ya tafi yana shiga duk da bayin da suke zaune a wajan bai hana ta tashi ta k'araso wajan sa ta rik'e shi tana fad'in, "Asad ya jikin naka?."
"Mamana ta kwantar da hankalin ta naji sauk'i, ina Hydar?" Ya fad'a yana tafiya d'akin da hydar yake tabi bayan sa. Gadon Hydar ya dafa yana masa addu'a yana kallon sa dan kaf cikin y'an uwan sa yafi son Hydar dan shima yana son sa.
"Asad ka daina jin ciwon cikin?" Mama ta tambaya tana kallon sa. Kallon ta yayi yace, "eh Mamana, da sauk'i."
"Abinda nake nuna maka baka ganewa shine ya faru Asad, zogalen da kaci a cikin gubar take, da ka mutu ya zanyi...?.."
Murmushi yayi yace, "Mamana ban mutu ba kuma na gane duk abinda mahaifiyata take fad'a min." Murmushi tayi tana kallon sa tace, "na gode Asad, Allah yayi maka albarka ya baka lafiya ya kare ka a duk inda kake." A iya labban sa taga ya amsa da amin.
Tare suka fito tana gaba yana binga ta kalle shi tace, "yanzu ina zaka je?." Shiru yayi bai amsa ba tace, "kar ka fita ka huta Asad please." Ya d'aga kai a lokacin Jidda ta fito daga d'aki tana ganin sa tayi murmushi, "Mama Bro deaf ne right?."
"Yeah, but ki daina kiran sa deaf fa." Murmushi tayi tana kallon sa tace, "ya jikin?." Kai ya d'aga kawai kafin ya wuce ya fita baice komai ba. Zuciyar Mama fal farin ciki ganin yaji sauk'i sosai kamar ba shi ba taji dad'i duk da kuma Hydar na kwance.
Asad lokacin da ya fita jakadiyar Hajiya ta zube a gaban sa tana fad'in, "Allah ya ja zamanin yarima mai jiran gado, Allah ya kare zakin mu, Allah ya kiyaye ka ya baka kariya daga mak'iya." Shiru yayi jin hakan ya saka tace, "Gimbiya uwar gidan mai martaba tace ayi maka magana tana son ganawa dakai."
Da hannu yayi mata alamun da su je, gaba yayi tana bayan sa tana kirari har sai da ya juyo ya kalle ta tayi shiru ya cigaba da tafiya tana bayan sa, yana zuwa ya shiga ita kuma tana tsaya a bakin k'ofa ya shiga da sallama. K'annen sa maza da y'an matan ta guda biyu Khaleesat da Juwairiyya ya gani suna ganin sa kowa ya mik'e suka gaishe shi ya amsa da murmushi kana yace, "kun b'oye." Mamaki suke jin ya musu magana Khaleesat tace, "naje duba ka d'azu kana bacci." Kai ya d'aga kai kafin Juwairiyya tace, "Hajiyan tace ka shiga ciki."
Kai ya kuma d'aga ya shiga ya same ta a falon ta ita kad'ai tana ganin sa ta mik'e tana cewa, "Asad wallahi ban baka komai dan na cuce ka ba, ina kallon ka kamar d'an dana haifa akan me zan kashe ka kona kwantar da kai ciwo....? kayi hak'uri ban san waye ba" ta fad'a kamar zatayi kuka.
"Babu komai Hajiya, na amince Hajiya tamkar Mamana."
"In kai ka amince mahaifiyar ka baza ta amince ba Asad, gani take kashe ka zanyi." Kai ya girgiza yace, "babu komai" ya furta da murmushi yana kallon ta kafin tace, "na gode Asad, Allah ya baka lafiya. Zan cigaba da aiko maka da ganye kamar yadda nasan kana so, wallahi da zuciya d'aya nake maka badan wani abun ba."
"Na gode." Tace, "Zaka iya tafiya." Baice komai ba ya juya zai tafi tabi bayan sa da kallo tana murmushi har ya fita kafin ta gyara tsayuwar ta tace, "Yanzu aka fara wasan Rabi'atu, yanzu kafcen ya fara, mu jira muga ni dake waye zaiyi nasara wa za'a bawa lambar girmamawa.....? Dan ni Sa'adatu bazan tab'a barin Asad ba sai naga bayan sa!" tayi murmushi ta shafa fuskarta ta shiga d'aki zuciyar ta kar.........
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*010.*
Asad lokacin da ya koma d'akin sa gaban mirror ya tsaya yana kallon kansa fassarar mafarkin da mahaifin yayi masa yana dawo masa cikin kansa tiryan-tiryan, kenan akwai mace da zata shigo rayuwar sa matsayin mata? Wacece ita?, a ina take Allah ya had'a su tun a mafarki?. Shin ita tana mafarkin sane ko batayi?. Sam baya so wata mace ta shigo rayuwar sa ko kad'an sabida shi kad'ai yasan illar dake tattare da hakan.
Lumshe idanun sa yayi tuno Jidda ce zab'in Mama ya bud'e idanun a zuciyar sa yana tambayar kansa kodai Jiddan itace yarinyar mafarkin...? Numfashi ya sauke a hankali kammanin ta suke bayyana a idanun sa kamar lokacin yake mafarkin.
Wara idanun sa yayi yana hango zubin ta da kammanin ta amma basa fita tarrr amma yana iya hango ta a idanun sa kamar almara, agogo ya kalla yaga yamma tayi sosai bazai yu yaje Abuja ya dawo a ranar ba da babu abinda zai hana shi zuwa Abuja wajan abokin sa Zaid ya zana masa fuskar da yake gani a mafarki ko zai iya gane ta in ya ganta, da ace yana kano ma a lokacin zai tafi amma yasan yana Abuja.. Haka yayi ta zaune da wannan tunanin kafin ya tashi ya d'auki makullin mota ya fita.
*☆☆☆*
"Dan Allah Malam ka bani koda duba d'aya ne a kud'in na siyo mata kayan marmari ta sha bata iya cin abinci, koda tana ci ma ba'a son mai karaya tana cin abu mai nauyi sabida zagawa band'aki" Umma ta fad'a tana kallon Baba da yake tsaye a cikin d'akin.
Baba ya gyara zaman hula yace, "Kinga ni babu komai a jikina kud'in ma da aka bani na adana su sai auren ta yazo sai ayi amfani dasu, ga shinkafa da manja nan ai nasan tana san cin abinci da manja shiyasa na saka aka dafa mata."
"Yanzu Malam mai karayar ce zata ci shinkafa da manja? Kazar gida fa ita ake so masu karaya suci sabida tabi jikin su."
"To ba'a haifo ta inda zata ci kazar ba in baza ta ci shinkafar ba ta hak'ura."
"Amma Malam kud'in da aka bayar fa duk nata ne tunda itace take jinya."
A fusace yace, "Amma ji kikayi nace ai na adana mata sai lokacin bikin ta ko? Ko saka su a gaba nayi naci banza da wofi dasu?." Jin yadda yake magana Rauda dake kwance tace, "Umma a bar shi zanci shinkafar." Umma tace, "ta ina zaki ci shinkafa Rauda?, baki san ba'a san mai karaya ya dinga cin abu mai nauyi ba sabida yawon band'aki?. Dan Allah malam ka bani koda naira d'ari biyar ce."
Tsaki yayi ya saka hannu a aljihu ya d'auko naira d'ari biyu yace, "gashi nan a siyo mata." Ba yadda Umma ta iya haka ta karb'a ta kalli Khairi da Khalil da suke gefe tace, "Khairi ina za'a samo mata kankana da lemon zak'i tasha?." Khairi tace, "Umma wajan asibitin nan akwai amma da gani zaiyi tsada tunda kinga asibitin manya ne."
"Jeki dai ki duba mana ko za'a samu" ta fad'a tana bata kud'in ba musu ta karb'a ta tafi.
Tana fitowa wajan asibitin kuwa suna nan masu kayan zak'in ta tsallako ta nufo su tunda ta tawo kowa ya tashi dan daman an san siyayya za'ayi ta k'arasa wajan d'aya tace, "Sannu Baba." Yayi murmushi yace, "yauwa y'ata me za'a baki?."
"Kankana nake so ta naira d'ari lemo ma na d'ari" ta fad'a tana mik'a masa kud'in. Kallon ta yayi ya kalli kud'in ya kalli asibitin da ta fito sai ta girgiza kai yace, "yarinya babu na kud'in sai dai na baki lemo guda biyu ko wanne naira dari."
Wara idanu tayi tace, "a unguwar mu naira ashriin-ashirin ne, bar shi bara na tambayi na gaba." Koda taje na gaban ma shima haka sukayi ta je na kusa dashi shi ce mata ma yayi babu ta tsaya cak kawai tana kallon su cikin rashin sanin abin yi.
Mota ce ta faka a kusa da ita aka sauke glass dai-dai lokacin da take cewa, "Yayata aka kwantar a nan kuma bata iya cin abinci dan Allah ku taimaka min ku bani kankana da lemo na d'ari biyu ita kad'ai ce damu itama dak'yar Baba ya bayar."
"Dallah malama bamu dana kud'in ki ki wuce ki bawa mutane waje, y'ar aiki kawai" daya daga cikin su ya fad'a ta juyo idanun ta ya fad'a kan Asad da yake kallon su mai siyar da Apple yana masa magana ma amma baiji ba.
"In sha Allah Takawa zanyi abinda aka umarce ni" ya fad'a da girmamawa kamar ko yaushe kansa yana kallon k'asa.
Mai martaba yace, "Allah ya bada iko. Kak'i kayi aure wata k'ila matar taka ce garkuwa a gare ka Allah yake nuna maka tun yanzu, ka daure ka nemo mata kayi aure a kwanakin Asad."
"In sha Allah zanyi" ya bashi amsa yana murmushi.
Murmushin shima yake yana kallon sa, kaf y'ay'an sa babu wanda yake so kamar Asad a baya yaso Aliyu amma a yanzu halayen sa sam sun saka ya fita a ransa amma Asad shine a kan gaba a kaf cikin yaran sa. Shi kad'ai ne zai zauna dashi yayi doguwar hira haka shima Asad d'in shi kad'ai yake iya fad'awa damuwar sa hakan ya saka in suka zauna waje d'aya sai su shafe awa d'aya mai martaba bai ga kowa ba sai shi kawai.
Bai wani jima sosai ba ya fito yana takawa a hankali kasancewar yamma tayi iska na kad'a shi yana kallon kowa na aikin sa ana ta gaishe sa yana d'aga hannu ko ya d'aga kai. Wajan Mama ya tafi yana shiga duk da bayin da suke zaune a wajan bai hana ta tashi ta k'araso wajan sa ta rik'e shi tana fad'in, "Asad ya jikin naka?."
"Mamana ta kwantar da hankalin ta naji sauk'i, ina Hydar?" Ya fad'a yana tafiya d'akin da hydar yake tabi bayan sa. Gadon Hydar ya dafa yana masa addu'a yana kallon sa dan kaf cikin y'an uwan sa yafi son Hydar dan shima yana son sa.
"Asad ka daina jin ciwon cikin?" Mama ta tambaya tana kallon sa. Kallon ta yayi yace, "eh Mamana, da sauk'i."
"Abinda nake nuna maka baka ganewa shine ya faru Asad, zogalen da kaci a cikin gubar take, da ka mutu ya zanyi...?.."
Murmushi yayi yace, "Mamana ban mutu ba kuma na gane duk abinda mahaifiyata take fad'a min." Murmushi tayi tana kallon sa tace, "na gode Asad, Allah yayi maka albarka ya baka lafiya ya kare ka a duk inda kake." A iya labban sa taga ya amsa da amin.
Tare suka fito tana gaba yana binga ta kalle shi tace, "yanzu ina zaka je?." Shiru yayi bai amsa ba tace, "kar ka fita ka huta Asad please." Ya d'aga kai a lokacin Jidda ta fito daga d'aki tana ganin sa tayi murmushi, "Mama Bro deaf ne right?."
"Yeah, but ki daina kiran sa deaf fa." Murmushi tayi tana kallon sa tace, "ya jikin?." Kai ya d'aga kawai kafin ya wuce ya fita baice komai ba. Zuciyar Mama fal farin ciki ganin yaji sauk'i sosai kamar ba shi ba taji dad'i duk da kuma Hydar na kwance.
Asad lokacin da ya fita jakadiyar Hajiya ta zube a gaban sa tana fad'in, "Allah ya ja zamanin yarima mai jiran gado, Allah ya kare zakin mu, Allah ya kiyaye ka ya baka kariya daga mak'iya." Shiru yayi jin hakan ya saka tace, "Gimbiya uwar gidan mai martaba tace ayi maka magana tana son ganawa dakai."
Da hannu yayi mata alamun da su je, gaba yayi tana bayan sa tana kirari har sai da ya juyo ya kalle ta tayi shiru ya cigaba da tafiya tana bayan sa, yana zuwa ya shiga ita kuma tana tsaya a bakin k'ofa ya shiga da sallama. K'annen sa maza da y'an matan ta guda biyu Khaleesat da Juwairiyya ya gani suna ganin sa kowa ya mik'e suka gaishe shi ya amsa da murmushi kana yace, "kun b'oye." Mamaki suke jin ya musu magana Khaleesat tace, "naje duba ka d'azu kana bacci." Kai ya d'aga kai kafin Juwairiyya tace, "Hajiyan tace ka shiga ciki."
Kai ya kuma d'aga ya shiga ya same ta a falon ta ita kad'ai tana ganin sa ta mik'e tana cewa, "Asad wallahi ban baka komai dan na cuce ka ba, ina kallon ka kamar d'an dana haifa akan me zan kashe ka kona kwantar da kai ciwo....? kayi hak'uri ban san waye ba" ta fad'a kamar zatayi kuka.
"Babu komai Hajiya, na amince Hajiya tamkar Mamana."
"In kai ka amince mahaifiyar ka baza ta amince ba Asad, gani take kashe ka zanyi." Kai ya girgiza yace, "babu komai" ya furta da murmushi yana kallon ta kafin tace, "na gode Asad, Allah ya baka lafiya. Zan cigaba da aiko maka da ganye kamar yadda nasan kana so, wallahi da zuciya d'aya nake maka badan wani abun ba."
"Na gode." Tace, "Zaka iya tafiya." Baice komai ba ya juya zai tafi tabi bayan sa da kallo tana murmushi har ya fita kafin ta gyara tsayuwar ta tace, "Yanzu aka fara wasan Rabi'atu, yanzu kafcen ya fara, mu jira muga ni dake waye zaiyi nasara wa za'a bawa lambar girmamawa.....? Dan ni Sa'adatu bazan tab'a barin Asad ba sai naga bayan sa!" tayi murmushi ta shafa fuskarta ta shiga d'aki zuciyar ta kar.........
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*010.*
Asad lokacin da ya koma d'akin sa gaban mirror ya tsaya yana kallon kansa fassarar mafarkin da mahaifin yayi masa yana dawo masa cikin kansa tiryan-tiryan, kenan akwai mace da zata shigo rayuwar sa matsayin mata? Wacece ita?, a ina take Allah ya had'a su tun a mafarki?. Shin ita tana mafarkin sane ko batayi?. Sam baya so wata mace ta shigo rayuwar sa ko kad'an sabida shi kad'ai yasan illar dake tattare da hakan.
Lumshe idanun sa yayi tuno Jidda ce zab'in Mama ya bud'e idanun a zuciyar sa yana tambayar kansa kodai Jiddan itace yarinyar mafarkin...? Numfashi ya sauke a hankali kammanin ta suke bayyana a idanun sa kamar lokacin yake mafarkin.
Wara idanun sa yayi yana hango zubin ta da kammanin ta amma basa fita tarrr amma yana iya hango ta a idanun sa kamar almara, agogo ya kalla yaga yamma tayi sosai bazai yu yaje Abuja ya dawo a ranar ba da babu abinda zai hana shi zuwa Abuja wajan abokin sa Zaid ya zana masa fuskar da yake gani a mafarki ko zai iya gane ta in ya ganta, da ace yana kano ma a lokacin zai tafi amma yasan yana Abuja.. Haka yayi ta zaune da wannan tunanin kafin ya tashi ya d'auki makullin mota ya fita.
*☆☆☆*
"Dan Allah Malam ka bani koda duba d'aya ne a kud'in na siyo mata kayan marmari ta sha bata iya cin abinci, koda tana ci ma ba'a son mai karaya tana cin abu mai nauyi sabida zagawa band'aki" Umma ta fad'a tana kallon Baba da yake tsaye a cikin d'akin.
Baba ya gyara zaman hula yace, "Kinga ni babu komai a jikina kud'in ma da aka bani na adana su sai auren ta yazo sai ayi amfani dasu, ga shinkafa da manja nan ai nasan tana san cin abinci da manja shiyasa na saka aka dafa mata."
"Yanzu Malam mai karayar ce zata ci shinkafa da manja? Kazar gida fa ita ake so masu karaya suci sabida tabi jikin su."
"To ba'a haifo ta inda zata ci kazar ba in baza ta ci shinkafar ba ta hak'ura."
"Amma Malam kud'in da aka bayar fa duk nata ne tunda itace take jinya."
A fusace yace, "Amma ji kikayi nace ai na adana mata sai lokacin bikin ta ko? Ko saka su a gaba nayi naci banza da wofi dasu?." Jin yadda yake magana Rauda dake kwance tace, "Umma a bar shi zanci shinkafar." Umma tace, "ta ina zaki ci shinkafa Rauda?, baki san ba'a san mai karaya ya dinga cin abu mai nauyi ba sabida yawon band'aki?. Dan Allah malam ka bani koda naira d'ari biyar ce."
Tsaki yayi ya saka hannu a aljihu ya d'auko naira d'ari biyu yace, "gashi nan a siyo mata." Ba yadda Umma ta iya haka ta karb'a ta kalli Khairi da Khalil da suke gefe tace, "Khairi ina za'a samo mata kankana da lemon zak'i tasha?." Khairi tace, "Umma wajan asibitin nan akwai amma da gani zaiyi tsada tunda kinga asibitin manya ne."
"Jeki dai ki duba mana ko za'a samu" ta fad'a tana bata kud'in ba musu ta karb'a ta tafi.
Tana fitowa wajan asibitin kuwa suna nan masu kayan zak'in ta tsallako ta nufo su tunda ta tawo kowa ya tashi dan daman an san siyayya za'ayi ta k'arasa wajan d'aya tace, "Sannu Baba." Yayi murmushi yace, "yauwa y'ata me za'a baki?."
"Kankana nake so ta naira d'ari lemo ma na d'ari" ta fad'a tana mik'a masa kud'in. Kallon ta yayi ya kalli kud'in ya kalli asibitin da ta fito sai ta girgiza kai yace, "yarinya babu na kud'in sai dai na baki lemo guda biyu ko wanne naira dari."
Wara idanu tayi tace, "a unguwar mu naira ashriin-ashirin ne, bar shi bara na tambayi na gaba." Koda taje na gaban ma shima haka sukayi ta je na kusa dashi shi ce mata ma yayi babu ta tsaya cak kawai tana kallon su cikin rashin sanin abin yi.
Mota ce ta faka a kusa da ita aka sauke glass dai-dai lokacin da take cewa, "Yayata aka kwantar a nan kuma bata iya cin abinci dan Allah ku taimaka min ku bani kankana da lemo na d'ari biyu ita kad'ai ce damu itama dak'yar Baba ya bayar."
"Dallah malama bamu dana kud'in ki ki wuce ki bawa mutane waje, y'ar aiki kawai" daya daga cikin su ya fad'a ta juyo idanun ta ya fad'a kan Asad da yake kallon su mai siyar da Apple yana masa magana ma amma baiji ba.