Sashe 46
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Asad yafi k'arfin ta ku sake b'alla k'afar tata dan uban ta" Mum ta fad'a tana daga gefe ana dukan Rauda kamar zasu kashe ta. Baba yace, "Waye Asad din nan da kike magana a kansa? Bamu sanshi ba balle muyi abinda kuke so. Dan Allah ku bar dukan su ko waye zata rabu dashi."
"Ai ko baka ce ba sai ta rabu dashi, ka kuma ce mata ta karya asirin da ta yi masa in tana son zaman lafiyar ta da ta uwar ta har ma da kai ubanta. Ta fita daga sabgar Asad d'an sarki sai y'ar sarki ko y'ar mai kud'i ba d'iyar talaka y'ar tallah kamar ta ba."
Ganin sun duku ya saka tace, "Guys ku shigo ku d'aye min kwanukan rufin gidan nan naga inda zasu kwana yau daman naga langa-langa ne kawai" ta fad'a daga k'arfi sai ga maza uku sun kuma shigowa suka hau saman d'akin suka farar b'alle kwanon rufin d'akin wanda yayi gardmar cirewa suna huda shi da abu mai kaifi. Mum ta saki dariya tana tafa hannu ta kalli Rauda da bakin ta ya fashe jini na zuba a gefe tace, "Ke ba y'ar marasa kunya ba...? yanzu kika fara gani, har ni zaki saka hannu ki mara da yake baki da mutunci ko? ai kin tarowa kanki bala'i da masifa har ki mutu. Ku k'yale su haka kuzo mu wuce ai ko yanzu sun ji a jikin su; sai ku ja mata kunne in bata fita daga rayuwar Asad ba wallahi nan gaba sai mun saka an rushe gidan nan an kuma yi musu abinda yafi haka, banzaye mahaukata masu kai kansu inda Allah bai kaisu ba" tana fad'a ta shige ta fita suma suka bi bayan ta mazan saman suka diro suka bi bayan ta.
Suna sakin Baba yayo kan Umma a guje dan ita kamar bata numfashi ma gwara Rauda tana motsawa amma Umma na kwance sosai. Kuka Rauda take yi sosai Rahma da ta maku tana gefe ganin sun tafi ya saka tayo kan Rauda ta d'aga ta fuskar ta duk jini hawaye na bin fuskar ta. Baba ya fita da sauri hankalin sa a tashe ya yi sa'a mai chemist d'in yana nan ya tawo dashi gida aka fara duba Umma da take kwance. Fita yayi ya dawo da kayan aiki aka shiga yiwa Umma taimakon gaggawa aka samu ta farfad'o dukan fuskar ta aka gyara aka saka mata ruwa dan jikin ta yayi zafi sosai ga hannun ta an mata targed'e. Kan Rauda akayi aka gyara mata fuska aka bata maganin ciwon jiki dana ciwon da taji a fuskar ta har loksckn kuka take. Ba kukan dukan take ba kukan zuwa gida da akayi aka wulaƙanta su take yi in ta kalli Umman ta bata sanin sanda hawaye yake sake zubo mata.
Yana fita aka zo da mai gyaran targad'e ya gyara hannun Umma aka d'aure hannun sannan suka tafi Baba jikin sa duka yayi sanyi.
Kuka sosai Rauda take yi tana jikin Rahma Baba yace, "Rauda ban fahimci abinda matar nan take nufi ba, meye tsakanin ki Asad har hakan ta faru?." Kai take girgizawa tace, "Wallahi babu komai Baba, bansan wanda suke nufi ba; sun yi amfani da power sun zo sun wulak'anta mu sabida bamu da gata bamu da wanda zai bi mana hakkin mu. Wallahk Baba bazan yarda ba sai maganar nan taje gaban hukuma sai an bi mana hakkin mu, Baba sai an karb'a mana hakkin mu bazan amince da wannan cik mutuncin ba" ta fad'a tana kuka sosai.
Baba yace, "Nima bazan bari ba Rauda cin kashin yayi yawa. Tunda sukayi maganar Asad d'an sarki zanje wajan mai martabar da kaina na kai masa k'arar abinda ya faru, ai talauci ba hauka bane ba. Meye tsakanin mu dasu in ba silar ciwon nan naki ba? Dan kawai yana sauke nauyin da yake kansu na nema miki lafiya kawai sai azo har gida ayi mana wannan shirmen...? To wallahi bazan amince ba." Kuka take ita dai har lokacin tana kallon saman d'akin Umma da aka kwashe kwanon kai rana tar a cikin sa sai wani b'angaren da aka huda, a hankali bacci ya d'auke ta Allah ya saka akwai inuwar rumfa a wajan.
*☆☆☆*
B'angaren Asad bai san me yake faruwa ba suna tare da Hydar a company dan bai koma aiki ba yana wajan Asad, sai da sukayi azahar suka bar company suka koma gida dan yunwa Asad yake ji. Suna b'angaren su Suhaima tazo ta kawo musu abinci ta ajjiye ta zuba musu kamar ko yaushe, Asad ya d'auki wanda ta zuba masa ya d'auka zai kai bakin sa Suhaima ta kalli Hydar tace, "Yaya Hydar wai me ya faru ne naga ran Mama a b'ace?."
Hydar ya fara cin abinci kana yace, "Ina zan sani Suhaima nida na dawo yanzu?."
"Naji tana waya tana a dake su bata kai matsayin yin soyayya da wanda ta haifa ba, na d'auka ma ko kaine ka fara soyayya da wata poor lady d'in ta saka ayi mata punishment." Gaban Asad ya fad'i ya ajjiye cokalin daman tunda ta fara maganar bai kai abincin bakin sa ya kalle ta yace, "Suhaima me kika ji tace?."
"A yadda take maganar dai an tura gidan su yarinyar ayi mata duka amma ban san wacece ba. Naji tana a dake ta inda dama a sake b'alla k'afar ta babu abinda aka siya ayi." Mik'ewa Asad yayi ya d'auki key na mota da sauri ya fita, ganin hakan Hydar ma ya ture abincin ya mik'e tare da bin bayan sa suka fita Suhaima ta bi su da kallo.
Mota suka shiga suka tafi gidan su Rauda gaban Asad sai fad'uwa yake yi har suka faka a k'ofar gidan, babban burin sa bai wuce Allah yasa basu illatata ko wani nata ba.
Baba suka gani ya fito yana waige-waige ganin hakan ya saka Asad ya fito daga motar Hydar ma ya biyo bayan sa suka k'araso kusa dashi, Baba na ganin su tun kafin su gaisa yace, "Kamar kusan kune a raina, me muka yi muku haka da za'a aiko azo a ci mutunci na dana iyalai na?, me Rauda tayi muku har haka aka yi mata wannan hukunci....? dan Allah ku fad'a na baki hak'uri."
Asad ya kalli Hydar shima ya kalle shi kafin Hydar ya kalli Baba yace, "Baba meye ya faru?." Baba yace, "Kuzo muje ku gani" ya fad'a yana yin gaba suka bi bayan sa gaban Asad sai fad'uwa yake yi sabida fargaba da tashin hankalin abinda zai gani a cikin gidan.
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*022.*
A hankali suke takawa zuwa cikin gidan suka shiga da sallama idanun sa ya fad'a na Rauda da take zaune cikin ranar da bud'e har taje inda suke fuskar ta duk taji ciwo musamman bakinta da ya fashe. Runtse idanu Asad yayi ya kawar da kansa gefe daga kallon ta kafin Baba yace, "Kunga irin abinda aka yi mana. kalli mahaifiyar Rauda har targad'e aka yi mata, ga ita kanta Rauda da ta kasa tashi tsaye tun da akayi abun bamu sani ba ko an sake karya mata k'afa ne; kalli saman d'akin babar Raudan sun cire kwanon bayan sun dake ta. Me muka yi muku haka?."
Hydar ya gyara tsayuwa yace, "Kuyi hak'uri Baba bamu san abinda ya faru ba kenan sai yanzu muke jin labari shine muka tawo nan d'in kai tsaye dan muyu maganin abun, Mama kiyi hak'uri bamu san abinda ya faru ba kenan" ya fad'a yana kallon Umma. Rauda ta kalle shi ta zaro idanu waje cikin zallar b'acin rai da tashin hankali tace, "Ba tun yau ba daman in aka cuci mutum sai ace yayi hak'uri, in aka zalumci talaka sai ace yayi hak'uri ya yafe sabida bashi da gata da wanda zai shige masa gaba ya karb'i hakkin sa. dan an fimu kud'i da mulki ba hakan yana nufin an mufi daraja a duniya bane, muma mutane ne baza mu lamunci azo har cikin gidan mu a ci mana mutunci sannan a dake mu ba kuma ace muyi hak'uri; bazai yu ba wallahi. Meye ya had'a mu daku da za'a dake mu a kanku? Tsautsayi ne ya ratsa tsakani fa akwai shikenan sai ya zama abin tashin hankali?, naga tun kafin bayyanar ku cikin matsayin wanda suka bige mu ai rayuwar mu muke yi babu abinda muka nema muka rasa, daga shigowar ku rayuwar mu har an fara neman raywuar mu?" Ta fad'a cikin fusata da masifa tana kallon su dukkan ranta a b'ace ba.
Hydar yazo wuya ba'a tab'a yi masa irin wannan fad'an ba a duniya sai yau nan take ransa ya b'aci amma babu yadda ya iya yayi k'okarin b'oye fushin sa kana yace, "Na fad'a miki ko meye ya faru babu sanin deaf babu sani na, inda mun sani hakan ai baza mu bari ta faru ba. Yanzu ake sanar damu muka tawo dan muga su waye amma bamu same su ba, meyasa baza ki fahimta ba?."
"Zuwan ku d'in banza da wofi dashi gwara ku zauna a gida ku sha a.c yafi min wallahi. Sai da aka gama ci maa mutunci sannan zaku d'auko k'afa kuce wai kunzo to kuyi mana me? Ku bamu hak'uri kenan ko?. Ni abinda nake so naji ma akan wanne dalili zasu dake mu har su yiwa Ummana wannan rashin mutuncin?, suna zancen wani Asad ni meye had'ina da wani Asad?, su ya dama bani ba wallahi in ma wani sharrin aka je aka min can ta matse muku amma wallahi sai maganar nan taje gaba in ba haka ba na shiga radio na yayata abinda aka mana ko babu komai k'imar gidan ku zata ragu."
"Ai ko baka ce ba sai ta rabu dashi, ka kuma ce mata ta karya asirin da ta yi masa in tana son zaman lafiyar ta da ta uwar ta har ma da kai ubanta. Ta fita daga sabgar Asad d'an sarki sai y'ar sarki ko y'ar mai kud'i ba d'iyar talaka y'ar tallah kamar ta ba."
Ganin sun duku ya saka tace, "Guys ku shigo ku d'aye min kwanukan rufin gidan nan naga inda zasu kwana yau daman naga langa-langa ne kawai" ta fad'a daga k'arfi sai ga maza uku sun kuma shigowa suka hau saman d'akin suka farar b'alle kwanon rufin d'akin wanda yayi gardmar cirewa suna huda shi da abu mai kaifi. Mum ta saki dariya tana tafa hannu ta kalli Rauda da bakin ta ya fashe jini na zuba a gefe tace, "Ke ba y'ar marasa kunya ba...? yanzu kika fara gani, har ni zaki saka hannu ki mara da yake baki da mutunci ko? ai kin tarowa kanki bala'i da masifa har ki mutu. Ku k'yale su haka kuzo mu wuce ai ko yanzu sun ji a jikin su; sai ku ja mata kunne in bata fita daga rayuwar Asad ba wallahi nan gaba sai mun saka an rushe gidan nan an kuma yi musu abinda yafi haka, banzaye mahaukata masu kai kansu inda Allah bai kaisu ba" tana fad'a ta shige ta fita suma suka bi bayan ta mazan saman suka diro suka bi bayan ta.
Suna sakin Baba yayo kan Umma a guje dan ita kamar bata numfashi ma gwara Rauda tana motsawa amma Umma na kwance sosai. Kuka Rauda take yi sosai Rahma da ta maku tana gefe ganin sun tafi ya saka tayo kan Rauda ta d'aga ta fuskar ta duk jini hawaye na bin fuskar ta. Baba ya fita da sauri hankalin sa a tashe ya yi sa'a mai chemist d'in yana nan ya tawo dashi gida aka fara duba Umma da take kwance. Fita yayi ya dawo da kayan aiki aka shiga yiwa Umma taimakon gaggawa aka samu ta farfad'o dukan fuskar ta aka gyara aka saka mata ruwa dan jikin ta yayi zafi sosai ga hannun ta an mata targed'e. Kan Rauda akayi aka gyara mata fuska aka bata maganin ciwon jiki dana ciwon da taji a fuskar ta har loksckn kuka take. Ba kukan dukan take ba kukan zuwa gida da akayi aka wulaƙanta su take yi in ta kalli Umman ta bata sanin sanda hawaye yake sake zubo mata.
Yana fita aka zo da mai gyaran targad'e ya gyara hannun Umma aka d'aure hannun sannan suka tafi Baba jikin sa duka yayi sanyi.
Kuka sosai Rauda take yi tana jikin Rahma Baba yace, "Rauda ban fahimci abinda matar nan take nufi ba, meye tsakanin ki Asad har hakan ta faru?." Kai take girgizawa tace, "Wallahi babu komai Baba, bansan wanda suke nufi ba; sun yi amfani da power sun zo sun wulak'anta mu sabida bamu da gata bamu da wanda zai bi mana hakkin mu. Wallahk Baba bazan yarda ba sai maganar nan taje gaban hukuma sai an bi mana hakkin mu, Baba sai an karb'a mana hakkin mu bazan amince da wannan cik mutuncin ba" ta fad'a tana kuka sosai.
Baba yace, "Nima bazan bari ba Rauda cin kashin yayi yawa. Tunda sukayi maganar Asad d'an sarki zanje wajan mai martabar da kaina na kai masa k'arar abinda ya faru, ai talauci ba hauka bane ba. Meye tsakanin mu dasu in ba silar ciwon nan naki ba? Dan kawai yana sauke nauyin da yake kansu na nema miki lafiya kawai sai azo har gida ayi mana wannan shirmen...? To wallahi bazan amince ba." Kuka take ita dai har lokacin tana kallon saman d'akin Umma da aka kwashe kwanon kai rana tar a cikin sa sai wani b'angaren da aka huda, a hankali bacci ya d'auke ta Allah ya saka akwai inuwar rumfa a wajan.
*☆☆☆*
B'angaren Asad bai san me yake faruwa ba suna tare da Hydar a company dan bai koma aiki ba yana wajan Asad, sai da sukayi azahar suka bar company suka koma gida dan yunwa Asad yake ji. Suna b'angaren su Suhaima tazo ta kawo musu abinci ta ajjiye ta zuba musu kamar ko yaushe, Asad ya d'auki wanda ta zuba masa ya d'auka zai kai bakin sa Suhaima ta kalli Hydar tace, "Yaya Hydar wai me ya faru ne naga ran Mama a b'ace?."
Hydar ya fara cin abinci kana yace, "Ina zan sani Suhaima nida na dawo yanzu?."
"Naji tana waya tana a dake su bata kai matsayin yin soyayya da wanda ta haifa ba, na d'auka ma ko kaine ka fara soyayya da wata poor lady d'in ta saka ayi mata punishment." Gaban Asad ya fad'i ya ajjiye cokalin daman tunda ta fara maganar bai kai abincin bakin sa ya kalle ta yace, "Suhaima me kika ji tace?."
"A yadda take maganar dai an tura gidan su yarinyar ayi mata duka amma ban san wacece ba. Naji tana a dake ta inda dama a sake b'alla k'afar ta babu abinda aka siya ayi." Mik'ewa Asad yayi ya d'auki key na mota da sauri ya fita, ganin hakan Hydar ma ya ture abincin ya mik'e tare da bin bayan sa suka fita Suhaima ta bi su da kallo.
Mota suka shiga suka tafi gidan su Rauda gaban Asad sai fad'uwa yake yi har suka faka a k'ofar gidan, babban burin sa bai wuce Allah yasa basu illatata ko wani nata ba.
Baba suka gani ya fito yana waige-waige ganin hakan ya saka Asad ya fito daga motar Hydar ma ya biyo bayan sa suka k'araso kusa dashi, Baba na ganin su tun kafin su gaisa yace, "Kamar kusan kune a raina, me muka yi muku haka da za'a aiko azo a ci mutunci na dana iyalai na?, me Rauda tayi muku har haka aka yi mata wannan hukunci....? dan Allah ku fad'a na baki hak'uri."
Asad ya kalli Hydar shima ya kalle shi kafin Hydar ya kalli Baba yace, "Baba meye ya faru?." Baba yace, "Kuzo muje ku gani" ya fad'a yana yin gaba suka bi bayan sa gaban Asad sai fad'uwa yake yi sabida fargaba da tashin hankalin abinda zai gani a cikin gidan.
*KWANTAN ƁAUNA*
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*022.*
A hankali suke takawa zuwa cikin gidan suka shiga da sallama idanun sa ya fad'a na Rauda da take zaune cikin ranar da bud'e har taje inda suke fuskar ta duk taji ciwo musamman bakinta da ya fashe. Runtse idanu Asad yayi ya kawar da kansa gefe daga kallon ta kafin Baba yace, "Kunga irin abinda aka yi mana. kalli mahaifiyar Rauda har targad'e aka yi mata, ga ita kanta Rauda da ta kasa tashi tsaye tun da akayi abun bamu sani ba ko an sake karya mata k'afa ne; kalli saman d'akin babar Raudan sun cire kwanon bayan sun dake ta. Me muka yi muku haka?."
Hydar ya gyara tsayuwa yace, "Kuyi hak'uri Baba bamu san abinda ya faru ba kenan sai yanzu muke jin labari shine muka tawo nan d'in kai tsaye dan muyu maganin abun, Mama kiyi hak'uri bamu san abinda ya faru ba kenan" ya fad'a yana kallon Umma. Rauda ta kalle shi ta zaro idanu waje cikin zallar b'acin rai da tashin hankali tace, "Ba tun yau ba daman in aka cuci mutum sai ace yayi hak'uri, in aka zalumci talaka sai ace yayi hak'uri ya yafe sabida bashi da gata da wanda zai shige masa gaba ya karb'i hakkin sa. dan an fimu kud'i da mulki ba hakan yana nufin an mufi daraja a duniya bane, muma mutane ne baza mu lamunci azo har cikin gidan mu a ci mana mutunci sannan a dake mu ba kuma ace muyi hak'uri; bazai yu ba wallahi. Meye ya had'a mu daku da za'a dake mu a kanku? Tsautsayi ne ya ratsa tsakani fa akwai shikenan sai ya zama abin tashin hankali?, naga tun kafin bayyanar ku cikin matsayin wanda suka bige mu ai rayuwar mu muke yi babu abinda muka nema muka rasa, daga shigowar ku rayuwar mu har an fara neman raywuar mu?" Ta fad'a cikin fusata da masifa tana kallon su dukkan ranta a b'ace ba.
Hydar yazo wuya ba'a tab'a yi masa irin wannan fad'an ba a duniya sai yau nan take ransa ya b'aci amma babu yadda ya iya yayi k'okarin b'oye fushin sa kana yace, "Na fad'a miki ko meye ya faru babu sanin deaf babu sani na, inda mun sani hakan ai baza mu bari ta faru ba. Yanzu ake sanar damu muka tawo dan muga su waye amma bamu same su ba, meyasa baza ki fahimta ba?."
"Zuwan ku d'in banza da wofi dashi gwara ku zauna a gida ku sha a.c yafi min wallahi. Sai da aka gama ci maa mutunci sannan zaku d'auko k'afa kuce wai kunzo to kuyi mana me? Ku bamu hak'uri kenan ko?. Ni abinda nake so naji ma akan wanne dalili zasu dake mu har su yiwa Ummana wannan rashin mutuncin?, suna zancen wani Asad ni meye had'ina da wani Asad?, su ya dama bani ba wallahi in ma wani sharrin aka je aka min can ta matse muku amma wallahi sai maganar nan taje gaba in ba haka ba na shiga radio na yayata abinda aka mana ko babu komai k'imar gidan ku zata ragu."