Sashe 15
Kwantan Bauna Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallon sa Umma tayi lokacin da yake juya kud'in tace, "Wanda ya buge Rauda ne yanzu ya fita shine ya ajjiye kud'in."
"Tooo!" Ya fad'a da murmushi a kan fuskar sa yana sake kallon kud'in.
Tab'e baki tayi tana kallon sa ya zuba kud'in a aljihu yace, "To shi wanne irin mai kud'i ne haka?."
"Ban sani ba" ta bashi amsa a tak'aice tana kallon wani wajan daban.
"Allah sarki daman in arzuk'i zai same ka sai Allah ya kawo silar faruwar sa, sai gashi silar arzuk'ina yazo ta hanyar hatsari" ya fad'a yana cigaba da murmushi ya saka hannu ya dafe kud'in.
Shiru tayi kawai bata ce komai ba tayi tagumi tana kallon Rauda da take bacci har lokacin bata farka ba. Fita yayi yana ta dariya ta bishi da kallo kawai tana girgiza kai har ya b'acewa ganin ta.
Fitar sa ba jimawa sosai Rauda ta farka rad'ad'in azaba ya kawo mata ziyara ta runtse idanun ta muryar ta bata fita tace, "Wayyo Allah!" Abinda tace kenan tana hawaye.
Jin hakan ya saka Umma tasowa da sauri tana fad'in, "Rauda sannu kin tashi?." Kai take juyawa tana fad'in, "Umma k'afana!, k'afa Ummana!!, zafi take min zata cire" ta fad'a tana kuka sosai ga kanta na mugun ciwo.
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, sannu Rauda, Allah ya baki lafiya." Kuka take sosai Umman ma sai ta fara hawaye tana rik'e hannun ta tana fad'in, "kiyi hak'uri Rauda, kiyi hak'uri." Bud'e k'ofar akayi aka shigo Umma ta kalli wanda suka shigo taga likita ne da Hydar likitan ya kalli Umma yace, "yaushe ta farka Mama?."
Sai da ta goge idanu tace, "yanzun nan."
"Rauda sannu, me yake miki ciwo yanzu?" Dr ya fad'a yana kallon ta.
"K'afana, k'afa na zai cire, kaina zai fashe ku taimaka min" ta fad'a cikin tsananin azaba tana juya kanta. Gaban Hydar fad'uwa yake jin yadda maganar ta take fita tausayin ta ya sake kama shi jikin sa yayi sanyi matuk'a ganin duk fa da bai buge ta ba da hakan bata faru ba.
Allura likita yayi mata ya d'aura mata ruwa har lokacin juya kanta take yi sabida ciwo. likitan ya kalli Umma yace, "Kiyi hak'uri Mama zata daina jin ciwo in sha Allah, sai a hankali zaki ga kamar batayi ba" Kai ta d'aga kai daga nan suka fita Hydar ya kalli Dr yace, "tana cikin ciwo sosai babu wani taimako da za'a yi mata?."
"Prince daman ai sai a hankali zata samu sauk'i, yanzu farkawar ta kenan dole taji ciwo a jikin ta amma yanzu zai lafa."
Hydar yace, "Dr ayi abinda ya dace please."
"In sha Allah prince zata dawo kamar batayi ba."
"Thanks" yana fad'a ya bar wajan da sauri shi kuma ya koma office.
Haka Hydar ya koma gida gabad'aya jikin sa ya gama mutuwa tausayin Rauda yake ji na shiga jikin sa sosai, da ya kulle ido sai yaga yadda take kuka tana kiran k'afar ta sai hakan ya sake tayar masa da hankali sosai, muryar ta da kukan ta kawai yake ji a kansa da kunnuwan sa hakan ya sake saka jikin sa yin sanyi yana ji kamar yayi mata kuka.
Lokacin da ya shiga b'angaren su Asad baya nan sai Aliyu yana zaune yana tauna chewing gum ganin yadda Hydar ya shigo ya saka yace, "lafiya kai kuma?."
Hydar ya zauna yace, "yarinyar dana kad'e ce tana cikin ciwo abin tausayi."
"Mtswww and so? I think y'ar talakawa ce ko?."
"Ita y'ar talakawar ba mutum bace?."
"Bata da banbanci da matattaciya."
"Ban san me yake damun ku ba, shi d'an talaka ba mutum bane ba ko me?, ko kuma kai ka zab'i taka rayuwar a haka?."
Aliyu ya tab'e baki yayi masa banza bai kuma kula shi da dan a ganin sa bashi da hankali in shine ya buge ta ko k'afar sa zasu gani ne balle ya dinga zarya haka akan kanta. Shima Hydar d'in banza yayi masa dan ya lura Aliyu da Mama halin su guda ne.
A b'angaren waziri da Hajiya suna zaune kamar yadda suka saba a inda suka zaba had'uwa a sirrance waya na hannun waziri an saka speaker muryar mace babba mai cike da kamala tana fita daga cikin ta, Waziri yace, "kamar yadda na fad'a miki anyi komai an gama gashi har mai martaba yana cewa an jinkirta komai." Murmushi tayi mai sauti tace, "na raina wayon ka da kai da ita kanta Sa'adatun, yanzu ku har kun amince da abinda yace?. Wasa yake muku da hankali ya d'auke hankulan ku daga kan sarautar gabad'aya rana tsaka sai dai kuji sanarwa Asad ya zama sarkin ku dole ku duk'a ku gaishe sa. Kun manta tare suka fita ne a jiya?."
Kallon juna sukayi kafin Waziri yace, "Haka ne, amma bakya ganin kamar wannan karon da gaske yake?."
"Ina baka kana mik'o min hannu. Kai kasan babu wanda ya san sirrin mai martaba sama da Asad sai kuma Mubarak k'anin ka, ko lokacin da suka je Kano da shi Mubarak d'in suka tafi tare aka tattauna aka cimma matsaya ku baku san komai ba. Ku a ganin ku mai martaba zai bada dama kayi sarauta ne? Kuyi tunani dakyau zaku gano kwantan b'auna ne."
Hajiya tace, "duk abinda kika ce haka ne tabbas tunani na bai kawo haka ba sai yanzu, tabbas kwantan b'auna mai martaba yayi mana yana so hankalin mu ya d'auke daga kan Asad ne shiyasa yace haka. Ya fahimci akwai masu nufi irin namu shiyasa yayi saurin dakatar damu." Murmushi tayi mai kyau tace, "Dad'ina dake kina da saurin fahimta. Ku nutsu ku kuma dawo hankalin ku in ba haka ba kuna ji kuna gani komai zai lalace muku. Suhail kuma tabbas ya sakawa Asad layar nan dana baka kuma ta fara shiga jikin sa zancen da nake muku yanzu ma zaman gidan ya fara neman gagarar sa, ciwon Hydar zai tashi a cikin kwanakin nan, ga Aliyu kuma daman ba zaman gidan yake ba. Matuk'ar bamu d'auke hankalin Rabi'atu ba to tabbas shirin mu bazai tab'a tafiya yadda muke so ba, rashin lafiyar Hydar da barin Asad gida ya isa ta fasa tafiyar da tace zatayi, dan matuk'ar taje Kano sai komai ya lalace."
Waziri ya girgiza kai yace, "Wannan shine shirin mu na gaba kenan?."
"Shiri na gaba a kan Asad ne ya zama dole ya bar gidan nan kota halin k'ak'a, ko kuma ya bar duniyar gabad'aya barin sa da numfashi barazana ne ga namu numfashin."
Hajiya tace, "Abinda nake nuna masa kenan tun farko amma ya kasa ganewa, a kawar da Asad shine abu mafi mahimmaci a wajan mu."
Tace, "kwantar da hankalin ki Hajiya baza mu gaggawa ba, a hankali zamu tafi da lamarin in muka ba bar Asad da Aliyu ma komai zai tafi yadda muke so, zakuyi mamaki idan nace Aliyu yana neman hanyar da zai bi wajan ganin ya zama sarki a garin nan, tabbas Ali zai iya kashe Asad abu ne mai sauk'i a wajan sa indai burin sa zai cika wannan ba komai bane ba. mu jira muga yadda wasan zai kaya."
"Abinda nake so dake Sa'adatu ki cigaba da nuna k'aunar Asad a gaban mahaifin sa, ki jawo sa jikin ki yadda baya sakewa da uwar sa ke ya sake dake, kiyi duk abinda zakiyi ya fara cin abin hannun ki ana zuwa wannan gab'ar mun kamo wuyan sa, na bar ku lafiya" tana fad'a ta datse kiran wayar. Hajiya tace, "kirata naji ta yaya zan jawo shi jiki na, dan Allah ka kira ta."
Waziri yace, "Bana tab'a samun ta a waya sai dai in ina taso zata kira ni sai ta bani lokacin da zamuyi magana."
"Gaskiya ta cika babbar master planer, amma wacece ita? Naso na gane maganar ta amma na kasa ganewa, na santa kuwa?."
"Ba lallai kin santa kedai kiyi abinda tace ta kai k'arshe wajan iya tsara plan. Ta wacce hanya zaki bi Asad ya zo hannun ki?."
Numfashi ta sauke tana girgiza kai kafin tace, "Salad, zogale, lansir, wad'annan shine abinda Asad yafi so yaci tun mai babban d'aki tana raye, duk juma'a sai ta aiko masa da d'aya daga cikin su an masa lafiyayyen had'i zai ci kuma hankali a kwance. Bayan shi sai kunun tsamiya mai lemon tsami, sai kuma shayi ko coffee ko kuma chips Asad yana son wannan abubuwan dasu zanyi amfani na meye gurbin mai babban d'aki wajan aika masa dashi duk juma'a, babbar matsalar ita Rabi'atu kana ganin zata bada damar da zan jawo Asad jikina?."
"Tabbas kinyi tunani mai kyau Asad yana matuk'ar son abubuwan da kika lissafa kuma shi halinsa daban ne dan kin bashi karb'a zaiyi yaci bazai kawo komai ba, yadda zuciyar sa take fara gani yake ta kowa fara ce, yarda baya nufin kowa da sharri gani yake kowa ma haka ne. Matsalar dai ita uwar sa kamar yadda kika ce."
Ta daki kujerar da take kai tace, "Amma bar ni da ita nasan abinda zanyi zan biyo mata ta k'ark'ashin k'asa sai burin mu ya cika."
"Ki dai yi a sannu kin san tana da wayo kuma ta dafu da magani ne tun tana yarinya ta kuma dafa y'ay'an ta, ki duba wahalar da muke ta sha tun suna k'ananu har yanzu akan abu guda muke, amma zamu kamo bakin zaren in Allah ya yarda."
Hajiya ta mik'e tsaye tace, "ni na koma zaka ji bayani daga baya" tana fad'a ta fita shima bai jima sosai ba ya tashi ya tafi.......
*ni kaina na shiga confuse fa, wacece Master planer kuma?.*🏃🏼♀️🏃🏼♀️🏃🏼♀️🤣🤣
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*008.*
Washe gari ta kama ranar Asabar kamar jiya da wuri Hydar ya d'auki mota ya tafi asibitin da Rauda take duk da ciwon kan da yake fama dashi haka ya jure dan da ita ya kwana a ransa. Dak'yar ya iya k'arasawa yayi parking motar ya shiga cikin asibitin kansa na sara masa sosai. D'akin da take ya fara shiga da sallama a bakin sa cikin takun nutsuwa da izzar sarauta da k'asaita da take yawo a cikin jijiyoyin jikin sa.
"Tooo!" Ya fad'a da murmushi a kan fuskar sa yana sake kallon kud'in.
Tab'e baki tayi tana kallon sa ya zuba kud'in a aljihu yace, "To shi wanne irin mai kud'i ne haka?."
"Ban sani ba" ta bashi amsa a tak'aice tana kallon wani wajan daban.
"Allah sarki daman in arzuk'i zai same ka sai Allah ya kawo silar faruwar sa, sai gashi silar arzuk'ina yazo ta hanyar hatsari" ya fad'a yana cigaba da murmushi ya saka hannu ya dafe kud'in.
Shiru tayi kawai bata ce komai ba tayi tagumi tana kallon Rauda da take bacci har lokacin bata farka ba. Fita yayi yana ta dariya ta bishi da kallo kawai tana girgiza kai har ya b'acewa ganin ta.
Fitar sa ba jimawa sosai Rauda ta farka rad'ad'in azaba ya kawo mata ziyara ta runtse idanun ta muryar ta bata fita tace, "Wayyo Allah!" Abinda tace kenan tana hawaye.
Jin hakan ya saka Umma tasowa da sauri tana fad'in, "Rauda sannu kin tashi?." Kai take juyawa tana fad'in, "Umma k'afana!, k'afa Ummana!!, zafi take min zata cire" ta fad'a tana kuka sosai ga kanta na mugun ciwo.
"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un, sannu Rauda, Allah ya baki lafiya." Kuka take sosai Umman ma sai ta fara hawaye tana rik'e hannun ta tana fad'in, "kiyi hak'uri Rauda, kiyi hak'uri." Bud'e k'ofar akayi aka shigo Umma ta kalli wanda suka shigo taga likita ne da Hydar likitan ya kalli Umma yace, "yaushe ta farka Mama?."
Sai da ta goge idanu tace, "yanzun nan."
"Rauda sannu, me yake miki ciwo yanzu?" Dr ya fad'a yana kallon ta.
"K'afana, k'afa na zai cire, kaina zai fashe ku taimaka min" ta fad'a cikin tsananin azaba tana juya kanta. Gaban Hydar fad'uwa yake jin yadda maganar ta take fita tausayin ta ya sake kama shi jikin sa yayi sanyi matuk'a ganin duk fa da bai buge ta ba da hakan bata faru ba.
Allura likita yayi mata ya d'aura mata ruwa har lokacin juya kanta take yi sabida ciwo. likitan ya kalli Umma yace, "Kiyi hak'uri Mama zata daina jin ciwo in sha Allah, sai a hankali zaki ga kamar batayi ba" Kai ta d'aga kai daga nan suka fita Hydar ya kalli Dr yace, "tana cikin ciwo sosai babu wani taimako da za'a yi mata?."
"Prince daman ai sai a hankali zata samu sauk'i, yanzu farkawar ta kenan dole taji ciwo a jikin ta amma yanzu zai lafa."
Hydar yace, "Dr ayi abinda ya dace please."
"In sha Allah prince zata dawo kamar batayi ba."
"Thanks" yana fad'a ya bar wajan da sauri shi kuma ya koma office.
Haka Hydar ya koma gida gabad'aya jikin sa ya gama mutuwa tausayin Rauda yake ji na shiga jikin sa sosai, da ya kulle ido sai yaga yadda take kuka tana kiran k'afar ta sai hakan ya sake tayar masa da hankali sosai, muryar ta da kukan ta kawai yake ji a kansa da kunnuwan sa hakan ya sake saka jikin sa yin sanyi yana ji kamar yayi mata kuka.
Lokacin da ya shiga b'angaren su Asad baya nan sai Aliyu yana zaune yana tauna chewing gum ganin yadda Hydar ya shigo ya saka yace, "lafiya kai kuma?."
Hydar ya zauna yace, "yarinyar dana kad'e ce tana cikin ciwo abin tausayi."
"Mtswww and so? I think y'ar talakawa ce ko?."
"Ita y'ar talakawar ba mutum bace?."
"Bata da banbanci da matattaciya."
"Ban san me yake damun ku ba, shi d'an talaka ba mutum bane ba ko me?, ko kuma kai ka zab'i taka rayuwar a haka?."
Aliyu ya tab'e baki yayi masa banza bai kuma kula shi da dan a ganin sa bashi da hankali in shine ya buge ta ko k'afar sa zasu gani ne balle ya dinga zarya haka akan kanta. Shima Hydar d'in banza yayi masa dan ya lura Aliyu da Mama halin su guda ne.
A b'angaren waziri da Hajiya suna zaune kamar yadda suka saba a inda suka zaba had'uwa a sirrance waya na hannun waziri an saka speaker muryar mace babba mai cike da kamala tana fita daga cikin ta, Waziri yace, "kamar yadda na fad'a miki anyi komai an gama gashi har mai martaba yana cewa an jinkirta komai." Murmushi tayi mai sauti tace, "na raina wayon ka da kai da ita kanta Sa'adatun, yanzu ku har kun amince da abinda yace?. Wasa yake muku da hankali ya d'auke hankulan ku daga kan sarautar gabad'aya rana tsaka sai dai kuji sanarwa Asad ya zama sarkin ku dole ku duk'a ku gaishe sa. Kun manta tare suka fita ne a jiya?."
Kallon juna sukayi kafin Waziri yace, "Haka ne, amma bakya ganin kamar wannan karon da gaske yake?."
"Ina baka kana mik'o min hannu. Kai kasan babu wanda ya san sirrin mai martaba sama da Asad sai kuma Mubarak k'anin ka, ko lokacin da suka je Kano da shi Mubarak d'in suka tafi tare aka tattauna aka cimma matsaya ku baku san komai ba. Ku a ganin ku mai martaba zai bada dama kayi sarauta ne? Kuyi tunani dakyau zaku gano kwantan b'auna ne."
Hajiya tace, "duk abinda kika ce haka ne tabbas tunani na bai kawo haka ba sai yanzu, tabbas kwantan b'auna mai martaba yayi mana yana so hankalin mu ya d'auke daga kan Asad ne shiyasa yace haka. Ya fahimci akwai masu nufi irin namu shiyasa yayi saurin dakatar damu." Murmushi tayi mai kyau tace, "Dad'ina dake kina da saurin fahimta. Ku nutsu ku kuma dawo hankalin ku in ba haka ba kuna ji kuna gani komai zai lalace muku. Suhail kuma tabbas ya sakawa Asad layar nan dana baka kuma ta fara shiga jikin sa zancen da nake muku yanzu ma zaman gidan ya fara neman gagarar sa, ciwon Hydar zai tashi a cikin kwanakin nan, ga Aliyu kuma daman ba zaman gidan yake ba. Matuk'ar bamu d'auke hankalin Rabi'atu ba to tabbas shirin mu bazai tab'a tafiya yadda muke so ba, rashin lafiyar Hydar da barin Asad gida ya isa ta fasa tafiyar da tace zatayi, dan matuk'ar taje Kano sai komai ya lalace."
Waziri ya girgiza kai yace, "Wannan shine shirin mu na gaba kenan?."
"Shiri na gaba a kan Asad ne ya zama dole ya bar gidan nan kota halin k'ak'a, ko kuma ya bar duniyar gabad'aya barin sa da numfashi barazana ne ga namu numfashin."
Hajiya tace, "Abinda nake nuna masa kenan tun farko amma ya kasa ganewa, a kawar da Asad shine abu mafi mahimmaci a wajan mu."
Tace, "kwantar da hankalin ki Hajiya baza mu gaggawa ba, a hankali zamu tafi da lamarin in muka ba bar Asad da Aliyu ma komai zai tafi yadda muke so, zakuyi mamaki idan nace Aliyu yana neman hanyar da zai bi wajan ganin ya zama sarki a garin nan, tabbas Ali zai iya kashe Asad abu ne mai sauk'i a wajan sa indai burin sa zai cika wannan ba komai bane ba. mu jira muga yadda wasan zai kaya."
"Abinda nake so dake Sa'adatu ki cigaba da nuna k'aunar Asad a gaban mahaifin sa, ki jawo sa jikin ki yadda baya sakewa da uwar sa ke ya sake dake, kiyi duk abinda zakiyi ya fara cin abin hannun ki ana zuwa wannan gab'ar mun kamo wuyan sa, na bar ku lafiya" tana fad'a ta datse kiran wayar. Hajiya tace, "kirata naji ta yaya zan jawo shi jiki na, dan Allah ka kira ta."
Waziri yace, "Bana tab'a samun ta a waya sai dai in ina taso zata kira ni sai ta bani lokacin da zamuyi magana."
"Gaskiya ta cika babbar master planer, amma wacece ita? Naso na gane maganar ta amma na kasa ganewa, na santa kuwa?."
"Ba lallai kin santa kedai kiyi abinda tace ta kai k'arshe wajan iya tsara plan. Ta wacce hanya zaki bi Asad ya zo hannun ki?."
Numfashi ta sauke tana girgiza kai kafin tace, "Salad, zogale, lansir, wad'annan shine abinda Asad yafi so yaci tun mai babban d'aki tana raye, duk juma'a sai ta aiko masa da d'aya daga cikin su an masa lafiyayyen had'i zai ci kuma hankali a kwance. Bayan shi sai kunun tsamiya mai lemon tsami, sai kuma shayi ko coffee ko kuma chips Asad yana son wannan abubuwan dasu zanyi amfani na meye gurbin mai babban d'aki wajan aika masa dashi duk juma'a, babbar matsalar ita Rabi'atu kana ganin zata bada damar da zan jawo Asad jikina?."
"Tabbas kinyi tunani mai kyau Asad yana matuk'ar son abubuwan da kika lissafa kuma shi halinsa daban ne dan kin bashi karb'a zaiyi yaci bazai kawo komai ba, yadda zuciyar sa take fara gani yake ta kowa fara ce, yarda baya nufin kowa da sharri gani yake kowa ma haka ne. Matsalar dai ita uwar sa kamar yadda kika ce."
Ta daki kujerar da take kai tace, "Amma bar ni da ita nasan abinda zanyi zan biyo mata ta k'ark'ashin k'asa sai burin mu ya cika."
"Ki dai yi a sannu kin san tana da wayo kuma ta dafu da magani ne tun tana yarinya ta kuma dafa y'ay'an ta, ki duba wahalar da muke ta sha tun suna k'ananu har yanzu akan abu guda muke, amma zamu kamo bakin zaren in Allah ya yarda."
Hajiya ta mik'e tsaye tace, "ni na koma zaka ji bayani daga baya" tana fad'a ta fita shima bai jima sosai ba ya tashi ya tafi.......
*ni kaina na shiga confuse fa, wacece Master planer kuma?.*🏃🏼♀️🏃🏼♀️🏃🏼♀️🤣🤣
*KWANTAN ƁAUNA*
FitattuBiyar 2023
©️ *Nana Haleema.*
*Book 1*
*008.*
Washe gari ta kama ranar Asabar kamar jiya da wuri Hydar ya d'auki mota ya tafi asibitin da Rauda take duk da ciwon kan da yake fama dashi haka ya jure dan da ita ya kwana a ransa. Dak'yar ya iya k'arasawa yayi parking motar ya shiga cikin asibitin kansa na sara masa sosai. D'akin da take ya fara shiga da sallama a bakin sa cikin takun nutsuwa da izzar sarauta da k'asaita da take yawo a cikin jijiyoyin jikin sa.